BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
8/28/20, 11:45 PM – Ummi Tandama: BAHAGGON, , , , , , , , , , , ,
????????6️⃣6️⃣????????
Barci mai dadi ne ya dauke ni bayan sallah azahar inda na sallamay sallah a wurin na kwanta saman ties sai barci.
Muryan mummy nake ji sama sama a cikin barcin nawa take fada min ga dan uwan ki nan yazo da kyat na bude idanawa na ganta tsaye akaina.
A cikin idon barci nake magana da ita nace mummy kina magana ne tace eh dan uwanki ne yazo daga gida.
Da sauri na mike zaune don nasan da zuwan yaya sani din a lokacin na dan jama zaune bayan mummy ta fita daga dakin .
Na fito yana zaune yana cin abincin da mummy ta gabatar a gare shi cikin jin dadi da ganin shi ina murmushi nace yaya sani kaine a garin yau?
Shima murmushi yake da gani na yace wallahi nine Safiya ai tun jiya naso zuwa to nakai su babane da ummi wurin alluran mahajta shiyasa na bari yau na taso.
Nace Allah sarki kuna kuna shirin tafiya zaku taka kasa mai tsarki abinku yace wallahi kin ga ikon Allah ke nan Safiya.
Ai maganan baba kullun yanzu akan mijin ki yake yana yawan cewa bai san itin adduan da zaiwa bawan Allah nan a rayuwan shi ga gida kuma ga makka kusan lokaci guda.
Nace haka abin Allah yake sai yazo ma ta inda baka zata ba a rayuwan ka na fadi ina zama kusa dashi.
Yace wai naso ummi taga yadda Safiyan ta ta koma kamar wata irin hajiyan birnin nan wallahi safiya haka kika koma yanzu.
Dariya nayi mai nace kai yaya sani ho yau kuma yar kaunar taka kake zolaya haka ?
Yace wallahi ba zolaya bane kin koma din ne yace ashe maigidan ya fita waje sai yanzu nake ji a wurin mummy da nazo gashi kuma shiyace in shigo a cikin satin nan.
Nace ai ina ganin yaya Saadu ne zaka hani don yabar sakon ka a gunshi koda yake ba,ayi dani ba amma kamar sakon na babane.
Yace kuma dai baba bai sani ba da bai bari nazo ba don sai da yaja min kunne tace kada in yarda yace zai yimin wani dawainiya gidan zumu ba kasuwa bane.
Murmushi nayi Allah ne kadai zai saka mashi da alherin sa ai amma Uncle yana dauwainiya dayawa wallahi bamu kadi harda yan uwanshi haka yake fama dasu suma.
Yace haka aike so indan ka samu yan uwanka ma su su san ka samu ba kazo masu inuwar giginya ba hange daga nesa.
Fitowar Mummy daga daki ne ya katse muna magana inda take tambayan shi Rukkaiya yace tana can gidan mijin ta ai yanzu.
Nace banko tambaye ka labarin mutanen gida ba mun zauna muna zuba hira yace cikin dariya kowa lafiya lau yake wallai.
Nan itama ta zauna mukai ta hiran gida dashi yana bamu labarin kasawar shanun baba da yadda abin yazo mai amma baba ya rabe wa mutane naman duka yace shima ai a alheri ya samu ya saya.
Sai da akai kiran sallah laasar yafita sallah muma muka kama gaban mu daga can ya fice gidan ya nufi gurin yaya Saadu.
Na idar da sallah ke nan waya na yayi kara na dauka hajiya baaba ce ke kirana da ladabi na amsa wayan kamar tana gaba na a lokacin.
Mun gaisa da ita take tambaya muna dai lafiya nace mata lafiya muke tace ashe shi yayi tafiya ne kuma nace hajiya bai fada maku bane ?
Tace ina zai fada muna don yasan in ya fada bazan barshi ya tafi cikin yadda tsufa din nan nace ai lafiya nake hajiya tace to aidaiyi ta hakkuri kin dai san yanayin mijin naki yanzu ba wani don haka zama tare sai da hakkuri nace nagode hajiya.
Tace yaya wurin su Aisha nace ta kwana biyu bata shigo ba amma dai lafiya take dai tunda naji shiru munyi sallama har zata kashe wayan naji ta tambaye ni.
Yanzu ke kadai ne a wanan katon gidan naku dariya nayi nace hajiya ai akwai mutane agidan yan aiki suna tare dani ban yarda na fada mata mummy na gurina don ban san yadda zata fasara abinba.
Tace hakan yayi ni dai ba zaku ganin ba sai idan Allah ya sauke ki lafiya zan zo inga jika na tunda nasan ba a nan zaki haihu muna ba.
Nace haka dai ummina tace bazata zo gida na ba sai na haihu tace ai shine mutunci ina dadi kullun kana yawo gidan dan ka.
Tasan mutuncin kanta ne tunda ta fadi hakan nace indai ummi ne hajiya nasan ba zuwan zata yi cewa zatayi ga iyayye na da yawa su zasu zo tace wanan shine daidai.
Kada kiga laifin ta dariya nayi nace amma ai hajiya mu bamuki ko yaushe mu ganku ba in zamu samu.
Ina jin dariyan ta tace bakuma zaku samu ba mudai fatan mu ku zauna lafiya shine adduan mu kullun akan ku.
Mun gama wayan naji dadin yadda hajiya ke jana a jiki tana nuna min kauna kamar yar cikin ta ko yaushe.
Wayan na jona charji zan fita daga dakin sai ya koma yin kuka na juya na dauka anty ce ke kirana saida gaba na ya fadi dam.
Na dauka da sallama muka gaisa tace kwana biyu najiki shiru nace barin in kiraki nace wallahi anty banjin dadi ne shiyasa ban kiraki ba kwana biyu.
Tayi min yaya na kara ji nace naji sauki ta dora da fadin kodai abin arziki ya samu ne kin ga ai magana na nafita yanzu sai mu tara kudi da tushe.
Zuwa haihuwan ki mun san abin da muka tanada ba sai dai kawai aga muna bushashan mu ba da kudi amma kin tsaya kina noke noke.
Ke barin fada maki duk wata mace da kike ganin tana heleke da haka ta tara ga gumin mijin ta amma ke naga tsoro yayi maki yawa baki karban kudi yadda ya dace ki tatse shi.
Murmushi nayi nace anty matsalan shi baya bada kudi ne sai dai yayiwa mutum hidima tace aike zaki koya mashi bayarwan .
Yanzu dai kin ga kin samu ciki kila don haka sai ki mayar da hankali kafin haihuwar ki musan abinda muka samu a wurin shi.
Ni dai murmushi nake mata kawai nace anty zanyi yadda kikace din idan ya dawo tace ina ya tafi nace yaje Spain ne.
Allah dawo dashi lafiya tace tana kara jaddada min in yi kokari ina yagan wani abu a wushin nace mata to anty tana fadin nan da yan watanin ai mun tara maiyawa yanzu haka daddy su twins ba karamin karba nake a wurin shi ba kin gani na.
Kokari nake yanzu in fara sanaa in bar wanan aikin nagaji dashi wallahi kullun mutum baida hutu a rayuwan shi yana hanya aiki.
Nayi mata godiya muka kashe wayan fitan da banyi ba ke nan na zauna ina tunanen maganan mu da ita yadda zan mu kwashe a karshe.
Don dai ni ban fada mata ina da ciki har ya tsufa a jikina ita da ke maganan nan da wasu watanen masu zuwa can.
Nidai buri na shine in samu mu rabu lafiya da ita don haka na yanke shawaran tura mata wasu kudi da ya bar min a gida don kawar da maganan.
Bayan sallah magariba su yaya saadu da yaya sani suka shigo gidan na fito falo wurin su nan muka zauna muna gaisuwa dasu.
Yaya Saadu sai sheri yake min wai na tsufa sosai na wani kara girma kamar bani ba kodai biyu na kwaso masu ne ?
Dariya na kece dashi nace aida sai Samira ta dawo gidan nan don ba zamu iya mu kadai da mummy ba.
Yace kina wasa mummy sarai ta iya rike so akwaita da kokari fa nace ai na gani wallahi itace ra fito daga daki tana masu sannu da zuwa.
Ta tambaye shi mutanen gidan shi yace suna lafiya yaji suna fadin gobe anan zasu wuni ai nace nikan ai saidai kuyi hakkuri dani yaya .
Don Allah ya hada ni da miji mai kule yace ai shi yafi Safiya mace mai yawan yawo ai bata da dadi sai da aiyi hakkuri kawai.
Mummy tace banda samira don ko dazun ta kirani wai suna kasuwa yayi saurin kare ta da fadin sun je sayayya ne fa mummy .
Don ni banda lokaci shiyasa nake bata kudi ita taje tace kudai zama yan bariki ai kaida matar taka dariya yayi yana kare matar shi wai ai bata da yawo.
Yaya sani ya kawar da hiran yace Safiya ki ji mijin ki wai ashe shanaye yake son sai wa baba .
Ido na zaro waje yaya Saadu yace yasan shanun baba ya kasa ne ko nace eh da yaya sani ya bugo waya muna tare anan yaji amma bai mun magana ba tun lokacin.
Yaya yace ai ya fadi don yace wai kada a fada maki nima next week nake son mushi wirin su muyi sallama don zuwa wani satin sama zasu fara tashi.
Mummy tace nasan dai kafin su daya suna samun kin haihu nace mummy tun yanzu tace laila da wuya in ba hakana zai faru ba kan.
Nace wai idan na haihu ummi bata kasan sai yaya sani ya tare ni da cewa ba aikwai mutane a gida ba sai wayanda ke nan suyi buki mana.
Shiru nayi dan tuna katobar dana so yi a gaban shi nace ai fa akwai mutane kan dayawa a gida zan dai ga yan gida kan.
Munyi hira dasu inda yaya Sani yace zai bi yaya saadu gidan shi ya kwana washegari samako yake son yi kada a nemay su baya nan.
Nace wai Alhaji sani ke nan yace bari ke dai Safiya har fa mutane sun fara kirana da Alhaji wasu ma gani suke da farko kamar karya ne ba zan tafi ba.
Nace wai ina yaya Nura yace yana nan wallahi ai yaso ya bata rai sai da mama ta fita bayan shi ya shiga hankalin shi.
Nace ya sani ko idan zamu tafi badi in Allah yakai ran mu muje tare yaya saadune yace dayake shi baida aiki sai kai yan uwan ki makka ba.
Dariya mm ayi tare da fadin yaya Allah ne ya kawo mu lokacin hutu mummy tace don haka sai a huta kuwa ai lokacin abu ayishi.
Mun dan jima muna hira mukayi sallama suka tafi mummy ta hada min abinci wai inci ban son ci amma dole tasani gaba dole na ci shi.
Daki daya muke kwana da mummy a dakina don haka muke kawa wani lokaci mu dan hira da ita sai mun gaji mu kwanta.
Washe gari su samira suka zo gidan nan muka wuni da ita da yar uwar ta anan nake jin wai yar uwar nata ta samu miji aure a inda suke.
A cikin hiran mu ne nake fada ma Samira abinda ke faruwa tsakanina da anty zancen in tura mata kudi tace.
Amma dai wanan matar ta fadi kasa wallahi ita duk kudin ta sai tayi zari haka mummy tasa muna baki a maganan mu tace hakan da Safiya keyi yayi kyau su dai rabu lafiya da ita ba shike nan ba.
Kudin may mutuncin da tayi mata yafi kudi ai tunda halin ta ke nan ba sai ai mata yadda take so ba a rabu lafiya rashin yin zai haifar da wani rikici a tsakanin su ne kuma.
Tunda yanzu mutane ba tsoron Allah ne da su ba kun sani ko har yanzu suna ga bakan su na son mijin ta ya auri yar wanan dayar matan.
Nace mummy in dai ma auren zasu yi su barni da lafiya suje suyi tayi kowa ya tsaya a matsayin shi mummy tayi saurin cewa dani.
Umm umm yar nan kada ki soma fadin haka kishiya idan ba dace ba babu wanda ke son ayi mashi sai dai in ya kama dole shine ba mafita.
Ai da zaran ya kara aure yanzu duk wanan mutuncin da kikaga yana maki sai ya ragu namiji ai ki barshi kawai.
Idanuwa na na lumshe ina tunanen maganan ta idan uncle yayi min kishi ni ai na shiga uku ko a gidan mu ba balle gun bakin jama,a.
Samira ne ke fadin jifa kishirya Aishan ku sai da mijin ya bata saki kwanan don ta ishe shi akan zancen gida da motar da aka sai wa Aisha din ji da muka je take fada muna.
Nace ai kaji matsalar duk da ba mijin nasu ya saya masu ba amma bata bari an zauna kalau ba kuma ?
Tace wai har nan gidan Aisha ta biyo shi da masifa anan ya dankara ma yar iska saki sai gata kuma ta zube tana kuka a gidan.
Mummy tace shine ai matsalar matan yanzu dan abu ba abu ba su mayar dashi fitina su hana kan su shaka da abokan zaman su.
Nace ai wanan zaman namu mummy sai mu, mace ta samu gidan aure amma kishi sai ya rufe muna ido mukasa koyi da halin iyayyen mu na baya.
Kuma mafi yawan mata haka muke yanzu da bakin kishi bamu natsuwa muyi kishin hankali sai na hauka wanda idan mutum yaji sai ya rena masu hankali.
Mun wuni cikin dadin rai dasu Samira a gidan sai yamma lis yaya yazo ya dauke suka tafi daga gidan.
A gaskiya ina jin dadin zama da mummy don ba karamin debe min kewa take a gidan ba bata bari taga na shiga damuwa ko kadan.
Mahajjata sun tashi lafiya har sun sauka kasa mai tsarki inda suka bugo min waya na samu layin da zan dinga kiran su a can .
Yaya sani ne ke rike da wayan a hannun shi don haka idan zan kira ummina ko baba sai nakirashi yake mika masu waya muyi maganan da zanyi dasu wanda duk wayan namu gaisuwa ne.
Har yanzu uncle yana gurin tafiya bai dawo ba a wani dare ya bugo muna hira yake fada min ba zai samu dawowa ba daga can zai wuce saudiya ya sauke fari a can.
Nace Uncle kayi min wayo ke nan ka tafi saudiya au na manta fa ki shirya gobe kema zaki biyo jirgin safe ki samay ni anan.
Kai daddy kana son a koroni tun filin jirgin Nageria ke nan a yadda nake nan na tun kare su ai sai suce ban da hankali yace.
Ki fada masu ke fa matar uncle ne ai zasu bari ki wuce kawai nace uncle abin ya koma yar haka ne kuma tsakanin kai dai kawai ka yarda kayi min wayo yace to na yarda madam ai min afuwan ko nace ayi ma Uncle.
Munyi hiran sosai dashi kwana biyu aka hau arfat nan mahajata na jirgin yawo suka fara shirin dawowa gida acikin su harda uncle.
Sallah da kwana biyar na tashi da matsanacin ciwon mara cikin dare mummy ta rude duk da tasan cewa haihuwa ne yaya saadu ta kira baizo gidan ba sai tare da likitan uncle da wata nurse.
Don haka agida Allah ya saukeni lafiya da taimakon Allah da tasu na likitoci na samu na haihu karfe biyar na asuba.
Nurse din ce ta taimaka min har wankan yaro da komai da itace tayi nan a gaban mummy bayan yan aune aunen da sukayi min sukace kada aba yaron nono wai ina da matsalan kaikayi a jikina wanda ni san suyi hakane don kawai batar da sawu.
Likitan ya kara dacewa mummy ba kowa za a bari yasan yaron bai shan nono ba don yawan surutun mutane amma zan dan iya bashi lokaci lokaci kafin yayi wayo.
Don sun diba zan iya shayarwa na dan wani lokaci yaya yace tunda akwai abinda zai sha kawai kada ma na bashi nonon ita mummy tace hakan ma yafi.
Tace ta fahinta yaya Saadu ma ya gara gargadin ta kada ta bari kowa yasan zancen mummy tace ai ko samira baza taji ba don bama zata bari aga yaron ba.
Nan ya kwashe su ya mayar gida don lokacin har gari ya haska ko an fara fitowa shaanin yau da kullun.
Mummy ne ta miko min yaron bayan sun wuce na kalli yadda ya kwaso uban shi da kama wai jinin uban shi yafi kadfin nawa a cewar ta.
Murmushi nace mummy ke nan daga inda nake zaune ba tare da na karbe shi ba nake kwararo mai addua.
Barcin gajiya ne ya dauke mu a gidan dagani har mummy din sai tara na safe su yaya saadu suka shigo da su samira gidan.
Shigowan su ne yasa muka tashi basu jima ba sai ga Aisha ta iso kowa sai yaba kyau yaron yake yi don ya gado kyau ta ko ina daga iyayyen shi.
Aisha sai cewa tayi dasu yaron yafi kama dan ya dauko fuskan yan gidan su ne ni dai sai murmushi nake masu karshe ma barci nayi na barsu nan.
Ganin na sake komawa barci mummy tace su dawo falo su bar ni in huta yaya Saadune ya shigo dauke da madaran da za a ba yaron da ruwan zamzam .
Nan dai yadan bata lokaci yana buga ma mutanen su matar oga ta haihu yau na tashi mummy tace na danje na gasa kaina a bayi.
Naje na taba ruwa na dawo dai dai lokacin da Uncle ya sake buga waya akace dashi na falka daga barcin.
Wayan yaya saadu ya miko min yace madam barkan mu da arziki ashe an sauka bayana dariya nayi nace Allah ya sauke ni uncle Allah ya rufa min asiri baka garin na haihu baki alaikum.
Yace kudai kunyi min wayau naso ace nine zanyi karban haihuwan ai naga kalar rakin ki har video zan yi maki a lokacin.
Murmushi nayi nace wanan dai ya wuce ka yayi saurin cewa saura wani uncle rufa min asiri nace dashi da sauri tare da kashe wayan