BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/21/20, 9:58 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON RAYUWA, , , , , , , , ,
????????8️⃣5️⃣????
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
NOVEL DINA NA KUDI NE DON ALLAH DON ALLAH IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA DON DON SHIGA HAKKIN WANKI DON GIRMAN ALLAH
Ke kuma mai fitar min da da novel nasan basai anje lahira ba ubangiji yazai daukan min fasan akan ki don kin nuna baki da imani da tsoron Allah a fili.
Mai imani bai wanan halin ko yaya yana nuna tsoron Allah ba zance dake komai ba amma zaki ga ni a rabon ki shi amana bibiya yake ta inda baki zata ba.
Jin dakin shiru bakajin komai sau karan nauran wutan dake aiki a dakin sai ko ni da nake sauke numfashin wallah har wani zufa nake yi don tsoro da fargaba alokaci daya.
Da kyat na yunkura na mike na sauke kafafuwa na daga saman gadona cikin karfin hali na nufi dakin shi don babu kowa a falo gidan yayi wani tsit a lokacin.
Ganin kofan shi a bude ya tabbatar min yana gidan har wanan lokacin bai fita ba ke nan da far gaba na tura kofan a hankali na shiga dakin.
Ya tsaye bakin window dakin dake kallon haraban gidan ya harde hannaye shi duka biyu a saman kirjin shi kamar bai san na shigo dakin ba ya nuna min.
A hankali jikina a sanyaye na karasa inda yake tsaye har na iso gab dashi na sa hannu na da nufin in rungumay shi ta baya ya juyo a zafafe cikin zafin rai ya kwashe da wasu irin lafiyayun maru guda biyu masu kyau.
Sai da na kai kasa ban sani ba ya nuna ni da dan yatsan hannun shi yana fadin ashe baki da mutunci baki da tausayi ban sani ba Safiya.
Ashe ke mutumiyar banzace nake zaune da ke ban sani ashe baki da tsoron Allah a rayuwan ki ban taba zaton haka ba a gare ki ban taba ba Safiya.
Ashe daukan da nake maki ba hakana kika dauke ni ba ke may nayi maki da kike son ki cuce ni haka da zafi may na rage ki dashi wanda na kasa baki kike son saka min da wanan abin da kike shirin yi min.
Ni dai ina duke na rike kumci na sai hawayen da ba kuka nake fitar wa wani nabin wani iri rike da kumatuna da yasha mahaukatan maru gare shi.
Kuma cikin maganan da yake fadi wani ma ban fahintar shi a lokacin wanda nake ji kuma ta yaya zan fara bashi amsan su don suyi min yawa a lokacin.
Naji yace uban wa ya baki wanan magani a ina kika samo shi yau naji na tsane ki nayi dana sanin auren ki dana nayi safiya tunda baki so na da karuwa banga dalilin zama dake ba a rayuwa na.
Dago kai nayi na kalle shi karo na farko bayan marin da yayi min da hawaye na shabe shabe a fuskana.
Mikewa nayi daga inda nake tsam ina shirin fita dakin wani tsawa ya daka min yace dakata baki bani amsa na ba tukun .
Uban wa ya baki wanan maganin nace tare da nuno min maganin a hannu shi dan kuturun yazo min nima a lokacin ban bashi amsa ba kawai na fice a dakin ba tare dana kara juyowa gare shi ba.
Daki na koma na haye gado na dunkule a wuri daya take wani irin kuka yazo min a lokaci daya mummy ne ta shigo dakin don taga fitowana daga dakin shi ita da Nura suna magana a falo.
Hajiya lafiya may ke faruwa ko jikin naki ne ya matsa maki haka take tambayana a jere lokaci daya sai kuka nake ban iya magana ba.
Banko kofar dakin da yayi da karfi shiya dakatar da mommy dake tsaye a kaina tana jera min tambayoyin ta a lokacin.
Ganin mommy bai hanashi fadin abin da yazo fada min ba yace ni zaki mayar mutumin banza ina magana ki wani fitowa ki barni yau sai kin fada min wanda ya baki maganin nan ko ki fice ki bar min gida na don ba zan zauna da macen da zata haince ni ba.
Da sauri mommy tace subbahanallahi Alhaji mai yayi zafi haka tsakanin ku har kake fadin wanan maganan haka ?
Kallon mommy yayi cikin bacin rai kamar zai mata magana kuma ya fasa nasan zuciya ce ta kawo mashi maiyi a banza balle yau ga dalili.
Ya juya gareni yace ke har kin isa baki san halina bane wallahi da bakiyi min hakan ba ban cutan na tare da ni shi kuma Allah bai yarda ya cuce ni.
Don Allah Alhaji kayi hakkuri ku bi abin sannu niko ina saman gado na dunkule sai kuka nake yi ya juya wirin mommy yana fadin mummy ashe duk ciwon da yarinyar nan keyi ita taja wa kan ta.
Da sauri mommy ta mayar da han kalin ta gare shi tace ita taja wankanta garin yaya haka ya faru kuma hajiya ?.
Gata nan shi nake tambayan ta tana son raina min wayau yanzu bayan Allah ya tona mata asiri wai mummy kin san zubar da ciki take kokarin yi yanzu na kamata.
Innalillahi safiya baki da hankali ne may yayi zafi haka cikin da kowa ke farin ciki da samun shi zaki ce kuma zaki fitar haba haka baiyi kyau ba wallahi.
Ni dai kukana nake ban saurare su ba don Allah Alhaji kayi hakkuri tunda ta gane kuren ta ai mata afuwan kurciyane ya kai ta ga hakan da batayi ba idan ta sani.
Kurciya ina kurciyan yake anan tunda har tasan ta zubar da ciki ta cuce ni ga abinda nake so don tana munafuka wawiya.
Zagin yayi min yawa uncle na iya furtawa da karfi a cikin kuka ya watsa min harara yana fadin ok har ma kina da bakin magana zagi yayi maki yawa ko ?
Alhaji kayi hakkuri don Allah ka bar zancen nan haka na tunda ta gane kuren ta yace sai fa ta fada min a inda ta samo wanan maganin zan barta mommy yace.
Zuwan yaya Saadu da ya kira ne ya katse shi ya fita falo wirin shi ya samay shi nan yake fada mashi abinda ke faruwa a tsakanin cikin bacin rai.
Mommy ce ta fito dakina a lokacin goye da Abba bayan ta da yake barci ta karaso inda suke tana gaisawa da yaya Saadu daya shigo.
Yaya saadu yace mummy abinda safiya take shirin yi ke nan ashe shiya tare da fadin ina mommy zata san mugun nufita tunda batason kowa ya sani nima Allah ne ya nuna min tun batayi min sawalwalin cikin ba.
Ka fada mata idan bata fada min wanda ya bata wanan maganin ba sai ta barmin gida na yau don ban zama da mace da bata sona da karuwa .
Yi hakkuri yallabai ina Safiyan take yana tambayan mommy tace tana nan dakin ta yace mommy ai min magana da ita don Allah.
Nan mommy ta juya ta shiga wurin ta fada min ga yaya Saadu yana magana dani azuciyar ta kuma sai addua take Allah dai yasa ba samira bace don rawan kan samira na da yawa.
Sai can na fito saye da hijjabin sallah na har kasa ina yiwa yaya saadu sannu da zuwa cikin miryan na da ya dishe saboda kuka da ciwo da fargaba.
Ina zama Uncle yana bina da harara yaya saadu ne yace safiya yaya haka kuma ya faru cikin lalama yake min magana wanda shi uncle din bai so haka ba a gare shi so yayi ya balbala ni da bala,i a lokacin.
Sai kuma yaji yana min magana may kama da lalashi yace may ya kawo haka safiya haihuwan ne baki so ko tsoro kike ji ne ?
Haushine ya kama uncle yace kaga malam ba lalashinta na kiraka kayi ba ta fada muna inda ta samo maganin nan in ba haka ba bata zama min gida.
Na dago cikin zafin rai nace samay idan na bar maka gidan ina dai da gidan ubana ko sai kuma idan ginan da kai muna zaka sa a rushe ka mayar muna da namu.
Tashi yayi kamar kububuwa yayo kaina yaya saadu ya tare shi yana fadin bari mubi a hankali yallabai abin bai kai haka ai zata fadi nasan halin safiya.
Yace amma kana jin har ta samu bakin fada min bakar magana ko da mamaki yake kallona ni kuma cikin zafin rai da hasala nace.
Dole in fada maka kana ta magana in bar maka gida, gida kan tunda ba anan aka haife ni ba ai nasan ba gidan ubana bane sai in bari din sai may.
Safiya ashe haka kike inji yaya saadu nace yaya abin yayi min yawa ne wallahi daga magana sai ya wanke ni da mari kawai.
Mari kinyi laife mai muni ne safiya dole ya mare ki ko nine abinda zanyi sai yafi wanan da yayi maki ai don may ba zaki tsaya kuyi magana ta fahinta ba kin tsaya garda yace ki fada mashi inda kika samo magani kin tsaya kina ja.
Wai may ma zai sa ki zubar da cikin ne safiya may cikin ya tare maki da kike son zubarwa ne da baki iya hakkuri ki haife shi.
Yaya maganin nan ya dade a cikin jakkata wallahi ba yanzu na saye shi ba da yake nufi ni kuma ba wanda ya bani dama na san shi tuntuni sai na sayo da nake ganin kamar ciki ke gare ni a baya.
Ba yanzun na saye shi ba yaya karya take wallahi yanzu ta sayo shi take sha don cikin ya bare to bari kiji ni ba dan rayuwa kawai na kawo ki gidana ba.
Don raya sunnan ma,aiki na kawo ki mu hayayafa mu cika sunna mai karfi ba a haihuwa ke aka haife ki yana fadi kamar zai buge yaya saadu ya rufe da duka.
Ranan iyakan bacin ranshi na gani a gidan ni kuma naki fadin inda na samu maganin na tsaya kai da fata maganin ya dade min a cikin jakkana kuma ba wanda ya bani maganin saye kawai nayi don na san shi.
Naki fadi ne don kada naja wa matar mutane jiddali daga taimako nasan kuma idan na fadi gaskiya abin zai iya shafan samira duk da bata da laifi aciki amma muna tare aka bani.
Har magariba ya gwauta muna wurin zaune yaya Saadu da mommy sai bashi hakuri suke yi suna fadin nayi kuskure sosai na bashi hakkuri.
Nace ni ban sha ba koda yake fadin nasha ban sha maganin ba aida cikin ya fita inda nasha din yace cikin dai yafi karfin ki ne yaki fita.
Nace ban dai so zubar dashi ba da babu abinda zai hana na zubar din yace yaya Saadu kana dai jin abinda take fadi.
Tayi laifi ban isa ta bani hakkuri akan abinda tayi min din nace ni ban san nayi laifi ba tunda ban sha komai ba.
Yaya Saadu ya tursasa akan in bashi hakkuri a gaban nace nayi kuskure ka yafe min daki ya wuce zuciyar shi nayi mai kuna sai tuna maganan hajiya baaba yake yi da tace mai ya rage matsamin don zan iya bijere mai daga baya.
Yanzu ko gashi ya ga na fara din wai safiya ce yake fadi take fadi har tana ikirarin na rushe gidan da nayiwa mahaifanta na mayar masu da kangon su.
Kwafa yayi yace dani kike wasa yarinya zan nuna maki kuren ki a gidan nan zaki san kin taba ni don sai kin gane kuren ki.
Yana alwala yana maganan zuci a falo kuma yaya saadune yayi min fada sosai akan yadda nayi ban kyauta ba nayi laifi kawai in bashi hakkuri.
Nace yaya kanaji fa yana fadin ban kwana mashi gida yau akan maganan ga zai ta fadin haka in ba dama ya gaji dani bane yana son mafita akaina.
A daidai lokaxin ya fito daga dakin shi ya kallemu kamar harara yana fadin Saadu muje muyi sallah rabu da ita mommy jekiyi sallah lokaci ya kure ko.
Yaya Saadu ya kalleni yana mikewa yace safiya yaushe kika kuma haka ne wai duk kin bi kin tada hankalin mutane a lokaci daya haka.
Don Allah ki kara bashi hakkuri idan na wuce don ba lalai ne in dawo tanan ba yayiwa mommy saida safe ya fice daga gidan, itama mommy tashi tayi zuwa sallah inda na dan dade zaune ina tuna irin karfin halin dana rufe idona nayi masu.
Mikewa nayi zuwa sallah nima ban fito don ishai yayi nan na zauna abina sai su hindatu ne suka shigo dakin suna min hira wanda ba fahintar su ma nakeyi ba.
Fitar maimu sai gata ta dawo tana fada min anty baban Abba ya dawo yana falo zaune nace ku tafi ku gaida shi yau banjin dadin jikinane.
Yaran suka fita zuwa wurin su suna gaida shi da dawowa ya amsa masu fuska a sake kamar yadda ya saba yi dasu kullun.
Nan suka dan zauna suna mashi hira suke fada mai antyn mu tace yau jikin ta yana damun ta bata iya fitowa Allah ya sauwaka yace ai na bata magani dazun.
Mommy ce ta kirasu suka shige ciki wurin ta ya gama abinda yake yi ya shige dakin shi batare da ko waigowa kofana ba.
Nima nasan da hakan shiyasa nayi zama na a daki ban fita don yasan nima ina jan zancen na gama har na kwanta a lokacin naja bargo na rufe kaina a ciki.
Da safe Samira ne tazo gidan dubani da kuma tambayana yadda akayi haka ya faru har na bari uncle yaga inda na aje maganin.
Nace kedai bari Samira baban Abba yakai dan halas wai mutumin da bai taba, taba min jakka ba shine wai da yake Allah yayi asirina zai tono sai gashi yaje daukan maganin da muka karbo asibiti a cikin jakka ta.
Na manta shaf wallahi da wanan maganin ai da na yunkura na tashi komai ciwon da nake ji na rufawa kaina asiri.
Tace ke dai bari aini da yayan ki ya fara min maganan baki ga yadda na tsure ba ina gudun suna na yafito a maganan tawa ta samay ni, in shiga uku gashi muna alkunya da mutum da ina zan saka kaina.
Dariya nayi mata nace ni zan fara ne in fadi gaskiya da fa har gidan matan nan yana iya zuwa yai mata cin mutum ci shiyasa na kafe dacewa dama nasan maganin na dade da sayan shi.
Zai kuma iya hani zuwa gyaran jiki shiyasa nayi mai borin kunya na labe ga zancen gida don yabar maganan.
Kuma nasan abinda yasa yayi sanyi ke nan a yadda ya dauki niyar ci mun mutunci ido rufe tace kai safiya sai kika lauye bawan Allah da jijiyoyin shi.
Nace ke kuwa kin san yadda uncle ya hau har fa maru biyu ya bani masu kyau rabona da duka tun gidan yaya Ahmed fa samira.
Tace ni banga dalilin ki sin zubar da cikin nan ba safiya baki rasa ci ba baki rasa shaba a gidan nan wanda zai gina maki jiki.
Don may zaki nace sai kin halaka dan cikin ki kika sani ko gwauna ko shugaban kasa kika samo muna zakiyi muna sawalwalin tsiya haka.
Nace samira ai yanzu na yi nadama sosai yadda naga uncle ya kwalafa rai ga haihuwan nan haka yasa jikina yayi sanyi wallahi.
Tace yanzu dubara ya saura gare ki ai sai ki san yadda zaki bashi hakkuri ya sauko maki don nasan yanzu ya hau sosai dake a gidan nan.
Nace ya hau kan zan jira sai ya sauka don yanzu yi mashi magana wani jidalin zan kara jawowa kaina barshi mu tafi haka har ya sauko da kan shi dai.
Tace kina ganin haka zaifi safiya nace ni na san halin uncle Samira barshi dai muje a hakan tace to shike nan ai mai daki shiyasan inda ruwa ke yoyo.
Tace sai da na fada maki tun farko safiya kada ki yunkurin zubar da cikin nan don dan halas sai an haife shi tunda an samu.
Wasa wasa mun share wurin sati biyu yanzun ba mai kula wani sai dai zan mai ina kwana ya amsa min a dake ba sakin fuska ko kadan.
Tun ina dari dari har abin yazo ya daina damuna tunda ban rasa ci da sha ba ba kuma korana yayi a gidan shi ba.
Sai dai wani lokaci abin yakan damay ni amma yaya zanyi tunda yaki tsayawa mu fahinci juna har in bashi hakuri ga kuskure na.
Allah ya gani tsoro nake ji don abin da ya samu kawata shine ya tsaya min a raina sosai saboda irin haka tayi tasha da kyat.