BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/14/20, 10:25 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , , ,
????????8️⃣0️⃣????
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Mun dawo gida mun samu jikin inna ba dadi ranan basu kwana da ita da dadi ba don maganin da ake mata allura a fara aiki a jikin ta sai ya jikin ta sakewa.
Dakin inna muka wuce don har baba yana gida ranan bai fita wurin sana,a shi ba don yanayin jikin inna din mun samu ta samu barci mun dade a wurin ta muka fito daga dakin.
Yan uwanta ma da suka zo a waje suka zauna suna tsoron shiga dakin inda take don gudun daukan ciwon da akace masu anayi.
Sai da na fito muka gaisa da su ban tsaya ba na wuce daki bamu dade da dawowa ba naji shigowan Saadatu gidan ashe dama tana nan ta fitane zuwa sayo masu abu.
Ina daki zaune da ummi na muna hira naji muryan ta tana cewa ashe bakin birni sun dawo nace eh anty Saa kin shigo ashe tace dama ina nan na dan fitane dazun .
Mun gaisa na jajanta mata akan jikin na inna ta samu wuri ta zauna a dakin ummi din tace ashe kin je wurin Amina ne birni nace eh munje ziyara wurin Amina.
Mun dade a dakin muna hira da ita tana bani labari har ta fara sana,a da fridge din ta kayan kallo kuma tun ranan aka hada mata su yanzu bata da wani damuwa ko zaman kadaici
Kiranta akayi waje ta fita na mike ina son in yi wanka dama sai ga mama ta shigo gaida mu da dawo nan na tsaya muka gaisa tana fadin ai babaku bai san zaku kwana ba ya dawo yana fada jiya.
Nace Amina tana da muhinmanci a wurina shiya naje na kwana mata daya yanzu saura kuma in tafi kauyen su ummi inyo ziyara in dawo in fara shirin tafiya don mun kusa cika kwanakin da aka bamu.
Tace au har can zaki tafi ashe nace ba dole inje in duba ma ummi yan tsofinta ba kada ta hake ni daga inda ummi take zaune tace ai ba a saki zuwa dole ba.
Dariya mukayi mata mama ne ke fadin ba a sata zuwa dole ba amma idan ta koma bata je ya isa ai mata gori ai tazo taki zuwa duba su.
Ummi dai dariya tayi da jin dadin zai tafi in duba yan uwan ta kuma nace kwana biyu zanyi a can fitan mama dakin yasa na mike na shiga bayi na watsa ruwa a jikina.
Na fito na samu shafiu ya dawo yana cika yana batsewa a falon ummi nake tambayan shi may ke faruwa shafiu yace bakomai cikin fushi.
Nace kuma ga yanayin ka ya nuna fushi kakeyi mana shafiu may akayi maka waya taba min kai nazo kusa dashi na zauna.
Ya wani turo baki a shagwabe yana fadin wai da su maimu zaki tafi indan kin tashi bayan na fada maki zan biki.
Murmushi nayi tare da dafa shi nace shafiu aikai namiji ne kuma in na tafi dakai wazai taimakawa ummi ga sana,an ta ?
Yace namiji bai zuwa gidan yayan shine akace nace kana zuwa shafiu idan anyi hutu sai yaya sani yakawo min kai hakan yayi maka ?
Dan shiru yayi kafin yace indai zaki sa ya kaini yayi mun don wallahi ina son zuwa wurin ki hutu anty nace zakazo shafiu.
Yanzun dai ka shirya zamu wurin su kawu dole gobe mukai masu ziyara kafin in koma yace ni sai kauye za a dani kun tafi birni bakuje dani ba ?
Wai shafiu yaushe ka zama haka ban sani ba bann saka da yawan hayayya ba fa ada ?
Ya mike yana fadin komai sai ace waini namijine namiji akace ba a yi dashi wallahi nima zan bar gidan nan ne.
Barci nayi ranan ban ko fito tsakar gida ba din ina son in dan huta ina jin ummi suna faman rikici da Abba a falon ta amma na kasa tasowa inzo inji may ya samay shi.
Har yaron yayi shiru ban sani ba don barcin dana koma a lokacin shigowan yaya Nura wuri na yasani tashi zaune.
Falo naa fito wurin shi mmun gaisa nace yaya Nura yaya akayi ne yace wallahi Safiya garin ne yayi zafi yanzu sam babu aiki tunda dama ya kama mutane sun mayar da kudin su gona.
Nace yanzu may ye shawara yaya ya shafa kan shi yana dan murmushi yace zuwa nayi wurin ki ki dan taimaka min da wani abu in dinga juyawa.
Shiru nayi ina nazari a raina sai nace yanzu dai ba wasu kudi nake dasu anan ba yaya gashi zan shi kauye wurin kawun ne na sai dai indan mun koma idan zaka iya shigowa Abuja sai musan abinda za ayi a can din .
Zaiyi magana na rigashi fadin barin in baka dubu ashirin duk da nasan zasuyi ma kadan amma kayi hakkuri dasu jibi zan koma ba dadewa zamuyi ba dama sai kazo mu san abinda za a yi don yaya Saadu na can.
Bva zai rasa wurin da zasu saka ba yafi wanan aikin da kakeyi a nan zaifi ma sauki nake gani idan zaka iya idan kuma kafi son zaman nan zan sama maka abin juyawa yace sai nayi shawara da mama ummi dake kofa tace shine daidai.
Na shiga daki na fito mai da dubu ashirin din na kawo mashi ya mike yana godiya ya fita daga dakin sai lokacin ummi tayi magana.
Kin san dai Nura ba kamar Sani yake ba karki saka shi a cikin harkan mijin ki ya yaudare shi bake kadai abin zai shafar mu nan zai iya shafan mu.
Nace har yanzu yaya Nura bai daina halinsa bane ummi tace ina zai daina tunda bajin maganan iyayye yake yi ba.
Shi haka rayuwan shi take a tsatsaye yake har yanzu baya ganin kowa da mutun ci a idon shi ko gidan nan ya shigo bai iya gaida mutane yanzu ma mamakin ganin shi a wurin ki ai.
Murmushi nayi nace amma duk abinda yake ummi ai bai kawo gare ki damu ko iya wanda ya shiga harkan shi yake tsayawa.
Ina dai ja maki kunne kisan abinyi tun wuri nace ummi ki bari a gwada shi ko sau daya ne kin ga ai mama bata jin dadin ganin da yaya sani kawai muke mu,amula a gidan nan ranta baya dadi nunawa kawai ne batayi.
Ba fa gwadawa a fili amma nima nasan abin yana damun ta nace ba a dukiyar uncle zan sakashi ba ai ummi nima nasan abinda nakeyi.
Washe gari muka isa garin kakan nina mun samu taro na mutantawa a wurin su irin taron da mutanen kauye kiwa wanda suke mutuntawa aikai muna a gidan.
Su yaya sani basu kwana ba suka dawo bayan sunci abi mukai sallama dasu suka tafi naji dadin kasan cewa a cikin yan uwan ummi danayi saboda yadda suke nuna muna don dukkan mu yaran ummi mukaje garin.
Mun so zuwa da ummi amma baba yahana ta zuwa don haka muka zo bada ita ba sai yamma mazan suka dawo daga gona wurin aiyukan su don da aiki noma da kiwo suke dogara su.
Sai da suka huta muka bisu daya baya daya muna gaida su a part din su najin dadin ganin mu a yadda sukaga munzo mu duka.
Mun fi dadewa a wurin kakan mu wanda tsofa ya kama yanzu har dan rankafa abu ga dogon mutum wanda ya manyanta don ko diyan shi ba yara bane balle shi tsawo rai daine daya samu yakai hakan.
Washe gari da muka tashi jumma a ne don haka kowa na gida basu zuwa gona duk ranan jumma, a ranan suke samu su dan huta a gida don yin sallah jumma a din.
Tsaraban da muka kawo masu ake ta rabawa a kofan kakan mu mace duk da ita ta haifi ummi mu ba wanda ta haife ta ta rasu tun ummi bata girma ba.
Amma ta rike su kamar ita ta haifesu yadda ta rike su a gidan nan suka fara shigowa godiya a gare mu duk mazan shaddan da ya bani na kawo masu dama na aje masu nasu.
Mun je wurin kakan mu gaida shi sai jan mu da hira yake yi yana bamu labarin rayuwa shi na baya yana kuma fada muna dan tarihin ummin da tasowan wata har auren ta a kauyen da tayi ta koma wurin gwago a garin mu.
Abba ke rikici a gaban shi yayi murmushi yace miko min shi nan khadija ta mika mashi yaron ya dauke shi tare da kara shi saman kafadan shi daidai saitin kunnen yaron ya dora bakin shi a hankali yana karato adduan daba mu san may yake fadi ba a lokacin.
Kara juya shi yayi bangaren hago ya kara maimaita abinda yayi mashi a bangaren dama ya gaba sai ya dan hura mai fuska take yaron ya zauke numfashi a hankali yake rage sautin kukan da yake yana ajiyan zuciya shikuma yana dan jijigashi a hankali saman kafadan shi har yai shiru ya lafe sai ajiyan zuciya yake sakewa a hankali.
Mudai mana kallon abinda yakewa yaron yace idan kunga yana kuka haka daukan yaro akeyi aimai kallaman shada sau uku a ko wani kunne da bissimilah zaku fara kowani sai kuga yaro ya yi shuru koda kuwa shedanune suka shafi yaro yana yawan kuka akai akai.
Nace aiko mun karu tsoho ya nisa tare da tambayana jiki na nace da sauki sosai yanzu gaskiya don ina shan magani kuma ina cin abinda zai gina min jikina ko yaushe.
Yace kin dai daina amfani da fitsarin rakumin ko don banga kin kara aikowa in sama maki ba nace gaskiya malam tunda na shanye wanda ka bani da farko ban kara amfani da shi ba kuma naji dadin shi sosai wallahi.
Yace tsiyan ku ke nan yaran yanzu baku tsaya ma magani har kuga aikin shi da kyau sai ku camza wani .
Nace tsoho ba inda zan samu ne a can kaga muna da nisa sosai yace kinzo a saa ai yau jumma a za a soke rakumi ayi tom tom din shi zan sama maki wasu abubuwan amfani da dama a ciki sai kije kiyi amfani dasu can idan kinji dasin su keda kan ki zaki aiko a kara maki wani.
Godiya nayi mashi tare da dan bashi kudin da na riko mashi duk da ina ganin basu da yawa amma shi sai washe baki yake yana saka min albarka.
Tashi mukayi daga wurin shi wanka mukayi muka shirya muka zagaya gaida dangin da suke a cikin gari
Bamu dawo ba sai yamma lis agajiye kowan mu yake abincin da suka aje muna na rana muka samu ba wani ci mukayi ba dama na bada sakon a saya min ganye da kwai da man shanu mai yawa da zan koma dashi Abuja.
Ganye nace khadija ta dan gyara min naci har dare dashi na kwanta a cikina don banji wani yunwa ba kuma.
Washe gari sai shirya muna tsaraba suke yi kin san kauye da kara wanan ya kawo wanan ya kawo sai gashi mun tashi da tsaraba mai yawa a gidan.
Sha buyu rana driver dasu yaya sani sun iso daukan mu bamu jima ba mukayi sallama dasu muka kama hanyan gida biyu da wani abu muna a cikin gidan iyayyena.
Kwana biyu yarage muna a garin sai shirya muna ummi da mama keyi nan ma dai tsaraban ake ta kawo min don duk wanda na ba tsaraba dana zo sai da ya dan samu abin da ya bani da zan koma sai dana ragewa su ummi wani abin.
Ana gobe zan koma ne da safe sai ga maimu da kuka ta samay ni wai baba yace ba zan tafi da kowa cikin su ba.
Hakkuri na bata nace zanyiwa baba magana da yamma da yadawa gida naje gaida shi yana zaune yana cin abinci mama na gefe shi na shiga wurin shi.
Gaisawa mukayi nayi mai yaya kasuwa ya amsa min cikin fara a na samu wuri na tsugun na yace kuna ta shirin komawa gobe ko nace eh baba.
Shine ma nazo fadama zan tafi da maimu da hindatu suyi min hutu idan hutu ya kare sai a dawo dasu.
Dan jimm yayi sai yace Safiya maigidan ki bazai ga rashin hankali mu ba kuwa nace ko daya baba babu ruwan shi ai shi bamai zama gida bane ko yaushe.
Sai yayi kwana nawa ma bai gansu a gidan ba idan ba ya kama ba yace nasan halin yaran nan basu jin magana kada kina zaman ki da mijin ki lafiya su je su tayar maki da hankali can.
Nace baba babu komai wallahi ai khadija ma baiso ta dawo ba itace ma ta matsa zata dawo din yace dayake tasawa kanta shiriritan son wanan yaron ba.
Niko da raina da lafiya na wanan abin ba zai yuyu ba muddin ina raye shirmay ta dai takeyi kawai.
Mun dan taba hira dashi yana ta min nasiha akan zaman aure da zaman takewa a cikin mutanen da ban saba dasu ba har magariba ya gabato muna wurin.
Haka ya mike yaje yayi alwala ni kuma na koma cikin gida ina shiga mama ta biyo ni dakin tana fadin kai Safiya ke kika iya da halin mahaifin ku.
Nace mama nasan halin baba don haka ban fito mai kai tsaye da daukan su zanyi ba sai na laba ga hutu ba sai ya gansu ba kuma ko yayi magana nasan abinda zan fada mashi gaba.
Yaran da sukaji za a tafi dasu suka fara murna mace kada su dauki wani kaya mai yawa kada baba ya gane tafiya zasu yi kayan sallah ku kawai zaku dauka.
Tun da safe ana ta fita muna da kaya waje duk sai naji raina ba dadi a lokacin ina kuryan dakin ummi ina shiri ta shigo dakin nace ummi amna dai ya kamata kizo kiga gida na idan na koma gaskiya.
Tace ba iyayyen ki sunje sun gani ba zuwan may zanyi kuma ni nace haba ummi kamar wace bata da gata ai dai dake da baba ku dan leka watarana ko ?
Tace ba dai yanzu ba sai maigidana zaiyi aure ko nace haba ummi khadija dake zaune gefe na tace kyale ta ninan zan rakota har Abuja idan kin koma.
Gwago dasu mama jimmai sun shigo sallama na dasu Saadatu har da mijin ta da kishiryar tan nan na fito tsab dani na shiga wurin baba na rusun na tare dasu maimu nace baba zamu tafi asa muna albarka.
Yace kullun cikin sa maku muke safiya nan yayi wa su maimu fada sosai na su natsu har su dawo lafiya na shiga wirin inna mukayi sallama nayi mata Allah ya sauwaka.
Na fito kofan gidan namu ya cika da jamma a ina tayiwa mutane ban kwana na shiga mota Adamu ya zo mukayi magana dashi ba wanda yaji may nake fada mashi.
Sai dariyan da yayi yana daga muna hannu nan muka barsu tsatsaye suna bin motar da kallo idona na lumshi ina jin wani iri a zuciya na gida a kwai dadi wallahi indai kazo da zuwan bakunta nace a raina.
Suka yaran sai farin ciki sukeyi yau zasu birni duk sun sallami abokai da yan uwa sai washe baki sukeyi cikin murna.
Sai karfe biyu da rabi muka shigo garin Abuja inda muka wuce gidan mu direct daga shigowan mu kanne na da suke ta surutu sai suka koma kallon gari.
Mun iso gidan duk zuciya ba dadi har lokacin a hankali na furta Alhamdullahi a fili tare da yunkurawa ina shirin fita daga motan ji nayi sunce anty mun iso ne eh kawai na iya ce masu.
Security din ne ya fito ya bude muna mota tare da fadin sannu madam sannu ismail na iya fada mai nace nagode.
Fita nayi daga motan tare da amsan Abba dake jikin maimu yana barci saida na karbeshi suka fito daga motan tare da daukar min jakkan hannu na muka nufi kofan shiga gidan.
A rufe gidan yake na dan danna bell ajima kadan sai aka bude Nura ce ta fito tana ganin mu tace ah wellcome madam.
Thanks nace mata ta matsa muka shiga tare da kanne na dake bina a baya tsakiyan falon na nufa na shimfede yaron saman kujerun falon da suka sha gyara.
Na juya naje kuna Ac da fanka a lokaci guda take falin ya fara canza yanayin shi daga zafi zuwa sanyi.
Har yanzu su maimu basu zauna ba nace dasu ku zauna mana gaku kamar masu tsoro da sauri suka zauna a takure saman kujeran duk sun matse juna.
Zama nayi ina kokarin dauko key din daki na a cikin jakka na can kasa naji key din na fito dashi daidai lokacin da Nura ta kawo muna ruwa da juices din kwali gaban mu da kofuna ta aje.
Goran ruwan na dauka na fara tsiyaya a cup tare da masu nuni da su dauki ruwa su sha mana suma da sauri kowa ta dauki cup din zasu zuba ruwa nace bazaku sha lemon bane muna sha maimu tace min da sauri.
Bayan na shanye ruwan na aje cup din na mayar da jikina ga makarin kujeran tare da lumshe idanuwa a hankali na danyi tunane sai kuma nayi ajiyan zuciya.
Wayana yayi kara daga cikin jakka na na jawo jakkan ina duba wayan yaya Saadune yake kira na alokacin na dauka tare da fadin hello yaya .
Yace Safiya yaya hanyan na amsa da Alhamdullahi yaya.
Yace kuna ina yanzu ?
Gamu gida yaya na bashi amsa a takaice.
Yace ashe kun iso ke nan , ?
Eh yaya
Yace OK sannun ku da zuwa gani nan tafe yanzu mu gaisa
Sai kazo yaya kawai nace na kashe wayan ina kara mayar da kaina yadda yake da farko.
Mikewa nayi na bude dakina yayin da su malam musa ke ta shigo muna da kaya cikin gida shi da wanan security din Nura ta tarawa daidai kofan kitchen din mu.
Dakin na shiga sai duhu na kunna wutan dakin tare da jefa jakkana saman gado kaya na fara cirewa a jikina na shiga wanka na dan dade ban fito ba.
Sai can na fito na sauya kayan jikina na samu Abba ya tashi daga barcin da yake yi tv na kunna kafin in zauna na kalli dining naga Nura ta jera muna abinci a wurin.
Makulin da nafito dashi daga daki na bude wani daki a kusa da na mummy nace da su maimu ku taso kuga dakin ku ko.
Da sauri suka taso zuwa inda na kira su wanda sai kayi dan tafiya zuwa wurin nace nan yayi maku ko yanzu dai gaku a cikin gidana.
Fushi ya kare maimu da baba dakin muka shiga dukan mu sai baza ido sukeyi kamar matsorata a raina nace rayuwan kauye baiyi ba gaskiya.
Ji yadda yara ke wani iri kamar wa yanda basu yarda dani ba ko wani saman gadon dakin na zauna nace suma su zauna Abba nake kokarin cire ma kayan jikin shi a lokacin.
Nace kunga ga bayi nan don Allah banda kazanta don shi zai hadani ku ba komai ba a kullun a wake bayin nan sau uku ko sau hudu a rana.
Taso muje in gwada maku yadda zakuyi amfani dashi nan dai na nuna masu komai nace su kwaso kayan su sushigo dashi dakin a tare muka fito ina ce masu suyi wanka muci abinci.
Sun gama sun fito shima Abba wanka nayi mai muka fito muka ci abinci muna kan ci yaya saadu suka iso gidan shi da samira.
Ina ganin su nace chewgun ke nan kina lake ko yaushe masu miji ke nan ina kuma kuka baro min diyata ?
Tana wurin uwarta tace ganin yaran yaya ce ina kuma kika kwaso wayan nan yan kauyen haka hararan shi nayi nace ina kaga yan kauye kuma anan ?
Tace ke ko kin so dawowa ji yadda kika koma kin je kin cinye ma tsofi abinci kin ki dawowa.
Na lumshe idona nace bari samira wallahi gida akwai dadi kamar karna dawo nake ke ji sai naga gidan nan yayi mi wani irin girma wallahi ba hayaniya ba motsin kowa.
Kajiki da wani zance har yaushe kika bar nan din da zakice wai wani gida dadi ai da ki zauna gida in baki dawo kin samu munyiwa uncle din ki aure ba.
Samira ke da kanki ke fada min haka lallai wata shigowan kishirya ki ya tsaya don wanan watan zamu kawo maki wanan karfen kafan da ta leke wa yayana.
Don Allah Safiya ki daina zancen wanan gajan matar da ta tashi aiki don wulkanci ta rasa wanda zata lekewa sai mijina yar iska.
Yace ai shike nan tunda kin san takon ta kuma da tayi maki tsiya bani go ahead kawai safiya na shigo da hafsat kai tsaye