BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/7/20, 8:07 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA , , ,
????????7️⃣3️⃣????
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Kamar yadda ya fada haka tafiya ta kamashi don an sake bugo mai waya da dare akan kayan da aka shigo masu dashi dole ya shirya da safe ya bar garin.
Sai mu ya bari a bauchin koshi don zai dawo buki ne yasa ya tafi ya barmu sai gidan ya koma muna ba dadi muna part din mu ni da khadija sai yan mata da suke dan shigowa wurin khadija jefi jefi.
Tashi nayi nacewa khadija ta zo mu shi wuri hajiya mu gaida ta na lura bata so zuwa ba don tana kallon wani india film ne.
Amma bata iya mussa min dole ta tashi muka shiga don Abba yana can gurin yan matan sun dauke shi da suka shigo dazun.
Tana zaune a falon ta kamar kullun tare da wasu mata da suka shigo wurin ta amma matan na shirin wuce wa don naji suna sallama da ita har daya ta mike tsaye daga cikin su.
Shigowan mu matan suka mayar da hankali sun su a gare mu, gaida hajiyan mukayi bamu tsaya wurin su ba sai muka nufi hanya shiga dakunan hajiya din.
Muryan hajiya naji tana fadin maman Abba zo ku gaisa da sarakunan ki matan baffanin ku ne suka shigo dubani.
Sai dayan ke fadin ko matar baba ne don kin san ai bamu santa ba tace dasu eh itace kin san sun zo don kawo muna yaro mu gani.
Haka mukaji ta haihu kwanaki da su suwaiba suka tafi suna can abujan, dawowa nayi na duka ina gaida su don cewa da baaba tayi sarakunnena su yasa na duka masu.
Masha Allahu suke fada yarinya ce ashe ikon Allah matar mutum ance kabarin sa har can akace ya auro ta ko baaba dai dariya tayi na mike ina jin suna magana a kaina ban tsaya sauraren su ba.
Dakin yan matan suna barbaje a dakin nasu na zauna a gefen gadon su suka shiga cewa ashe tare kuke da anty khadija tace eh.
Hira suke yi in dan jefa baki a hiran nasu amma hankali yana ga waya na da muke charting da samira tana zolayana wai naji dadin bauchi naki dawowa gashi ance uncle ya shigo abuja yau.
Nace da ita bauchi zama daram ai tace kina fara shi ai da mun biyo ki nan muma dariya ta bani har ina darawa ni kadai da wayan .
Yar wurin anty suwaiba da tafita duba girkin da sukeyi ta dawo tana fadin mummy hajiya tana magana dake.
Haka yasa na mike ina rubutawa samira yanzu idan kin gani ai baki gane ni saboda dadin da sarakuwa na ke bani kullun.
Na tura mata daidai ina isa falin hajiya nayi saurin kashe wayan na karasa ina fadin hajiya gani tace kunyi waya ko yace ya isa ?
Eh baaba ya sauka tunda safe ina ji aiki ne yasha mai kai be kara kira ba tun bayan isar nasu ta sake fadin yace yau yake so ya dawo in da hali nace haka ya fada baaba.
Nakai zaune a saman dan Center Capet din falon tace su dai maza basu mayar da tafiya a bakin komai ba ni gashi kullun ina waken zuwa duba masaukin ku acan amma ban tsayar da lokaci ba har kuka kai ga zuwa.
Nace ai shi uncle tafiya ko acan muke haka yake yawan yin shi idan ya kama mashi tace ai hakan na dakyau don bidan na kai ne.
Ni dai abinda zan fada maki shi ne ki kara hakkuri hakan danaji yasa na mayar da hankalina gare ta taci gaba da fadin ko can da maza sai a hankali balle mazan wanan zamanin da muke ciki.
Ko wani gida kika gani ta kalar tasu matsalan daban don haka idan ya na fushin shi ki bar biye mai kuna zama daya shi wanan fushi da zan iya raba babana dashi da na rabashi dashi tun yana yaro .
Don haka ya tashi shi yanzun ma ai ya rage sosai wallahi sai ma ince shigowan ki yasa ya daina abubuwa da dama ni ban san halin wanda ya dauko haka ba wallahi.
Murmushi nayi nace baaba ai yanzu na saba da halin shi ni abinshi bai kan damay tun farko Anty Aisha ta sanar dani halin shi shiyasa abin yazo min da sauki.
Abinci da suka gama suka kawo suna fada mata ga abinci nan an gama hajiya shiya dakatar da mu ga hiran tamu nan take fadin.
Ai ku zubo mutaru muci anan don zumunci wanan halin na hajiya yana matukar burge ni sosai don sam bata da matsala irin na wasu uwayen miji da nake gani.
Birbiscon gero sukayi da miyar taushe sai man shanu da za a zuba ga mai so da dan miyan dage dage ga wanda baison ci da miyar taushen.
Fitowa sukayi daga dakunan su nan aka shiga zuzuba abincin kowa yaja nashi plate din khadija ce ke tambaya na wai wanan wani irin abinci ne haka ?
Dariya muka soma yi mata nan hajiya ke mata bayanin akan abinci sai faman juya cibi take a cikin sa nan hajiya tace taci taji yana da dadi sosai.
Muna ci hajiyan hankalin ta yana wurin mu a ranta take cewa Allah ka shirya tsakanin yaran nan su zauna lafiya ban son fitina sam a tsakanin su.
Don yarinyar na da tarbiya sosai gashi sanadin ta abubuwa sun sauya ga rayuwan baba na sosai wallahi ba zan so ace yana yawan samun matsala ga auren shi ba.
Mun kare lokacin sallah yayi nace zamu tafi muyi sallah tace mu shiga daki muyi hijjabai na nan saman kujeran dakin nata don haka sallah ma anan mukayi .
Bamu koma shiyan mu don na tsaya na taya yan matan aikin abincin dare duk da hajiyan ta hana nace ko a gida hajiya ai nakan yi girki sosai .
Tace kin ko kyauta ma kanki wallahi yo may nene auren dama ai girki yana cikin ginshikin aure sosai amma matan yanzu basu gane hakan.
Sai su dauka wai wayewa ne daukan yar aikin da suke yi basu san wani daman su bane suke ragewa har ga Allah.
Kwanan uncle biyu ya dawo ranan da ake ta shiri zuwa kamun amare da za a yi don bai nan nima kuma fitan yanzu bai a raina don na saba da rashin fita tunda shike jawo muna matsala tsakani na dashi.
Sai ban mai da kai da mutafi ba misakin sha biyun rana ya shigo bauchi da gajiya don haka tunda yayi wanka ya kwanta wai yana son ya huta ne.
Khadija sun fita tare da yan matan gidan zuwa gidan bukin haka yasa na dauki Abba muka samay shi a dakin shi.
Barcin nima nayi a lokacin sallah azahar ya tayar damu sai kuma cin abinci misalin karfe hudu sai ga anty suwaiba ta shigo lokacin muna falon mu zaune da shi.
Sun gaisa tayi mai yaya hanya ya amsa mata da lafiya sai da suka gama gaisuwa ne tajuyo tana cewa dani Safiya yaya haka kuma naga baki shirya ba kun san kuma karfe hudu ne akasa program din.
Nace anty ku tafi kawai ba zan samu zuwa ba yace mata ina zaku kuma tace gidan su kawu wurin kamun amare zamu tafi yace oky, .
Bai sake magana ba sai ita ke fadin amma ko banji dadin rashin zuwan ki ba wallahi gaku cikin gari kin san fa mune zamu wakilci baaba fa.
Anty kiyi hakkuri ba zan samu fita ba don kin ga ma yau ya dawo tace oky yayi ta juya tana fadin to mukan sai in mun dawo zamu fita don sauran sunce mu hadu a can.
Dama don ke nazo don mu tafi tare daku din ashe ma baki samun zuwa din a dawo lafiya nayi mata ko kallon mu bai sake yi ba tunda ya kawar da kai.
Sai bayan fitar ta yake fadin saka lalle din ne har sai anje yin wani program can don sun bidia kawai irin na mata shiru nayi ban yi magana ba ya mike yana fadin bari in leka hajiya tunda na shigo ban fita ba.
Itako anty suwaiba tana shiga tana fada sai hajiya tace kada kiga laifin yar mutane kin san fitan ku na satin da ya wuce sai da suka samu fitina a tsakanin su.
Bar mashi matar shi a inda yake son ganin ta don Allah kin dai san halin shi ko tace amma baaba ai suma suna son idan nasu ya tashi a tafi ko ?
Bata san yana shigowa ba saiji tayi yana fadi daga bayan ta nace baza ta fita ba ku baku iya zama gidajen mazan ku kullun kuke nan hanyar gidan buki ?
Banzo nan da ita don yawon buki ba don haka kada na kara jin wanan magana ya fadi yana hararanta yana zama tace amma dai yaya zaka bari ranan buki ko ?
Ta tambaya tana kallon fuskan shi don son jin amsa kafin yayi magana hajiya ta amsa mata da cewa a a ranan buki kan zata tafi mana tunda suna gari.
Kallin mahaifiyar tasu yayi sai bai ce komai ba tunda ta yanke hukunci yake cewa shike nan ai amma ku rage wanan yawan zuwa bukin naku.
Ku wai mazajen ku basu kishin ku ne wai?
Dariya tayi tace kai yaya kowa fa ba irin ka bane mai kishi wai ko don matar ka tana da kyaune haka yasa baka son a ganta ?
See you yace don na hana ta fita shine wani abu baaba tace shifa raayin shine haka kin manta lokacin da kuke yan mata yadda kuke kwasa dashi ne ?
Safiyan ma tana da hakkuri wallahi tace tunda sukai aure fa bata je gida ba har yanzu ido hajiya ta fitar waje tace kai baba na kada ka raba yarinya da iyayyen ta don Allah.
Yace haba baaba may zata je tayi kullun ba suna waya ba tana jin lafiyan su kadai samu mai hakkuri ne tace amma wanan samiran taka ta farko ai shashani ce sarkin yawo.
Tsaki yaja yace don Allah ku bar dauko min maganan wanan macuciyar ban ma son in tunata a rayuwa na wallahi.
Mikewa suwaiba tayi tana fadin ni zan tafi kada a fara badani ba hararan ta yayi kawai ya kawar da kai ta fice tana mashi dariya hajiya na mata sai sun dawo.
Babana zumunci yana da dadi ba yawo bane haka don mutum ya ziyarci bukin yan uwan shi ka rage wanan tsananin da ke wa yarinyar nan don Allah ka bata freedon din kanta itama ta shiga yan uwanta matsin yayi yawa wallahi.
Murmushi yayi ya kawar da zancen yana fadin ai hajiya gara dana daure nayi tafiyan nan don mutane yanzu basu da gaskiya ashe laifin wanda muka tura odo kayan ne yayi muna wanan sheri.
Nan ya fara mata bayani komai da ya faru tace yanzu yaya zakuyi da kayan da kuka ce basu da kyau ?
Yace dole zamu karyar dasu a farashi mai sauki shi kuma mun sallamay shi don ba zan zauna da mahainci ba.
Nikan ina can part din mu damuwa da kadaici ya ishe ni a lokaci ga khadija dake debe min kewa ta fita yau don haka dagani sai Abbati ke part din namu.
Haka yasa na dauko waya muna hira da ummi na haka ya dan rage min zaman kadaicin da nake yi ni kadai babu abokin hira.
Idan banda wanan matsala na uncle da sai in ce banda matsala ko da muwa a wanan auren nawa don zai bani ci da sha da sutura mai kyau amma ba fita ko ina sai dai idan mutum yaji marmarin ganina yazo gidan.
Don na fahinci har da yan uwa na idan banyi da gaske ba uncle zai rabani da su ne don basu zaman zuwa wurina kullun ni ban zuwa gurin su.
Saukin abin ma yanzu da yaya Saadu ke kusa dani yana debe min kewan yan gidan mu sai ko yaya sani da kan shigo jefi jefi idan yazo yin wani abin.
Tun da ya fita gun hajiya bai dawo ba don yayi baki daga cab suka fice da mutanen bai dawo ba sai bayan sallah ishai ya shigo lokacin khadija bata dade da shigowa gidan ba.
Muna zaune tana min hiran event din da akayi sai gashi ya turo kofan dakin da sallaman shi sannu da zuwa mukai mashi.
Ya dan je nakin mirrow ya tsaya tare da jingina jikin shi akan mirrow din yana fadin naga alama khadija garin nan ya amshe ki fa ?
Dariya tayi tace kai wane ni yaya nida na matsu mu koma mu tafi gida inga ummi na da sauran yan uwa .
Yace ba yanzu ko mun koma sai na tafi Egypt na dawo zaku tafi gida da sauri na dago kai na dube shi ban kuma kawar da idanuwa na akan shi ba
Ya gane may nake nufi don ba haka mukayi da shi da gida zan tafi sai yace mu dakatar da zuwa gida sai idan mun koma daga bauchi zamu tafi.
Yes yace haka na tsara tsara yanzu don nima ina son in tafi in duba su idan ban samu zuwa tare da kuba tafiyan zai min nauyi ne daga baya.
Haushi bai bari nayi magana ba alokacin don khadija kuma dake wurin sai kawar da kaina da nayi daga duban shi kawai.
Sun dan taba hira da khadija sama sama ya fita ban bishi ba yana fita nace mutumin nan ban san abinda yake nufi ba a kaina khadija ?
Kiyi hakkuri kibishi yadda yake nidai da mun koma zan tafi don bazan tsaya jiran ku ba don babu ranan tafiyan ku gwago ma nasan ba zata tsaya yadda ta matsu din nan.
Ta yunkura tana tashi daga inda take zaune tace nasan ko ya dawo cewa zaiyi zai tafi Etopiar kuma dariya ta bani nace a a Niger zai tafi tace a ba ya zama sarkin yawo ba shi.
Nace ni kuma wanan bahagon rayuwan na sake fadawa idan ka fita wanan ka fada wancan idan bakai hakkuri ba sai ace kai mace sai aga laifin ka amma saboda Allah don kana aure sai ka watsar da iyayyen ka ai ba komai kudi ke sayawa mutum ba a duniya.
Sai da na gama abinda nakeyi na fito don duba shi waya yake yi don haka na juya na koma don shi wayan shi ba mai karewa bane da wuri.
Fita nayi zuwa wurin hajiya nayi mata sai da safe a lokacin take cewa ga abin bukina da suwaiba ta bayar a bani don ba ta tsaya ba sauri take yi da ta shigo.
Na karba cikin ladabi na juya na koma part din namu, daki na shiga na shirya tare da gyara Abba don yau khadija na san a gajiye take sosai a ranan don haka na dauki yaron na tafi dashi.
Koda na tura kofan ya fito daga wanka yana tsaye yana goge jikin shi jin shigowan mu yasa ya maida hankalin shi gare mu.
Yaron na shimfede saman godo na juya na fita naje dauko abincin shi duk da bai faye falkwa da dare ba sosai amma ban kwanciya sai da abincin shi a kusa dani.
Na dawo dakin da sallamata na shigo na samu wuri na aje a gefen da zamu kwanta fita nayi na rufo kofunan part din namu tare da kashe wutan ko ina na dawo dakin.
Zama nayi a bakin godan dakin tare da zuba tagumi a lokaci daya tare da dukar da kaina kasa may ke faruwa ne koma naji ya jefo min tambaya.
Na dago nace yanzu uncle don Allah bazaka bari naje gida naga iyayye na ba sai ka tsiru da wani zancen tafiya kuma bayan ba haka muka yi da kai ba kuma ?
Ke dakata may kike so dani ne wai so kike ki na aje abinda ke gaba na don na dadada maki ranki komay , ?
Da mamaki nake kallon shi don kaina ya daure sosai ga maganan shi yace nace bazaki ba sai na dawo Egypt period.
Ya juya ya dauki laptop din shi ya haye gado batare da ya kara bi ta kaina ba har ya fara latse latse sai kuma ya juya gare ni yana fadin .
Kuma bari kiji idan har zaki tayar min da hankali akan maganan nan gaba daya sai in ce bazaki tafi ba inga yadda zakiyi ?
Da mamaki na sake dago kaina kamar zanyi magana sai kuma na fasa naja bakina na rufe a raina nace ashe maza duka haka suke.
Nadan saci kallon shi aikin shi yakeyi bai kulani ba na gyara na haye gadon tare da rungumay dana muka kwanta tare da bashi baya.
Ban jima ba da kwanciya barci ya dauke ni don ban yarda na saka zancen shi a raina ba tunda naji ya fada ya tabbata ke nan ba zan tafi din ba sai ya dawo.
Sai dai na san cewa gwago da khadija bazasu iya kara lokaci haka ba suna jira na don kullun maganan su ta zuwa gida ne tun da nayi arbain.
Juya yayi yakalle mu ina kwance ina yadda na kwanta na kankamay yaron ga jikina kamar za a sace min shi a jikina shima yaron sai kwasar barcin shi yake yi hankali a kwance.
Rufe laptop din yayi tare da kashe wutan dakin ya hawo gadon ya kwanta rigingine tare da harde hanaye shi wuri daya yana tunane.
Don shi gani yake na canza mai yanzu bani bin umurnin shi ina son in tsiro da wasu halaiyan da bai sanni da shi ba a baya.
Ya rasa ko may ya canza ni haka lokaci guda ya zama mai dole yayi wa wanan halin da na tsiro mai waige tun da wuri.