BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/23/20, 5:39 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , ,

????????6️⃣2️⃣????????

NOVEL DIN NAN NA KUDI NE DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA YAR UWA IDAN KUMA KIN FITAR MIN DASHI UBANGIJI ZAI SAKA MIN A KANKI KAN NOVEL.

Ina kwance na saman kujera na dunkule a ciki naji ya sauke min kiss a goshina yana fadin Alhamdullahi kinga Allah ya amsa muna adduan mu yanzu ni na gama aikina saura naki.
Da sauri na bude idanuwa na dake lumshe na sauke su gareshi acikin sanyayyar murya nace dashi.
Uncle kada ka zamo mara tausayi mana kana nufin yanzu aikin nawa ne ni kadai kai ka gama naka ke nan ?
Ya mike ya samu wuri ya zauna yana fadin eh to ai gaskiya na fada don nayi yadda duk wani kosashen namiji ya kamata yayi dasa ciki a jikin mace.
Kin ga yanzu ke kuma sai kiji da amai da daukan nauyin ciki amma kada ki damu zandan rika taya daukan shi ta hanyan rage maki jin nauyin shi a jikin ki.
Sai idan haihuwan yazo kuma ai tare zamuyi labour dake ba inda zan fita ranan hararan shi nayi sai muka kwashe da dariya kuma.
Nace ashe kai har wahala kayi wurin dasa vikin a jikina yace ba kadan ba ai nayi kokari sosai wallahi yanzu jina nake wasai don na fara sauke nauyi na.
Murmushi nayi mai ina gyara kwanciya ban san lokacin da barci mai nauyi ya dauke ni ina dan tunane daga inda nake kwance.
Ban falka daga barcin ba shikuma bai tadani ba sai karfe takwas na dare lokavin yana zaune yana buda baki a falon kusa dani.
Jin motsin da nayi yasa shi dago idanuwan shi ya dube ni ganin shi nayi zaune yana yana buda baki da sauri na mike ina fadin anyi sallah ne Uncle ?
Yayi murmushi yana fadin kin falka yays jikin nace da sauki tare da sauko da kafafuwana kasan kujera da nake sama.
Yun kurawa nayi don in tashi zuwa sallah sai na gaza tashi wani irin jiri ya dauke ni da sauri ya mike ya taso zuwa inda nake yana fadin yi a hankali fa.
Kin san ba ke saya kike ba yanzu dole kibi sannu don Allah zama yayi saman kujeran tare da riko min hanaye na ya mayar dani ya kwantar yana fadin sannu bari ya dan sake ki sai ki tashi.
Na dan dade kwance a wurin sai da naji jirin ya sake ni na mike na shiga dakin kwanan mu wanka nayi don nauyin da jikina yayi a lokacin ko zai sake.
Na fito na tada sallah bayan na idar na dade a wurin zaune ina mika godiyana ga Allah tare da fatan Allah ya bani mai albarka.
Ina nike abin sallah nawa sai gashi ya shigo dakin dauke da abinci a hannun shi wanda noddle ne ya dafa a lokacin yake shan ruwa dashi kallo daya nayiwa abincin naji wani amai yazo min a bakina.
Da sauri na juya tare da boye fuskana ga ganin abincin dake gaba na tashi na shiga ban daki banyi komai ba na fito.
Yana zaune bakin gado yake fadin abincin bai maki bane kuma na cewa ban dai jin cin shi ne a raina kawai.
To may zaki ci ya tambaye ni nace zan dai ci fruits in na samu falo ya koma ya debo min fruits mai yawa zai juya sai gani na fito falon na karbi plate din a hannun shi da sauri na koma saman kujera na zauna.
A hankali nake taunan apple dana fara dauka naji yayi min dadi a baki na muna hira ina cin abina sai gashi na cin fruits din sosai.
Naji yace a lissafi na cikin nan tun kan mu tafi bauchi gaida hajiya kika samay shi idanuwa na na lumshe kawai tare da daukan dan annibi in jefa a bakina.
Tun wanan lokacin na ke samun wani kula na mussanman daga wurin uncle din nawa ciki kuma na bunkasa acikin koshin lafiya da samun kulawa a jikina.
Don ban damu da cin abinci ba saidai bani wasa da cin diyan itatuwa dama gashi akwaishi kasan da muke kamar banza.
Tun Uncle na fadan rashin cin abinci ya gaji ya kyale ni tunda yaga diyan iccen kawai zanci ya zauna lafiya a cikina abincin da raina ke so babu shi a kasan.
Alhdullahi uncle ya gama abinda ya kawo shi kasan kai ya kammala sunyi nasaran shiga da kayan su daga nageria sun kuma juya su sun zama kudi sun saro abinda suke so a can sun tura nigeria din.
Saura sati daya mu bar kasan zuwa kasa mai tsarki ya dauke ni mukaje shopping din kayan baby acewar shi yana da wuya ya samu dawowa kasan kafin in haihu.
Mun dawo a gajiye gida ba abinda nake so kamar indan watsa ruwa lokacin sai in dan kwanta kuma don in huta saboda naci gaba da azumi da na samu sauki.
Bayan na fito daga wanka falo na dawo inda yake zaune yana wani lissafi a cikin laptop din shi a lokacin.
Kujera na samu na zauna ina kokarin kwanta a lokacin sai ga kiran Faiza ya shigo min na dauka da sauri muka shiga gaisawa da ita din.
Yana zaune yana jin hiran mu take fada min wai ashe haka mukayi ma anty bana na hana uncle ya bata rabon kaya wa yan uwa sai ni na raba.
Nan dai take fada min irin zagin da nake sha gun anty yana jin mu sai murmushi yake yi kawai yana ci gaba da aikin shi mukayi sallama na dago ina sauke ajiyan zuciya.
Tare da fadin nikan na shigesu ga anty wai sai yaushe ne wanan abin zai kare a tsakanin mu ne wai ?
Bata tare da ya kalli inda nake yana aikin shi yace sai ranan da zaki bar mata mijin ki ta aura ma wacce take son ta aura min din.
Nace zan dai bita a hankali in gani ko zamu kawo karshen matsalan amma zancen in bar mata mijina ai ko a mafalki bata raya haka gare ni yanzu.
Ina wurin kwance har lokacin shan ruwa yayi na mike jiki a sabule na har hada muna komai anan mukayi buda baki shine yake bamu sallah kullun dani da shi.
Mun idar muka zauna cin abinci kowa yayi shiru sai cin diyan icce na nakeyi hankali kwance naji yace dani zanso kafin mu bar kasan nan mu koma asibiti su baki don kin san asibitin irin ta masu lalurar mune zallah a wurin.
Da sauri na dago kai na dan kalle shi nace uncle kana nufin duk mutanen da na gani a wurin suna da cutar dake karya garkuwan jiki a tare dasu.
Yace ai kin san kasan nan mafiyawan su kasan baki ne don haka kowa ke abinda ya ga dama a kasan shiyasa har suka kai ga bude asibiti irin haka.
A hankali na shiga tunane a raina don zama da uncle yasa yanzu har sai in manta cewa muna dauke da matsala a jikin.
Tuno abinda zan haifa nayi ko in haifi mai lafiya ko kuma kasin hakan Allah kadai ya sani banyi aune ba naji idona yana fitar da hawaye tausayin kan mu da abinda zamu haifa din ya kamani a lokaci guda.
Dago kai yayi ya dan kalle ko ban fada ba yasan abinda nakewa kuka a lokacin don yasan tunane na idan ya nufa.
Ji nayi yace dani kiyi hakkuri madam ni kaina wanan tunanen kanzo min a rai har a baya nikan raya ba zan yi aure ba balle har in haihu in mutu in bar yara a cikin maraicin iyayyen su.
Amma da na natsu sai naga ai Allah mai kashewa kima shine mai rayawa ga masu lafiya suna mutuwa subar marasa lafiyan abin daga hannun Allah yake don haka sai na barwa ubangiji sanin sa.
Haduwa ta dake kuma sai kika kara mantar dani daga damuwan da nake ciki a baya don haka yanzu na ragumi kaddaran da ubangiji ya jarabi rayuwan mu dashi a duniya.
Ga komai na rayuwa ubangiji ya hore ma rayuwan mu dashi amma sai dai muna rayuwan ne cikin BAHAGON RAYUWA.
Domin bamu san yadda abin zai kasance damu ba a karshe sai dai muyi fatan gamawa da duniya lafiya don wanan rayuwan yishi kawai ake a bahagon yanayi.
Nado kai a hankali muka kalli juna sai naji so da kaunar shi da tausayin mu ya dira min a zuciyana.
Nace Uncle mu namu kaddaran ke nan yazo muna a haka sai muyi fatan samun mai lafiya mutaima mu bashi tarbiya mai inganci koda bayan mu bazai samu matsalan rayuwa ba.
Naji ya riko min hannuwana da na sake fruit din da nake sha a hankali yana dan murzawa yace Safiya har kullun addua na shine mu samu zurian da zamu bari a duniya ko bayan mu zamu samu masu muna addua da tunamu a matsayin iyayye a gare su.
Addua na yanzu shine Allah ya sauke ki lafiya ina mai tabbatar maki bayan haihuwan ki zaku samu kullan yadda ya dace a gare ni.
Don a lokacin zan tabbatar maku dani din zsn zamay muna jigon rayuwa da ko bayan raina zakuyi alfari da samu na a tare daku.
Nayi murmushi tare da fadin insha Allahu a tare zamu raka da junan mu har diyan da zamu haifa din yace tau Allah ya bamu rai da lafiya din nace amin da sauri don yadda ya karasa maganan shi akwai tarin damuwa a zuciyar shi sosai.
Nayi ajiyan zuciya tare da kokarin hada kayan da mukaci abinci ina gyara wurin ina gamawa na shiga wanka don a gajiye nake lokacin.
Bayan shima ya fito wankan ne ina zaune bakin gado na mayar da hankalina sosoi a wayana ina duban sakon nin dana samu ranan.
Yafito daga wankan yake cewa dani ya kamata dai tunda anji sauki kuma sai in samu tukwaici haka horon yayi yawa mana madam ya iso gare ni yana kokarin taba min , , , .
Da sauri na manna mashi cizo daidai kunnen shi cikin rashin damuwa sai dai kokuwan da muka fara yana sai ya rama a lokacin na shiga rokon shi sai kirjina yake hari wai anan zai rama cizon shi na fara tsala mai ihu bai sa ya sake ni ba.
Sai dariya da yake kwasa yana fadin sai ya rama cizon shi anan din saman kirji dole na kyaleshi yayi abinda yake so din.
Washe gari muka tafi asibitin kamar yadda yace munga likita yakuma dora mu a maganin da zanyi amfani dashi da kuma yadda zan kare lafiyana dana jariri har reno da komai sai da yayi muna bayani yadda ya dace.
Yaje ya sayo maganin masu inganci da amfani wanda bazamu samu a gida nigeria ba sai a nan din ko wata kasa da taci gaba sosai a duniya.
Mun hada komai na ranan thursday muka tashi da dare zuwa saudiya inda zamu yadda zango a wata kasa kafin mu isa can din.
Sai dai duk wani sayaya da mukayi a canada ya tura gida Nigeria za a tafi muna dashi a cikin sabin kayan da zasu tura can.
Mun sauka a birnin madina direct inda already an sama muna masauki inda zamu zauna wanka kawai mukayi muka isa masallacin fiyayyen halita muka mika gaisuwan mu gare shi bamu dawo masaukin mu ba sai da mukayi sallah ishai acan muna ta rokon Allah saukin alamura.
Kwanan mu takwas a madina muka wuce birnin makka mukayi umurah sai mu muka shiga zama ko yaushe a massalaci barci ne kawai ke kaimu masaukin mu.
Ban taba sanin haka uncle keda yawan ibada ba sai wanan tafiyan namu don duk da yasan ina cikin lalura hakan bai sa mun dan huta ba sai dai ko yaushe yana kara min karfin gwiwa da fadin in dai jajirce in matsa mu samu wanan falalan.
Cikin ikon Allah Allah ya bani lafiya sosai dana samu kwarin yin abinda ya kaimu kasan mai tsarki ranan da aka sha ruwa washegari muka fara shirin komawa gida .
Ban samu zuwa sayayya ba shida wani abokin shi da matar shi suka tafi sun ko sayo muna kaya masu kyau koni naje da kaina iyakar abinda zan sayowa kaina ke nan.
Jirgin mu ya sauka lafiya a Abuja inda su yaya saadu suka zo taron mu da dawo kallo daya mutum zai min ya fahinci na samu sauyin rayuwana.
Na murje na zama wata katuwa na kara girma da cika ta ko wani sassan jikina haskena na asali ya fito sosai a jikina.
Rigar dake jikina ya biye cikin jikina sai may kaifin tunane ne zai gane hakan gare ni da sauri amma wanda bai san ciki ba sai yace na samu lafiya ne kawai.
Na dan jirkita don zaman jirgin da nayi don haka hutu kawai nake bukata a lokacin don tafiyan dare mukayi muka iso da safe.
Don haka muna shiga gida sallah na gabatar sai na samu wuri na kwanta sai barci da zazzabi mai karfi ya rufe ni ga samira da su Aisha duk gidan amma ban samu zama dasu ba a ranan.
Sunzo sun fahinci banda lafiya haka yasa jikin su yayi sanyi sai kuma aka shiga yi min sannu ina dunkule a cikin bargo shi yashi ya bani magani na sai barci ya dauke ni.
Ni dai har suka watse gidan ban sani sai mummy maman samira da yarta aka barmin so zauna dani a gidan sai da nayi kwana biyu sannan na samu zazzabin ya sauka min.
Na fito falo da yamma na zauna don jikin nawa ya dan kara sake min sosai ya shigo gidan anan ya samay mu zaune muna dan hira jefi jefi dasu.
Zama yayi a kusa dani yana gaida mummy da gida sai ya juya inda nake yana fadin jiki ya jikin madam ?
A hankali irin mutum ya tashi ciwo yadda yake ji nace mai naji sauki tare da lumshe idanuwana a hankali.
Mummy dake gefena zaune ta nisa tare da fadin amma sai ina ganin kamar wanan madam din ta samu karuwa ne don tun ranan da kuka dawo nake ganin haka a gareta.
Uncle yayi saurin dago kai ya kalleni na dukar da kaina kasa yace mummy na magana dake fa.
Nace aiba dani take magana ba dariya yayi ya gyara zaman shi yana fuskantar mummy din sai dai ina ga in jikin bai bari ba zuwa gobe sai mu koma asibiti.
Da sauri nace mashi ai naji sauki ba gashi na fito ba yace kin ci abinci nace kai nake jira ka aika a sayo min fruit in sha.
Mummy tayi saurin cewa bana fada maka ba wanan ciwon nata da walaki a cikin sa mutum yace baicin komai sai diyan icce kawai yake dura ma cikin shi.
Ya dan kalle ni yayi murmushi yace mummy ko acan shine kawai abincin ta duk abinda taci sai ta amaye shi shi kadai take ci a zauna lafiya.
Mummy ta sake cewa ai duk wanda yasan ciki ya kalli Safiya yasan tana da ciki ubangiji ya raba ku lafiya yaba rayayye mai albarka ya amsa da amin da sauri.
Mikewa yayi yana fadin barin in sa a sayo maki yanzu ki samu kisha ko jikin zai kara sakewa yace mummy dai ta gano abinda kike boye masu.
Murmushi nayi kawai idan yaso wasa sai ya juye kamar ba shi ba a gidan amma indan yan kai na saman kan shi zaifi sati daya yana dunkulan baki rai bai magana da kowa bayan gaisuwa.
Ni yanzu na saba da halin shi don haka duk irin yadda ya juya nasan yadda zan bi dashi a zauna lafiya masan mun dawo gida yanzu halin zai tashi mai.
Don a can ko yayi fushin bai jimawa yana yi zai sake mu koma daidai amma da zaran naga ya fara daure fuska nima sai in kama kaina dashi.
Washe gari ne mukayi baki daga bauchi inda yan uwanshi ne mata zallah hajiya baaba taba mota wai su zo su dubani su kuma ga sauksn mu.
Basu fada muna suna tafe ba sai ganin su mukayi Allah ya taimake ni mummy na gidan kafin wani lokaci tayi masu abinci mafi sauki don har Nura ta tafiko yamma yayi.
Dole na mike haka na ba dadi jikin nawa muka shiga hidimar baki a gidan ya dawo ya samay su don sun fita da yaya Saadu a lokacin .
Yayi murnan ganin su sai dai tunda suka gaisa ya shige dakin shi bai sake fitowa ba sai da naji shi shiru ne na leka shi dakin nashi.
Na samu ya fito wanka yana saye da jallabiya a jikin shi haka yasa na gane zai fita sallah ne a lokacin yana gani na yace ashe baki gare ki haka gidan ?
Murmushi nayi don jin abinda ya fadi nace wallahi aisun yi kokari da suka zo dubamu don basu taba zuwa ba sai wanan karon.
Gashi kuma naji suna fadin wai gobe zasu koma baaba tace dasu lalai su dawo a gobe din yace kai haba ai ta bari su dan kwana biyu dai.
Nace to sai kayi masu magana ai suma zasu so hakan wallahi don akwai gajiya a jikim su.
Tare muka fito ya wuce massalaci nikuma na koma daki na don inyi shirin alwala sai da na bi ta wurin su naga basu bukatan komai na wuce bayan sun dan jani da wasa irin ta kannen miji da akeyi.
Naji dadin kansan cewar mummy a gidan don tana da matukar kokari sosai bata jin nauyin jikin ta ko kadan kamar ba ita ta haifi Samira ba, don samira bata kaita kiza kiza ba.
Bayan na idar da sallah nan dai na dan kai kwance don yanayin jikin nawa da bai gama sake ni a lokacin wanda nasan gajiyan aikin da mukayi ya dan tambaye ni da zaman jirgi.
Yar uwa riban da kike samu wurin fitar da novel dina sai ki shirya dake da masu karatun novel din sata don taki ta samay ki a rayuwa muje zuwa in dai kin ce wasa da kallaman Allah kike yi .

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92Next page

Leave a Reply

Back to top button