BAHAGON RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

YAR UWA BA SAI KIN RUBUTA BATSA BA NOVEL DIN KI ZAI SAMU KARBUWA, KE MAI GYARA TARBIYAR AL, UMMA CE BA MAI BATA WA BA.
KIN SAN YARA NAWA NOVEL DIN KI YA HALAKA DA WA YAN DA KIKA SAKA ZINA TA SANADIN NOVEL DIN KI NA BATSA.
KI WA KANKI FADA TUN LOKACI BAI DAINA YI DAKE BA ABIN KWARAI AKE YAYI BA NA BANZA BA, , , , , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
9/21/20, 10:00 AM – Ummi Tandama: BAHAGGON RARYUWA, , , , , , , , , ,
????????8️⃣6️⃣????
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Yau ya kama jumma, a tunda safe ina shirya yan kanne da zasu makaranta don dole duk safe koni ko mummy daya ya tsaya wurin su don su shirya.
Idan ba haka sai su tsaya shiririta da gardaman banza har su makara don yanzu sun rage zagwadi son makarantar da sukeyi .
Tunda sukaji baba ya yarda da zaman su a guri don da farko kin yarda yayi lokacin da hutun su ya kare yaji shiru sai gashi ya bugo min waya wai baiga yaran shi ba.
Nace baba yaran ka suna nan lafiya makaranta ne ya boye su yace wani irin makaranta kuma nace ai mun saka su school a nan din dana boko dana muhamdiya.
Yace bam yarda da wanan tsari ba don ba haka mukayi dake ba nace baba na sani amma kayi hakkuri da hakan da nayi.
Fada yayi sosai a wayan ina sauraren shi saida ya gama nace baba nasan munyi kuskuren yin haka da mukayi.
Amma ba nayi bane don mu raina maka nayi ne don taimaka wa rayuwan mu baki daya saboda indan suna nan zasu samu karatu mai inganci da ci gaban rayuwa.
Kayi hakkuri baba don Allah kabar min su anan don zama su a nan din yana da matukar muhinman sosai yace.
Safiya ai wanan rashin hankalin ne ki dauki yara har biyu ki kai wa mutum gida wanan ya zama rashin hankali ai.
Baba shi ya yarda da zaman su don shi da kan sa ya kaisu makaranta mai tsada ta kudo anan din munyi kuskure ba zamu kara ba in Allah ya yarda.
Bayan ya gama saurare na ya kasha wayan ya nufi wurin su ummi da fada mama ya fara kira sai ummi suka fito yake fadin.
Ashe kun hada kai da yarinyar nan safiya ne ta yaudareni ta kwashe yaran nan, ta tafi dasu su zauna a wurin ta ne ?
Haba malam ai wanan abin kamar taimokan ne tayi inji mama ta katse shi ga maganan shi yace ke dakata min.
Taimakon may nace na gaza da “ya”ya ne ita a ina ta taso in ba nan din ba ummi tace amma ni wanan abin sai naga kamar taimakon kane yarinyar nan tayi banga abin fada ba don safiya ta dauki kannen ta ta kaisu gare ta.
Mijin ta baiyi fadan haka na sai kaine zakiyi haka dakan shi ya bata baki kan hakan yace ke nan da sanin ku aka yaudare ni ?
Yaudara kuma malam babu yau dara acikin hakan wata rana hakan zai maka dadi yaya Nura ne yashigo gida a lokacin yake tambayan may ke faruwa.
Ummi ke fada mai yace baba koni safiya zata dauka yanzu ai zuwa zanyi da gudu balle maimu da hindatu yara nacen cikin daulan duniya za ai masu bakin ciki kuma.
Kaifa mahaukacine sakaran banza kawai waye zai masu bakin ciki din niko uwar ka ya wuce yana a bakin ciki za ai masu mana mai kaya ya daure sai mai cira ke wassh Allah.
Uwarka nace ya nufe shi gadan gadan shiko ya fice gidan yana dariya wanan abin yasa su ummi saurin watse wa gaban shi yaci fadan shi yana fadin ai zai gamu dani ne.
Murmushi nayi da tuna wanan magana da ummi ta fada min ya faru a gidan mu sauri muke mu tafi sai Abba ya kama kuka ina jin mommy tana lalashin shi yaki shiru.
Uncle ne ya leko daga dakin shi yana fadin wai may yaron nan yake ma kuka haka ne ke kuma baki dubashi ba ?
Bai mai magana ba sai wucewa da nayi dakin kawai na samu mommy tana lalashin shi yaki shiru daukan shi nayi ina lalashi bai yi shiru ba.
Mummy ta tara hannun yaki zuwa wurin ta dole sai na goya shi don yayi shiru saboda mommy ta saba mai da goyo yau kuma bata jin dadin jikin ta ne.
Ya fito daukan ruwa ya samu su maimu zaune falo suna jirana yake fadin baku tafi bane har bakwai da minti goma yanzu suka ce anty muke jira ta fito Abba ne ke kuka yaki yin shiru.
Sai gani na fito dakin mommy da goyon shi da goran ruwa a hannun shi ya dago yana kallona goye da yaron a bayana.
May ya samay shine yau ya fadi yana kallo na cikin dakewa nace fitane kawai yake ji mommy bata jin dadi tun jiya miko min shi nan yace dani ina kokarin sance yaron a baya ma in mika mashi sai yaton yaki ya kara lafewa.
Ke mi ko min shi yace goyon nan zai iya maki illar koda dama ba son cikin kikeyi ba nace yake zaune a jikina idan ban so ka barshi kawai mutafi in kaisu in dawo.
Barshi in kaisu naji yace tare da fadin ku tashi kada ku makara sosai yaran suka mike sai maimu ke fadin anty kudin exam din fa uncle zai bada ?
Nace ku bari monday zanje in biya maku idan na kaiku yake cewa nawane kudin suka ce five hundred kowan mu fita yayi baiyi magana ba ya wuce suna biye dashi a baya.
Nan suka fice na sauke ajiyan zuciya yaushe rabon da yayi min magana haka sai yau sanadin Abba dake kuka a gidan ya jawo yayi min magana.
Da motana ya fita dasu bai jima ba ya dawo ina zaune goye da Abba a bayana ya shigo wurin mu yayo direct yana fadin .
Babana may ya hadaka da mommy yau kake fushi haka ban san ka da fushi na fa ya dan duka yana yiwa yaron wasa sai kuma yace.
Kin bashi abinci yaci ko yunwa yake ji kai na girgiza mai yace ki bashi a gani ko yunwa yake ji don yanzu dai madara ba isan shi zaiyi ba.
Mikewa nayi zuwa inda Nura tafara jera abincin na dibo mashi dankali kadan na dawo ina sance yaron sai ya karbe shi a bayana shi da kan shi yake bashi abincin yaron yana karba.
Yace don Allah ku bar barin shi da yunwa haka yaya madara kawai zai ishi yaro dan wata tara yanzu nace ya dai so cin abincin ne yanzu amma in an bashi sai yaga dama yake ci.
To na dai ce a dinga bashi in baici a barshi daga yau naji nace dashi ya gama sai kuma yace sai in kara goya shi yasa muna fitina a wurin yana jawo zanin da na sance goyon shi a bayana.
Wuf uncle ya dauki yaron yayi ciki dashi murmushi nayi bayan sun shige daki da yaron wanda nasan ya fara saukowa ne da kanshi da ina binshi ina bashi hakkuri da yanzu bai isa saukowa ba haka.
Ya fito cikin shirin fita yake cewa Abba na nace daki yana barci ki lakashi don kada ya tashi yana kuka ya fado ya fada ba wani sakin fuska gare shi.
Fita yayi daga gidan mukai mai a dawo lafiya bayan awa daya ne naje dakin leka yadon yana kwance yana barci abinshi hankali kwance har lokacin nan nabi dakin da kallo yayi kaca kaca sai na fara gyara bathroom na fito na gyara ko ina na goge na sa mai room fresh yaron ya tashi kafin in gama.
Na sauke shi na canza mai zanin gadon na jawo mai kofa sha biyu daidai na fito zuwa dauko su maimu ni da Abba ne muka fita na dauko su tare motan mu ya kunno kai kwanan gidan.
Bayan mun shiga ciki na rufe mota bai fito ba har na shiga gida sai can gashi ya shigo muna falo zaune muna cin marasa gasas da muka sayo a hanya hajiya tana hanya zata shigo yace dani.
Ras naji gabana ya fadi ban san lokacin da nace mai hajiya baaba ba yace ita yana wuce wa dakin shi bai tsaya falon ba nasan shirin jumma,a yadawo yayi lokacin.
Yana shiga idon shine ya sauka a dakin dana gyara mai shi tson ya sauke ajiyan zuciya ya aje waya ya nufi ban daki nan ma a gyare yake komai sai walkiya yakeyi a wurin yasha gyara.
Murmushi ya sauke a fuskan shi shi kadai a dakin yace mata halin su sai su watau tunda yau nayi mata magana shiyasa ta shigo tayi min gyara itama ta iya ke nan yanzu.
Daren jiya kamar ummi ta sani tasa ni gaba a waya tayi min tas sai da nayi kuka sosai tace lalai lalai in bashi hakuri don nice ban da gaskiya ko ina akaje kuwa da maganan mu.
Kuma akan may zance wai ya rushe gida ya mayar muna da namu yaushe na koyi rashin kuya haka ko nice nasa ya gina muna gidan.
Idan banyi hankali ba zata hadani da mahaifin mu kuma zata kira uncle ta bashi hakkuri da sauri nace ni ummi ba sai kin kirashi ba ni zan bashi hakkuri da kaina.
Sai washe gari kuma na tashi naga ya rigani ma saukowa ko shima mahaifiyar shine tayi mai magana oho ?
Yanzun kuma da yace zata shigo sai tunane na ya kai ga ko tasan da matsalan ne zata zo inko har uncle ya fada ma hajiya yabar ni cikin tsunbul.
Fitowa yayi cikin farin voil na maza wanda har zaka iya hango farar singlet din shi na shiki yana haskawa a inda ya bar mu ya samay zaune har lokacin muna wurin.
Ke maimu ku shiya kafin in gama mu je masallaci ku shirya Abba yace dasu ya nufi hanya waje dama yakan je da yaran idan ya bushi iska amma ya dade bai tafi dasu ba sai yau.
Namike na nufi dakin mommy nace ta ban kayan shi zasu je masallaci ne da baban shi nan na zauna dakin ta na shirya yaro tsab anan kuma nake fada mata yau sarakuwa na zata zo.
Tayi murna da jin haka sai dai tace dani zato za ta samay ki cikin wanan zaman doya da manja da kukeyi a tsakanin ku haka ?
Ni mommy yaya zanyi tunda in ya hau bai sauka sai yaga dama don kan shi tace ke ko keda yadda zakiyi don ke ce mace safiya nasha fada maki kada ki fushi haka dashi tunda ke ce baki da gaskiya.
Babu namijin da zai kama mace da wanan laifin ya iya kyale ta ni naga hakkurin shi kwarai da gaske wallahi.
Mommy har yanzu fa fushi yake yi dani kan maganan kuma sai kice kinga hakurin shi mommy ?
Tace kin san girman laifin da kika aikata kuwa yar nan ai sai baka son namijine kake gudun haihuwa dashi nace shima yasan ai bada wata manufa nayi ba mommy kawai dai lafiya na nake jawa .
Amma ni ba wai don ban son haihuwa dashi bane kawai dai haka Allah ya nufa sai ya faru a tsakanin mu yaki yarda ya saurari manufata kuma.
Maza fa a sannu ake binsu diyar nan don Allah ya riga ya basu girma a kan mu ki lalaba mijin ki ku zauna lafiya yadda kuke yafi.
Hindatune ta shigo daukan Abba a lokacin ban koma daki ba na nufi kitchen don shirya ma hajiya abinci sai dai ban san ko su nawa zasu zo ba kuma.
Kafin su dawo nayi nisa ga aiki sosai don da Nura muke aikin abinci nagama abinda zanyi na fito kara gyara gidan su maimu na taya ni.
Mun hada komai zuwa hudu hudu da rabi suka iso gidan yafita a lokacin dakin da aka gyara masu na kaisu ita da anty suwaiba sai yan matan ta biyu da tazo dasu.
Mun gaisa na tambaye su sauran yan uwa suka ce duk suna lafiya abinci na gabatar masu sai da sukai sallah suka zauna ci .
Ban koma wurin su ba na barsu su dan huta don sun kwaso hanya mai nisa dakina na koma na dan kwanta kadan don na gaji a lokacin.
Cikin yan matan da suka zo da su ne daya tazo ta kirani.
Na samu har sunci abinci ko na shigo dakin dayar yarinyar naa kwashe kayan abincin daga dakin tana kaiwa kitchen baaba yaya gajiyan hanya nace bayan na kai zaune kasa gefen gadon.
Garin nan naku akwai nisa yar nan shiyasa ban sa kaina zuwa ba tun farko ko yanzu don naji ance kinyi fama da jikine har kin kwanta asibiti koda yake ke da ke da mijin nake ba fadar ciwo kukeyi ba.
Ko sannu akace maku ai an rage maku ciwo a daidai lokacin uncle ya shigo dakin yana fadin sannu ku da zuwa naje dan nesa shiyasa ban shigo da wuri ba.
Bata fasa maganan da takeyi tace idan shi bai fada min ba aike kya gaya min tunda muna waya kusan ko yaushe dake.
Zaune yakai kasa shima don mika gaisuwa ga mahaifiyar ta shi cikin girmamawa ta amsa mashi tana ci gaba dayi muna fadan rashin fada mata matsalar mu da baya yi.
Yace aiyi hakkuri baaba ai ta dade da samun sauki dama ba wani matsala bane sosai ke damun ta a raina nace ka fadi hakan mana tunda cikin ba ajikin ka yake ba ai.
Allah ya sauwaka tace muka amsa da amin tace Safiya kije ku bude tsaraban nan kada su lalace a saka a fridge nace baaba har da dawainiya aka zo muna kuma ?
Kin jiki da magana ina dawainiyar yake anan ni mai gida na nayowa tsaraba dama ba ku ba yar uwar ku dai ta kawo maku tsaraba.
Ina mikewa nake fadin baaba ba a zo da maryam na dai tace maryam din nan tana fama da laulauyin ciki bata iya zuwa ai taso ta biyo mu hakana hanata nayi.
Nace Allah sarki ashe zamu sha suna idan rai ya kai mu lafiya tace a toh zaku sha kan don wanan cikin ma ya zo mata da matsala sosai wallahi ba kamar wanda take a baya ba.
Yace dama ai haka ciki yake ko wani da kalar tashi zuwan fita nayi daga dakin na nufi inda kayansu yake yan matan na zaune falo da su maimu suna hira.
Da dare na shirya bayan na idar da sallah na shiga dakin nasu suna ciki dukan su muka gaisa na samu wuri na zauna muna fita da anty suwaiba hajiya na lazimi saman carpet din sallah har lokacin.
Ya shigo cikin jallabiya baka sai kamshin turare yake yi yace ke kije ki kama yaron nan haka na yau mommy bata jin dadin jikin ta.
Mikewa nayi na bar dakin ba tare da nayi mashi magana ba zuwa kama Abba din dake ta kuka a dakin mummy baaba ne ta shafa ta juyo gare shi tana fadin kullun ina fada maka kabi yarinyar nan a sannu.
Ji yadda kake faman daure mata fuska babu walwala a tare da ita duk tabi ta fige ta koma wata iri jikina yayi da bayan shi a bango yana fadin ni bani na fige ta ba baba halinta ne ya fige ta.
Dan kallon shi tayi kamar harara tana fadin wani hali ke ga wanan yarinyar banda kai dake son takura mata a kullun hakan da kake wallahi tun tana tsoron ka na fada ma zata zo ta daina ne.
Wani matsi ai bai da kyau wallahi idan yayi yawa ya danbala mutum ko ya hinjira shi murmushi yayi yace yanzu kuma wani matsi nake mata.
Yarinyar da take gani ban isa da ita ina fadi tana fadi tace ba zan taba yarda da wanan magana duk da karya ba haki ka bane a baya.
Hajiya yanzun haka ciki ke gare ta na kamata tana yunkurin zubar wa nayi magana tason tayi min rashin kunya kuma.
Kira min ita suwaiba tace anty suwaiba ta tashi zuwa kira na muna kitchen muna hira a can ta samay ni .
A daki kuma ce mata yake hajiya ban san may take nufi da yunkuri zubar min ciki da take yi ba ka zauna kunyi magana ta fahinta da ita ka saurare korafin da yayin hakan da tayi niya ?
Lokacin na shigo dakin nuna min wuri tayi alaman in zauna nakai zaune jiki a sanyaye sai da taja dan lokaci tace min.
Safiya yanzu mijinki ke fada min wani magana da banji dadin jin shi ba sam na dukar da kaina kasa sai haaaye tace Safiya may zai sa kiyi yunkurin zubar da cikin jikin ki kuma ?
Har kin sa zargi ya shiga tsakanin ki da mijin ki yana zaton kin yi haka ne don baki son shi ko baki son haihuwa dashi ?
Da kyat na dago kaina ga nauyi ga kunya dake cina nace ba hakana bane baba yaki ya fahinci manufata ne a hankali na kora mata bayani na da dalilin daya sa nake yinkurin cire cikin da farko.
Tace banda abinki ai komai na Allah ne Allah daya baki shine kuma zai raba ki dashi lafiya ai kowa da irin tashi kaddaran rayuwa.
Sai kiga ke kin haife komai ba zai samu ba cikin hukuncin Allah wani kuma sai yasha bakar wahala haka abin yake ga Allah.
Kinyi kuskure babba don kisan kai kika so kiyi ba don Allah ya gyara kin fahinta daga baya ba kiba mijin ki hakkuri ban son irin yadda na samay ku din nan sam.
Ana maku kallon sha,awa daga waje a ciki kuma baku da jittuwa tsakanin ku abin bai yi kyau ba wallahi kuna zaton wani bai san halin da kuke ciki ba to kirana akayi aka fada min abinda kuke ciki a gidan.
Da sauri kowan mu ya kalle ta da mamaki tace eh ba dole bane in fada maku wanda ya kira amma dole tasani tasowa in zo don in tsawa ta maku.
Dan shiru ne ya biyo dakin cikin sanyi murya nace uncle nayi kuskure ka yafe min don Allah babu komai yace a takaice.