KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVEL

KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVEL BY M SHAKUR

Wuraren 1 suka kai Abuja, tadata yayi ta hanyar kiran sunanta. “Du’a, Du’a” bude idanunta tayi kadan, hararanta yayi yace “duk uban baccin dakikayi jiya bai isheki ba yarinya saison bacci” tashi tayi yace “gyara kujeran” gyara kujeran tayi yataso sanan takalli hanya yace “kinga yanda Abuja keda kyau kalli titi ba irin na Kanon Kuba” murmushi tayi tace “mun kuwa kaiwa gidan” gyadamata kai yayi yace “takirani yafi sau uku duk kina bacci” shiru tayi tana kallon ko’ina kaman zata hadiye garin da idanunta saiwani irin sanyi da shauki takeji har sukakai wani estate mai suna Presidential Estate. zaro ido tayi tana kara kallon ko’ina ganin gidaje masu suna gidaje ba muna gidaje ba, tasha ji idan su Mum na gulman su tana yawan cewa ai Abba sabida ya rainata yar gidan masu kudi yaje ya auro mata, itama yarinyar kaman mayya itace kawai ta auri talaka mahaifiyarta tabarta ne sabida ita kadaice yarta mace, ita bazata iya tuna gidan dasuke zuwa a dan memory dinta na Grandma sonta lokacin tana yarinya akazo kuma aka dena zuwa da ita saidai su Aneela da Muhammad da Mudasir.

Shiga Estate din yayi yana tafiya ahankali ganin yanda Du’a is enjoying the view din, agaban wani lafiyayyen gida Hamad yay horn, wani security yafito ganin Hamad yasa yace “barka da zuwa yallabai Hajiya ta sanar dani zuwanka” gyadamai mai kai Hamad yayi yana murmushi shikuma yakoma ciki yabude musu Gate din, Jan motar ciki yayi Du’a ta kwalalo idanu tace “nan ne gidan Grandma Ya Hamad” murmushi kawai yamata yana karasa parking motansu acikin jerin motocin dakenan gidan wanda babu mate din seinna su, bude motan yayi yafito sanan yamata alamu data fito gyadamai kai tayi daidai security yagama kulle gate yazo yace “akwai akwati ne Yallabai” “oh yeah” Hamad yafadi yana budemai booth daidai lokacin Du’a takaraso wajen tsayawa chak security yayi yana kallonta ganin haka yasa Hamad yace “ga akwatin” dasauri yajuyo yakalli Hamad hannu yasa yadauki akwatin yawuce Hamad kuma yarufe booth din yajuyo daidai lokacin wata hadaddiyar mata wacce kana ganinta kasan ba yarinya bace dan ta ijiye jikoki tafito, tana sanye da bubun atampa ajikinta gatanan black beauty da akalla zatakai 70.

“oyoyo oyoyo, su maigida an iso” jin muryanta yasa dasauri Hamad yajuya washe baki yayi yace “Hajiya wanan kwalliya haka, bazaki barma yara ba” dakuwa tamai tace “kaci gidanku, yanzu dani dasu idan akaje gasan kyau basai akwasheni sau dari baza’a kwashe suba” karasawa yayi har inda take sanan cikeda girmamawa yadan runtsuna yace “ina yini Hajiya” hannu tasa tashafa kanshi tace “kasha hanya Soja na maigida, jekai wanka kahuta kaida komawa kano sai gobe” tai maganan tana kallon Du’a dake bayan Hamad kanta akasa tana wasa da hijabinta kunya yahanata dago kai. “Du’a” matar takirata ahankali, ahankali Du’a kaman wacce ke tsoro tadago kanta takalli kakanta fess tagane ta danga kamanninta da Mami nan, black beauty abinta yar gayu, ganin takasa magana yasa dasauri tabude mata hannu tace “zonan zoki rungumeni, taho taho” ahankali Du’a taje dasauri tashige jikinta takankameta kankameta Hajiya tayi tace “Alhamdulillah Alhamdulillah, Du’a sannu, sannu kinji, akwai abinda ke miki ciwo”?girgizamai kakan nata kai tayi, dagota Hajiya tayi tasa hannu tai cupping face nata tana kallonta kaman yanda Du’a me kallonta ahankali rasama mezatama yarinyar tayi hakan yasa ta manna mata kiss a goshi sanan takama hannunta tarike tace “muje nakaiki dakinki kiyi wanka”

Ciki tashiga da Du’a falon wani irin hadadden gaske gashinan Duplex sai yan aiki guda biyu dataga suna gyara dinning suna ganin Du’a duk suka bitada kallo suna gaidata. “welcome Du’a” murmushi Hajiya tayi tace “kingan su suke tayani aikace aikacen gida, wanan sunanta Shema’u, dayan kuma sunanta Razika, duk sun sanki, jeki musu sallama” gabansu taje ahankali sai kallonta suke kaman basu taba ganin mutum ba, hannu tamika musu cikin muryanta mai dadi tace “Assalamu Alaykum, nice to meet you” dasauri suka karbi hannunta suna murmushi Razika tace “you are so beautiful” tsayawa tayi turus tana kallonsu Hajiya dake kallonsu tace “tell them thank u sunce kinada kyau” ahankali tace “thank u” sakinta sukayi itakuma Hajiya tasauke ijiyan zuciya sanan tace “taho mutafi” dasauri tajuyo kaman jira take dama stairs sukayi sukai sama saitaga ashema kasan baida kyau wani daki tabude dakin mai kyau sosai saiga hoton ta datana yarinya tana rarrafe kusada Hajiyan dasauri tashiga dakin tana kallon hoton, murmushi Hajiya tayi tace “lokacin kina yar tatsitsiya keda Mamanki kunzl ganin gida, little Du’a, jeki yi wanka kizo kici abinci zan baki labarin anjima” gyadamata kai tayi sanan tacire hijabi ahankali tawuce zuwa kofan datagani wanda ta tabbata bathroom ne saida tashiga sanan Hajiya tafita daga dakin.

Saida tayi wanka sanan tafito daure da towel,
akwatin ta dataga anshigo dashi tabude tadauki wata doguwan riga wanda yawanci kayanta dogayen riguna ne daidaikune riga da skirt, saka rigan tayi sky blue ce mai kyau sanan tasaka hijabi salla tayi sanan tazauna tana tunanin maganan Hajiya datace tasauko, tashi tayi ahankali tacire hijabinta ta ijiye sanan tabude kofa tafito, ahankali take sauka daga stairs tana karabin gidan da kallo, daga sama sama takejin maganan Hajiya da Hamad saikuma takarasa suna ganinta sukai shiru. “kin idar tahonan” tauna mata kusada ita akan dinning hakan yasa ta taho zama tayi wajen Hajiya tace “debi abincin ki kici” dasauri Hamad yace “kafin namanta banfada mikiba kuran nama tazo gidan nan ba” turo baki tayi Hajiya ta harareshi tace “karkaga kana maigida kanemi samin jika kuka sama zamu hau nidakai, ci abinci ki kinji kome kikeso” gyadama Hajiya kai tayi sanan tadebi rice da stew da plantain da fish tanaci, bini bini Hajiya ke kallonta hartaci rabin abincin sanan tasha ruwa haka

???? KYAWUNA JARABTA TA ????

       ✍️M SHAKUR 

EPISODE 1️⃣3️⃣
Har dare hira suke Hajiya da Hamad, kagansu zaka dauka Hamad jikan ta ne, Hajiya wata irin mace da idan kana tareda ita you have no reason or what so ever to hate her ne, kodan sabida yaranta biyu kachal aduniya saisa takeda son mutane haka oho, danta na farko yaranshi uku dukansu Maza kuma kanana dan Mami tariga shi aure yana UK achan yake aiki sai Mami dakeda yara hudu tana aure a kano, Bayan Mami ta haifi wata tarasu, Hajiya is very very educated, lawyer ce babban gaske amman yanzu tai retire saidai she’s still an advocate na Human right, batun yauba taso tadauki Du’a, akwai lokacin data kusan kulle Maman Abba wato Kaka, sabida kukan da Mami tamata ne tana rokonta yasa tahakura daga lokacin tai fushi da Mami ta shareta, saisa koda wasa bata taba taka kafarta agidan Abba ba dan batada daukan nonsense and zasuga yanda zata maida yarinyar nan, Du’a tariga tabar gidan nan kenan har abada saidai in bata raye.

Ganin Du’a na gyangyadi akan kujera yasa ta tadata. “Du’a Du’a tashi kije ki kwanta adaki” ahankali ta tashi murya chan kasa tace “saida safe Grandma” murmushi tamata tace “kiyi alwala sanan kiyi addu’a kafin ki kwanta kinji” gyadamata kai tayi sanan tawuce, dakinta tabude tashiga tamaida kofan tarufe, bayi tashiga tadauro alwala kaman yanda aka umurceta sanan tafito, fadawa kan gadon tayi tana karanto addu’an bacci sanan taja bargo ta lulluba tana rufe ido fuskan mutumin nan tagani yay flashing a idanunta dasauri tabude idanunta tana yaye bargon tafito da kanta waje tanabin dakin da kallo, mutumin daya ciro ta daga rijiya she just saw fuskanshi, lumshe ido tayi ahankali still tana ganinshi saikuma ta girgixa kanta kaman tana kokarin koran abin dan bataso tana ganinshi, ahaka bacci yay awon gaba da ita……

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button