BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/14/20, 7:12 PM – Ummi Tandama: BAHAGGN , , , , , , , , , ,

????????5️⃣1️⃣????????

NOVEL DI NA NA KUDI NE NA FADA TUN FARKO KARKI FITAR KARKI KADA KUMA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA, CIN AMANA BIBIYA TAKAI TA INDA BAKIYI TSAMANI BA, , ,

Tun farko na fada maki karki fitar min da novel don karatun ba dole bane ba kowa nake ba amma nasan Allah ya isana dama bai tafiya ga banza.
Bakiji bake kaida bane don akwai wata mai fitar wa bayan ke ke ce kika fara gani saura dayan nata sai yafi naki don ko abin ba zai zo mata da dadi ba ita.
Akan novel akan son kai tajawa kanta masifun duniya sai da na fada maku dan Allah kada ku fitar min don kada in dauki alhakin ku a kaina.
Kullun ina nanata maku kin dauka wasa ne ba abinda zai faru dake har yau kaf makaranta novel dina ba wanda zaice maki yasan makawa ko ya san ida take da idon shi hmmm muje zuwa yanzu aka fara ai ya kama binki ke nan ta hanyar dabaki zata ba yar uwa.
Ganin gidan namu nakeyi kamar bakon wuri a idona don komai ya canza min a idona sai nake jin wani irin dadi a zuciya ta.
Ranan barci dai ne barawo da ya iya dauka na safiyan fari kiran sallah masalacin da Sulaiman ya gina wa mutanen unguwar mu ya karade min kunni na dole mutun ya tashi saboda karan lasifikan da yai yawa.
Duk da bani sallah amma na tashi a lokacin na kewaya na dawo na kwanta ban iya kwaciya ba na mike zan fita don shara ummi na dake falo kwance ta dakatar dani da fadin.
Dama kin koma kin kwanta don ko dan Albarkan nan ya rabawa kowa wurin ta don haka yanzu ma ba komai akeyi a gidan gaba daya ba.
Na koma na kwanta kamar yadda ummi ta umurce sai dai ba barci nayi ba kwantawa kawai nayi zuciya ta fam da tunane.
Misalin sha daya saura na safe na fito saye cikin kayan barci na da ban cire ba a falo na samu ummi da kanne na suna karyawan safe tayi masu faten doyan da nazo masu dashi jiya.
Na fada saman kujeran da babu kowa saman shi don kasa suke zaune dukkan su tare da yin mika nace duk na gaji kamar nayi wani aiki mai yawa.
Ummi ne tace min ai tafiyan mota mai nisa gajiya yake sawa mutum ajiki na gyara kwanciya ina fuskantar su dakya nace ai rabin tafiyan a jirgi nayi ummi daga nan dai zuwa abuja ne ya saukar min da gajiyan.
Tace masu gari yau kece mai tafiya a jirgi yar nan lalai duniya abin da ya baka tausayi wata rana shi zai baka mamaki.
Kwarai da gaske ummi wallahi ni kaina ganin abin nake kamar a mafalki don nakan yi tunanen hakan a raina.
A jiuan zuciya naji ummi tayi tace mhmm ai tun dawowan mu gidan nan yau sati uku ke nan inna ku sai ta baka tausayi don zaman ta a babban gida ta raina kanta sosai a can don basu raga mata ba ko kadan.
Tace yaya wajan anty naki suna dai lafiya ko bansan adduan da zawa wanan matar ba a rayuwana sai dai fatan gamawa da duniya lafiya.
Shiru nayi ina mai ci gaba da tunane sai da naji ummi tace yanzu yaushe zaki koma naga kin kwaso uban kaya kamar baki da niyan komawa can.
Nisawa nayi na dawo daga tunanen da nakeyi nace ummi ba zan koma gidan anty ba indan ba aure nayi ba in je in gaida ita.
Da sauri ummi tace akwai matsala ke nan a tsakanin ku ganin kanne na dake zaune sun kallo ni lokaci guda yasa ni cewa babu komai haka dai na yanke a raina.
Shiru naga ummi tayi sai can tace a zubo maki faten ne kishashi da zafin sa tun baiyi sanyi ba ki kasa sha barshi ummi ban iya cin abu mai nauyi da safen nan.
Sai kaunana tace ai kin san anty Safiya bata son cin abinci ummi kina dai wahal da kankine sai zuwa rana zakiga tana neman abu mai ruwa ta sha shi ne karin kumallonta ita.
Ummi na mikewa take fadin mukan na kauye ne sai da abu mai dan nauyi muke jin dadin karin Safe don badon doyan nan da kika zo muna dashi ba da shin kafa da wake zan masu da safen nan su karya ko wanan wanan yar sa idon ne nayi aune da ita tana ferewa wai fate zasu sha da safen nan.
Muryan baba danaji ya nufo kofan mu yasani mikewa na isa kofa ina fadin baba har ka fito banje mun gaisa ba.
Yace zan fita Safiya jinki shiru yasa na dauka ko barci kikeyi yaya hanya yaya wajen su hajiyar taki nace suna lafiya sun mace agaida kai.
Yace ina karbawa yaya wajen gwagon naki kina lekasu kuwa na dukar da kai sai yace aiko baki kyauta ba Safiya ai ba a yanke zumunci tunda ita ta yanke da sai ke ki raya shi lada zaki samu a wurin Allah.
Nace baba ai zan tafi amma gaskiya ba yanzu ba yanzu ba nafi son sai ina da aure inje da mijina yafi sauki.
Yace kuma fa kinyi tunane maikyau kuma Allah yasa mu dace yaya shi Alhaji sulaiman din suna dai lafiya ko na amsa kasa kasa da lafiya yake shima yana gaida kai baba.
Ya juya yana magana da ummi da take kofan daki hakan yasani mikewa na shige uwar dakin namu ban zauna ba wanka na shiga don makewayin da ke akwai a dakin kuma da ruwa a ciki.
Na fito ina shafa mai ummi ta shigo kuryan dakin tana ce min may ke faruwa tsakanin ki da uwar dakin naki naga ganin kannen ki yasa baki fada min ba.
Nace ummi ba wani matsala sai dai akwai matsala kadan nan dai na fara bata labarin abinda naji da kunne na anty din tana fadi.
Ta nisa tare da fadin ikon Allah ai tayi kokari ko wanan da datayi Allah ya saka mata da Alheri ai an gode.
Shi son kai sone ba wanda yaki nasa ya samu bata so ki ba taki dangin mijin ta don ko sune nata don da su take zama.
Nace aini ummi banga laifin anty ba don sanin ko waye anty uwa danayi don ba karamar macen duniya bane sosai anty uwa.
Tace Allah yai muna mafi alherin sa nace amin tace yanzu shi may yace a nasa bangaren nace yace wani sati magabatan shi zasu zo sai a saka ranan aure dayani.
Tace to Allah ya kyauta muna magana kiran wayan shi ya shigo nan ta fice dakin ta barni ina karba wayan nayi sallama ya karba yace.
Watau kin ga ummi kin manta da kowa ko nace ba hakana bane yanzu na tashi ina batun kiran ka sai gashi ka kirani yanzu.
Yace yaya gajin hanya don nasan akwai gajiya nace Alhamdullahi yaya na barku can?
Ya amsa da kalau sai nace yallabai naga ka mayar muna da gida kamar bila ubangiji Allah ya saka da alheri ya dada daukaka da yalwatan arziki murmushi naji yayi yace anty ki ta kiraki kuwa ?
Ya kawar da maganan nan take nima murmushin nayi mashi nace baka son godiyan nawa ke na ko ?
Yace tambayan ki nake yi antyn ki ta kiraki da kika zo arewa?
Nace har yanzu bata kirani ba yace na san za a rina ai, kyale ta, jiya ta kirani yau ma da safen nan munyi magana da ita.
Sai naji bakina yana tambayan shi may tace ma ?
Sai yace min ina ruwan ki da maganar mu da ita.
Haba uncle dina don Allah yaya kukayi da ita yace maganan dai ne na in rabu dake in auri diyar hajiya uwa don tafi asali.
To kai may kace mata yace cewa nayi haka shine daidai don dama ke baki waye ba.
Nace to Allah ya hada kowa da rabon sa yace amin ai ya hada tunda ya hadani dake kin sace min zuciya yanzu bani jin maganan madam dina kuma.
Murmushi nayi wanda ya baiyanar mashi da jin dadi na a fili tare da sauke ajiyan zuciya tare dacewa nagode uncle dariya yayi yace aini zan gode maki da baki yarda sun hadani da ke ba.
Murmushi nayi nace ai ba zasu iya ba don hadin Allah ne bana mutum ba da zasu iya da sun raba ko tunda duk wanda aka fadawa irin kazafin da sukai min dole ya dauka gaskiya ne.
Ya katse ni da cewa ai baki san wani abu ba nace ina jinka.
Yace ai tunda ta gabatar min dake da farko hankali na ya kwanta da zancen ki don haka ma daddy su twins shima ya yaba da hankalin ki.
Banga abinda zaisa yanzu daga baya ba kuma ta kawo min zancen wata na dai ce da ita haka ne daidai sai idan lokaci yayi zata sani.
Mun dauki lokaci muna waya dashi kamar ba kudi yake kashewa ba sai da ya gaji don kanshi yai min sallama na tashi na karasa shiri na dakin mama na fara shiga muka gaisa muka dan taba hira sai na wuce dakin inna inda na samu saadatu ita kadai a dakin wai inna tafita unguwa.
Nan na sake jikina muka dauki lokaci muna hira da ita nake tabayan ta fanin Isah dayai mata ciki take fada min bata da labarin shi.
Nace baya kawo maki komai ne tace tun wanan lokacin bai kara kulata ba kuma ba wanda yai masa magana akai ana batun ginan gidan mu.
Da yaya sani ya shigo na tuntube shi da zancen sai cewa yayi min ai shi ba abinda ke gaban shi ke nan ba nace haba yaya sani idan baku tsaya muna tsaye ga alamarin mu ba wa zai tsaya muna akai yace zai duba yagani yadda za a yi.
Anan muka bar zancen ban jima da fita dakin nasu ba inna ta dawo gidan tana shigowa sai ta fara budan hancin ta tana shakan kamshina dana bari dakin tace.
Safiya ta shigo dakin nan halan sai Saade tace eh tace karuwan banza ina shigowa naji kamshin turaren ta.
Haba inna Safiyar ce kuma karuwa Saa ta fada mata haka na tace idan ba karuwa bane may nena ita uban wa take nema a birni.
Abinda kikeyi gaskiya inna baida kyau shiyasa kullun bamu ganin karuwa ga alamarin mu don bakin hassada irin naki.
Aiko tayi cikin Saade din da fitina ita kuma kamar mai jiran uwa nan suka shiga yaba ma juna bakar magana har ya jawo hankalin mutanen gida aka tsaya sauraren ta yaya Nura da yaya Sani ne suka shigo gida suke tambayan ba asin maganan.
Inna ta kama inda inda sai Saaden ne ta fada masu abinda ya hada fadan da sukeyi daidai ina fitowa daga daki kenan maganan ya daki kunne na.
Cak na tsaya raina ya baci sai yaya nura ne yace in ma karuwanci Safiya ke yi a birni ai anci albarkacin karuwancin ta a gidan nan.
Yaya Sani ya karbe da fadin wallahi fa ke yar taki mai take zaman suna takeyi maki a daki da tsohon ciki komay ba gara safiya ba kowa ya san alherin ta ne ya kaita ga haka.
Wallahi inna idan kice bazaki bar halin nan ba watarana sai kinji kunya ba kadan ba zuwan Safiya dakin ki alheri ya kawo ta ba tsiya ba.
Don zuwa tayi ai magana da Isah asan halin da Saadatu ke ciki don bai waiwaye ta ba har yau mama tace kai kedai Rakiya halin ki baiyi ba wallahi.
Safiya tayi maki kama da wacce take karuwan ci koda ba a ganin zuciyar mutum ai abin duniya baya boyuwa da muji tun tuni.
Daki na koma van iya tsayawa na saurari sauran maganan ba sai dai na sa a raina cewa ba zan sake shiga dakin inna ba komai ya faru kuwa.
Har yamma naji anty bata kirani ba don haka na dauki waya na kirata amma har wayan ya katse bata dauka ba.
Ban kara kiranta ba da dare muna zaune a dakin mu sai ga baba ya aiko a kira masa ummi ta dan dade wurin sa ta dawo muna hira da kanne na sai tambayan ta kauna tayi tace halan baba yaji zancen maganan dazu ne ummi ?
Tace ina ruwan ki sai kin san abinda naje yi gunsa nace kai kedai baki da kunya Aisha may zai kara ki idan kin ji ni ban ma son baba yaji zancen tace sai dai kada a kara don Nura ya tare shi da zancen a waje.
Ina ga ki je gun su kawun ki kafin bakin ki su iso kin dawo zaifi nace to ummi zan tafi amma ba don naso a raina ba don dai ta ce in je ne kawai ba yarda zanyi.
Kwana biyu da zuwa na na shirya dani da kani na sai kyauyen su ummi na ida mahaifanta suke da zama.
Tafiyan safe mukayi don haka muka isa da wuri mun samu karbuwa na mutunci a wurin su aka kai muna kayan mu dakin kakan mu mace .
Bayan muci mun sha daga abincin su da suka fi karfi suka gabatar muna dashi muka zauna a na gaigaisawa da yan uwa.
Sai yamma mazajen suka dawo daga gonakin su wanda dashi suka dogora suna ci suna sha daga gare shi sai kiwo da suke hadawa dashi.
Kakan mu ne na karshen shigowa gida sai da ya huta mukaje gaida shi bayan mun gaisa ya tambaye mu mutanen gida.
Yake tambayana zancen aure nace insha Allahu malam ba za a dauki lokaci ba zanyi yace ko dai anzo sallaman mu ne gaba daya nayi dariya ina ce mai a a na dai zone in duba ku.
Shekaran jiya na zo shine ummi tace in iso nan in gaida ku yace ai ta kyauta tun bayan abinda ya faru dake bamu sake ganin ki ba sai nake ji wai kin samu mane mi a can birni har yai masu abin arziki a gida.
Na soke kaina kasa din kuya yace yanzu dai ciwo ya wuce ko nace malam yadai lafa dai amma ai ciwon ba mai barin jiki bane kwata kwata.
Yace ummh ummh kar ki yarda da wanan ki sa a ranki Allah zai baki lafiya ko yana nan baya tashi har a manta cewa kina dashi a jikin ki nace Allah yasa malam.
Yace ai kin ga rakumi nace eh malam yace to komai na jikin shi magani ne bani na fada ba in ji fiyayyen halita SAW ya fadi.
Yace da zaki samo fitsarin nan nasa koyaushe ya zama maki kamar ruwan shan ki to da kan ki zaki dawo nan ki bani labari bance zaki warke ba atake amma akwai faida a gare shi.
Nace shi fitsarin rakumin yace kwarai kuwa sannan namar shi ya zama maki abin ci ko yaushe akalla a sati ki kici shi ko sau biyu.
Sai kuma nonon shi ki dinga sha akai akai shima yana da faida sosai a jikin bawa ya dan kurkure baki da ruwan butan dake gefen shi yace sannab kin ga kashin rakumi nace eh malam yace ki samu kashin ki gone shi zai ya kono sosai sai ki daka ki dinga sha da albarkan annabi zaki neme ni indan muna raye.
Ba fa wai matsalan ciwon da ke damun ki ba kawai a a koda jikin ka ne baka gane kansa ba ne mi daya daga cikin sassan jikin rakumi ka riki sahihi da yardan ubangiji zaka ga faidan shi.
Nace ikin Allah yace shiko kashin nan nasa da kika gani nace eh malam mutane ne basu gane mai ba ai da zaki samay shi.
Ki busar dashi ki samu kanufari ki hada dashi kina yin hayakin shi a jikin kin ki sai yayi murmushi yace aiko maza dake samun matsalar rashin karfin gaba gane wa ne ba sayi amma da mutum zai samay shi yayi yadda nace maki sai ya dinga hayaki a gaban shi dashi ai ba katamin taimako yake yi ba za ka iya kuma dafa gaban shi sai dai ba a faye samun shi ba don tun wurin soke shi ake sayewa.
Namiji in dai yana amfani dashi ai masa romon shi da bakin iri ban san yaya kuke kiran bakin iri ba ku.
Nace ko habbatussaudat yace sunan sa ke nan ko nace eh yace sai a hada da kanumfari da citta da masoro da tafarnuwa yace ai bashi ba gazawa ga iyalin shi don karfi ne zai taso mashi sosai yaji shi gyagyan kamar dan shekara a shirin a duniya.
Yace kaiyya ai abar gado tun baya an dauki aladun wasu mun dora wa kan mu amma kin ga mu na kauye ai bamu bar gado ba, kin ga ko mun fiku karfi da lafiya don mu ciwon nan da ake fadi duk bamu sanshi ba.
Nace hakane malam amma ai inda mutum zai samu rakumi ne aiki malam har ya tara fitsarin shi da yawa haka.
Yace kuke nan dake birni amma munan ai shi yafi komai sauki ko yanzu kafin ki tashi zan iya sa a tara maki jarka kuma samo maki sauran sassan jikin ki jeraba ki gani.
Godiya na fara yi masa yace may ye abin godiya a ciki lafiyar ki ai namu ne duka yanzu barin fita idan na dawo maci gaba don lokacin sallah yayi yanzu.
A Zuciya na fara tunabe nayi yadda mutum zai sha waban abin da ya fada min amma dai ko yaya ne zan nema un jeraba in gani nma mikewa na yi zuwa rumfar kakata inda dakin ta yake na zauna rubuta duk abinda yace min nayi a wayana.
Bayan munyi sallah aka gabatar muna da tuwon surfafen dawa da miyar danyen kuka an lema man shanu a saman shi.
Kanina yace bazai ci ba shi zai fita yasamu bread da shayi ya sha azuciya ta nace ikon Allah ashe akwai abincin da dan gidan mu zai kyamaci ci a yanzu.
Nikan naci shi sosai nayi kat tare da hamdala na wanke hannu na sai naji kawo habu ya shigo yana cewa ina bakuwar tamu ga dan tsaraban kauye nasan ba iya cin abincin namu zakiyi ba ya miko min leda na karba hannu bubiyu ina cewa ai ko naci kawu sai da na koshi.
Ledan na aje a gefe na shima ya samu wuri ya zauna muna hira kakan mu tana sa muna baki jefi jefi.
Nan dai har ya gan garo kan zancen aure na nake fada mai halinda ake ciki yanzu ga zancen nawa ban boye mai komai ba ya murmusa yace abinku ne na yan birni.
Baku neman gida sai abu ya kure maku gani kuke yi kamar mu kauyawa ne komai bamu sani ba banda noma da kiwo amma ai aiki sai kauye.
Nace kawu ba hakana bane nayi nisa ne daku ko gida sau biyu ke nan nazo tun tafiya na yace to kin ga tunda kinzo yanzu ai ba a barki haka ki koma ba ai wani dan abu ba.
Kin ga ki samu kaucin gwandan daji da kan tunkiya ki daka ai maki miya dashi kaucin zaki iya dafawa kuci har da yara in Allah ya kawo su amma fa banda mai gida wanan mallakane sahihi.
Sai na neman farin jini ga dukkan dangin miji da ma mijin kan shi zaki samu farar dawa da farin goro farin kudi kurma farar kaza sayen tunfafiya na gabas din shi ki hade ya bushe kiyi wanka dashi da hayaki bayan kin dake su wuri daya, sai naga yayi murmushi.
Don watse makircin makiya kuma zaki karanta Lah illah hailala muhammadun rasulallah, hasbunal lahu wani imal wakil kafa dari duk safe zaki ga yadda zasu kwashe da yardan Allah.
Domin tsarin jikin ki kuma zaki samu ganyen hankuwa da ganyen sabulun dawaki da ganyen geza wanda suka fadi kasa da kansu a dake ki sha.
Wanan ma na tsari ne zaki samu gero wanda ya fidda kai ya baci yayi geza da suren fatake a dake asha da kunu .
Kiran da matar shi ta aiko tana mashi ne yasa ya tashi badon ya gama bani ba sai da ya fita nace ma kakana ni ina zan samu wanan abin daya fada min tace Allah ya kaimu gobe sai in zagaya nan bayan gari in harhado maki su wanda babu in kin koma can gwagon ummin ki sai ta samo maki ban samu ganin kakana ba don ance yana waje da bamin fulani da suka zo wurin shi.
Don haka nayi shirin barci na kwanta da wuri sai barci can cikin barci na naji Shafiu ya dawo kakan mu nace mashi ya dauki ga leda nan da kawun mu ya sayo muna nama ciki.
Ban iya bude idona ba don barcin da yaci karfina a lokacin har ya gama ya fita ban tashi ba tagama abinda take yi ta rufe kofan daki ta sauke min gidan sauron da ta kafa min na gyara kwanciya na asuba ta gari yan uwa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button