BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/21/20, 6:24 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , ,

????????6️⃣0️⃣????????

NOVEL DINA NA KUDI NE IDAN KIN FITAR MIN KO KA FITAR MIN BAN YAFE MAKU BA UBANGIJI YABIN HAKKINA AKAN KU DA DUK WANDA YA KARANTA BAI BIYA BA.

Satii biyu ya rage mu daga zuwa kasar Canada wanda yai dai dai da kwanan kin azumi baifi kwana goma ba tsaka ni.
Zaune yake a saman gadon ya mai da hankali ga laptop din shi daya tasa a gaban shi ya mai da hankalin shi gaba daya akan abinda yake yi din.
Dakin na shigo dauke da abinda ya sa in dafa mashi na nauin samun lafiyan maza na shigo dakin dakin da sallama na.
Har na isa saman dan katamin table din dake dakin na aje tire din da ke dauke a hannu na da kayan shaye shaye irin na maza mai kara masu lafiya karfi.
Bayan ma aje na samu wuri na zauna a kusa dashi ina fadin uncle ga yanan na gama hada maka idon shi na akan laptop din shi nima dai ba wai shi nake kallo ba ko da na zauna hankalina yana ga wani takarda da na gani saman gadon shi a lokacin.
Amma wanan kamar wurin da muka sayo ma Anty Aisha kaya mana, nake cewa dashi cikin dan, kallon fuskan shi dake duke saman laptop din.
Bai ce komai ba sai ci gaba da abinda yake yi yana murmushi nagama kallon takardan na aje inda na ganshi tunfarko tare da mikewa zan bar dakin .
Da sauri ya dan riko min hannaye na yana fadin ki dan dakata min in gama please komawa nayi na zauna tare da dan kai kafaduna saman gadon nayi rigingine.
Bai dade ba naji ya sauke ajiyan zuciya ya juyo yana dubana tare da kokarin rufe laptop din da yake aiki a cikin sa .
May zaki yi yanzu idan kin fita, yace dani, sai tambayan nashi ya bani mamaki sai dai ban kai karshen tunane ba naji yace dani zuba min ruwan maganin na.
Na dago a hankali zuwa gaban dan table din na fara tsiyaya mai ruwan ganyen maganin da ya sa na dafa mai.
Muryan shi naji tana cewa yanzu yaya zamuyi da mutane ga tafiya a gaban mu kafin azumi wanda ba zamu dawo ba sai bayan sallah insha Allah kin ga ban gida za ai azumi da sallah ke nan.
Juyowa nayi gare shi dauke da cup ina mika mai nace hakane Uncle a yadda kace za ai tafiyan ya amshi ruwan maganin dake tiriri a cup ya dan kurba yaji da saura zafi.
Ya dago ya kalle ni nace da sauran zafi ko kai ya gyada min amsa nayi nadan kada spoon a ciki ina dan motsawa a hankali yana zaune ya mayar da hannuwan sa baya ya tokare a saman gado.
Ya kura min ida baya ko kiftawa na dago kai ina cewa dashi sai dan ban san abinda kake shirin yi wa mutane ba kan azumin da sallah.
Yace in banda abinki yanzu ai wanan a cikin aikin ki yake ni dai kawai idan kin tsara sai ki sanar dani komai ake ciki da can madam maimuna ce take tsara min komai indan lokaci yayi.
Na ce a raina akwai aiki gaba na ashe don ban san komai a yadda take shirin ta amma dai ba matsala zan yi iya kokarina yadda ya dace.
Mika mashi cup din ruwan maganin nayi ya karba ya kafa kai bai cire ba sai da ya kurbe duk ruwan maganin a lokaci guda.
Ya kare yana ya mutsa fuska da alama bai da dadin sha ya dauki ruwa kadan mara sanyi ya dan kora a cikin shi.
Gauron numfashi na sauke ina fadin wai wanan maganin may ye haka kake sha kwanan nan yace ba matsalan ki ba ne yanzu.
Mikewa yayi tsaye yana fadin ke nake saurare yanzu don bani son a makara zan baki list din last year don ki san mutanen da ake aikawa .
Wurin wani dan drower dake dakin ya nufa yana tono list din ya juyo yana fadin sai dai ta wajen baba can gida ban san wa yanda kike so aiwa sadakan acan.
At list mutane hamsi maza nake son a raba ma abinci da mata hamsin suma a basu abin azumi dana sallah haka nakeyi duk shekara daga riban da nake samu na wurin masana,antan taya na.
Duk bayanin da yake min bai dago kai ya kalle ni ba sai da yake miko min takardan ne ya kare da fadin ki duba idan an samu kari sai a kara dasu.
Ni zan fita dama maganin nan ya tsayar dani yau akwai aiki a gaba ina son in kammala komai a yanda nake so shi a cikin satin nan.
Namike tare da daukar mai jakkan aikin shi yana gaba ina binshi baya har muka isa haraban aje motocin gidan bai dauki driver ba shida kan sa ya tuka motar ya fita.
Nayi ajiyan zuciya na juya zuwa cikin gidan zuciyana fam da tunanen nauyin da ya dora min akai yau a gidan.
Dakina na wuce sai da na kara yin wanka na gyara jikina na dawo na zauna na fara tunane gashi yana jaddada min kada nayi mashi delay a tsarin ni yanzu ta ina zan fara ne.
Anty Aisha ne ta fado min a rai da sauri na jawo wayana ina kiranta har kiran ya katse na sake danna kiran sai nayi sa a ta dauka.
Mungaisa tare da tambayanta yara da gida ta amsa da suna lafiya kafin ta fadi wani abu nace Anty Aisha ki taimake ni don Allah banda wani mafita yanzu sai gare ki.
Tana dariya tace niko matar yaya mai zan taimaka maki dashine haka a rayuwana nace bari kedai yayan kine ya dora min nauyin rabon kayan azumi da na sallah bana.
Dariya naji ta kwashe dashi tare da fadin Allah mun gode da ka nuna muna wanan ranan don wanan magana kika tayar min da hankalina da farko.
Ai wanan abin farin ciki a gare ki don dama matar yaya na can lagos ne take yo mashi sayayyan sai abinda muka gani zata bamu.
Nace to yanzu yaya zamuyi don kawai mu kawar da zancen anty da take son daukowa nan dai tayi min bayanin abinda suka samu last time sai na kwatanta na gani idan nabi list din zasu samu abinda yafi haka.
Godiya nayi mata ba tare da na tsaya sauraranta ba tace wai ko kin san kokarin da yayana yayi min na maganan canza gida nan take kora min bayanin abinda ya kasance tsakanin shi da maigidan ta.
Tace yanzu tunda aka fara zancen ba zaman lafiya tsakanin shi da kishiryar ta kullun fitina suke kwasa a tsakanin su ita yanzu ta matsu ta tashi ta bar mata gidan ta koma gidan ta.
Nace kin ga haka yafi aiyafi ance kazantar daba kagani ba sunanta tsabata shi takewa bakin ciki yanzu true colour din ta zai fita a tsakanin su.
Kin ga sai yasan halin ta na gaskiya shi take ma gudu dama tace gata ragguwa ko jikin ta bata iya gyarawa balle na diyanta.
Mun dai dauki lokaci muna magana akan gidan mijin nata a karshe mukayi sallama nan ta barni ina tunane ai ita tasan tana da kishiya ke nan ni yanzu ban san idan na dosa don wanan nauyin da ya dora min zai iya saka wani sabon tsana tsakanina da anty kuma.
Kamar yadda yace duk cikin kwana kin nan abinda muke fita ke nan yi daga sayan kayan masrufi zuwa tufafi da kayan tea da sauran su .
Ga kuma shirin komawan Aisha sabon gidan ta a wani sati da muke yi a makon nan muka shiga bauchi inda na samu taro na mutunci a wurin yan uwan Uncle da mahaifiyar shi don yanzu Aisha ta gama shigar dani a gare su ko.
Saida mukayi sallah muka shiga wurin hsjiya baaba don mu gaida ita tana zaune cikin kamala duk muka zube kasa a gaban ta .
Da fara,ata take muna sannu da zuwa da yaya hanya daga nan kuma suka fara dan hira da danta a cikin hiran ne yake mata bayanin tafiyan da zamuyi.
Wanda yasa muka zo kawo masu abin sallah dana azumi kafin mu wuce din tayi farin ciki da jin haka tace babana kokai fa abinda nake fada ma ke nan da dadewa cewa samun mace ta gari zai iya canza maka rayuwanka.
Yanzu gashi tun ba a je ko ina ba abubuwa suna canzawa sannu a hankali a wajen ka wanda wanan kokari ba kowane ya kawo shi ba sai ke mai sunan gwago na.
Na dago kai na dan kalle ta cikin mutunci da nuna alkunya gare ta tace eh a dalilin ki na samu farin ciki da hadin kan diya na da yan uwan uban su suka watsa min kawunan su a baya saboda son zuciya.
Yau gashi babana dake zaman yaya kuma uba a gare su ya dawo ya rugumi yan uwan shi da hannu bibiyu abinda na dade ina fatsn gani a gare su.
Yau ko wacen su tana farin ciki a dakin auren ta ta sanadin ki kin saka ya sauya masu rayuwan su na kunci don dan abinda suka gada a wurin mahaifisu dama yan uwa sun ciyen shi kaf gare su basu barsu da komai a hannun su ba.
Fatana gare ku yanzu shine Allah ya baku zuria masu albarka nima in ga jikokina ta wurin babana in runguma in goya kamar yadda ko wace uwa ke burin gani a rayuwan ta.
Kaina na dukar kasa don kunyan abinda ta fada a karshe sun dauko maganan da ya shafi gida don haka na zamay jiki zuwa inda kaunar shi take wacce baaba ke riko a gidan a wurinta nake jin ashe ya gyara ma sauran sisters din shi dakunan su a nan garin kamar yadda ya gyarawa Aisha nata.
Naji dadin jin wanan labarin da ta bani nan muka zauna ina fahintar wani abu a cikin hiran ta sai da zai fita ne hajiyan ta kirani na fito muka tafi.
Muna shiga part din mu na kai mashi runguma ya juyo yana kallona da mamaki nace Uncle naji abin alherin da kayiwa su anty suwaiba unangiji ya saka da alheri ya kara budi.
Murmushi yayi ya kamoni zuwa jikin shi tare da subbatan goshina sai ya soma magana kamar mai rada bakin shi a daidai kunne na yace ba wanan godiyan nake so ba kin dai ji abinda baaba tai muna addua a kai.
Kunya ne ya kamani na kara shigewa cikin jikin shi sosai ina dariya don kunya ina fadin insha Allah soon.
Ya jawo ni ya kara matseni sosai yana fadin da kyau bari ma yanzu mu fara gwada sa,ar mu mu gani ko zamu dace dariya ya bani da haka muka kwanta barci don muna da gajiya dama.
Washe gari muka tashi da aikin rabon kaya wa yan uwa da abokan arziki don motar kaya ta isa da daddare sosai ne.
Saboda hakan ne muka bari sai da safe banga zarah ba tun jiyan da muka iso tana gidan iyayyen ta tunda muka zo.
Saida muka share kwana uku muna abu guda ana hudu ne muka dawo abuja sai dai uncle ya hanani zuwa gida in kai wa mutanen gida abinda ya saya masu da kaina a cewar shi sai mun dawo zamu tafi gaida su.
Yaya Sani aka kira nayi mashi bayanin komai da wayan da zai ba na hada dashi da kayan suka tafi nan muka fara shirin tafiya wanda ni ta fanni na ba wani shirin da nayi don a shirye din nake dama.
Ina murnan tafiya sai ga shi yana fada min gidan anty zamu sauka indan mun tashi daga nan abinda ya sani cikin damuwa ke nan kuma.
Shiko naga ko a jikin shi bai damu ba kamar ba wani abinda ya faru tsakanin mu tun farko da ita sai ni ya bari da tarin damuwa a zuciyana.
Ana gobe zamu tafi ne dadare muna zaune falo yake cewa dani wai may ke damun ki ne kwanan nan naga kin shiga damuwa ?
Gwauro numfashi na sauke tare da kakaro murmushin dole a fuska na nace babu komai may kaga ?
Ya tsuramin ido kafin yace dani tun fa ranan da mukayi magana dake na sheda maki lagos zamu fara tsaya muyi kwana biyu naga kin ta da hankalin ki a gidan nan.
Ajiyan zuciya nayi wanda ya baiyana a fili nace uncle bawai nadamu bane kawai dai ina tunanen yadda zan hada fuskana da ita ne bayan abinda ya faru a tsakanin mu din.
Murmushi yayi ya kamo ni zuwa jikin shi yace kin san ko muna waya da ita a yan kwanakin nan kuma ni bata nuna min komai akan abinda ya faru din.
A raina nace kaika ai ba zata gwada ma komai ba nice dai matsala dama a tsakanin ku ji nayi yace dani kin dai san ba zan taba barin ta muzanta baki ba kina a maysayin mata ko ?
Nace amma uncle abinne da nauyi wallahi yadda anty ta rike ni ace haka ya kasance a tsakanin mu aikasan da nauyi wallahi.
Yace koma dai may ne yanzu sai ki bari idan mun je ayita ta kare yafi wanan boye boye da kike yi mata kamar mara gaskiya a tsakanin ku.
In ke kina da laifi ai itama tafiki laifi a wanan magana don ko dani dake itace ta hada mu don may daga baya zata kawo wani zance kuma.
Haka dai yayi ta karfafa min gwaiwa har na danji raina ya dan sake koma may nene gara dai ayita ta kare ma nace a zuciyata.
Washe gari yan uwa da abokan arziki sukayi ta zuwa sallaman mu yaya don sai da yamma ne zamu tashi.
Yaya saadu da anty Aisha kusan anan suka wuni damu shiga na alfarma nay duk da ba wasu kaya na kwasa ba ga tafiyan.
Mun sauka lagos da karfe shida da wani abu hotel muka wuce bamu tafi gidan ba a ranan anan hotel din muka tsaya.
Washe gari ma da yafita bai dawo banan ya barni ina ta barci abina hankali kwance sai bayan karfe biyu ya dawo yai wanka ya ci abinci yake fada min in shirya muje mugaida anty din da mijin ta.
Kayan da Anty Aisha ta zabar min don in sa idan zamu gidan na saka wani lace ne da suka sayo dubai lokacin da suka tafi sayayyan auren mu da ita shine na saka.
Sai sarkan gwalal da zaikai kimanin kudin nigeria milayan daya da dan kai wanda shi yafi tsada a cikin kayan da suka sayo da wasu takalma masu dan hill da duwatsu masu kyan sin shiga da lace din sune a kafana da jakkan su.
Na gama tsab ban san yana zaune yana kallona ba sai da na gama shiri na na dago zan yi mashi magana na samu ya kafa min idanuwan shi a kaina.
Murmushi nayi ina isowa wurin shi da sauri yace ashe matar tawa ta iya shiga ne haka ban sani ba.
Yace ai wanan shiga zaki sa yau madam ta rude tace koba safiyan ta bane da ta ke dauka yar kauye bata dace dani ba.
Ya miko min hannu a haka muka fito zuwa lifter muka sauka kasa inda muka shiga mota muka kama hanya.
Ko a hanyama sai faman zolayata yake yi wai zan hana shi tuki da kamshin turaren da na sa a jikina yace turaren yana da dadi shi nake son ki dinga amfani dashi ko yaushe.
Mun isa gidan musalin karfe hudu na marance lokacin na tabbatar da daddy yana gida don motar shi da nagani a waje abinda ya sani sauke ajiyan zuciya ke nan don nasan ko maue zai zo muna da sauki tunda yana gida.
A tare muka fito zuwa cikin gidan inda ya danna bell din shiga cikin gidan ba ajima ba na jiyo tafiyan mutum xuwa bude muna kofan nace ko yaushe suka fara rufe kofa haka kuma.
Zuciyana sai duka yake uku uku fargaba da tsoro suka mamaye min zuciya a lokaci daya sai dai hakan bai hanani yin addua a bakina ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button