KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVEL

KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVEL BY M SHAKUR

Wani kallo yabi Mum dashi yace “I am so disappointed in you Hajara, halinki nabani mamaki and ki sauraren kiji bazan zauna inaji ina gani ki rabamin kan yarana ba, wlh duk randa kika kara attempting abinda kikayi yau kinasa anacirema yarana mata kaya kina kiran yara suyi ihu wlh wlh saina rabu dake take this as a warning” cikin kwantar da murya tace “kayakuri Alhaji na yarda nasan nai kuskure I know I took everything far, but raina abace ne maganan da Kaka keyawan fadi duk yadawomin kai, wlh Alhaji da gaske Du’a yar aljanu ce to inba hakaba ya za’ayi Muhsin dake tareda Nana kusan sjekaru biyu kenan yau kawai daga ganin Du’a yace ita yakeso yafasa auren wacce yasani for years, dududu bikinsu saura wata daya, tuntuni Kaka tace ka tattara yarinyar nan ke korata chan duniya inba hakaba bala’i da masifu iri iri sundinga samunta gidan nan kenan, yanzu maganan Muhsin baiwani dadani da kasaba amman what if dagaske yake eh? da gasken gaske yake shi yafasa auren Nana Du’a yakeso bahakan ya tabbatar mana itadin yar Aljanu bace ba kenan, wlh indai aka fasa auren nan saina kira Kaka na sanar da ita komi gwara tun yanzu nagaya maka sabida kar bayan kaji nayi kaga kaman na yaudareka ne” “tashi kifita daga dakin nan” Abba yay maganan cikeda fada, tashi tayi tace “narasa me kakeyi da yarinyar dakai karan kanka kasan bataka bace agidan nanba saisama baka ambato sunanta cikin y’ayan ka, hakanan wlh koma mezai faru saidai yafaru I am a mother bazan zauna inada zankada zankadanyanmata ba sukasa aure ba sabida yar aljanun da aka haifa maka agidan nan, gaskiya nake fadi I can go to any limit dannai protecting yarana, grounding nata adaki doesn’t solve anything dan gashinan fita take causing trouble, the best thing is tabar family mu takoma chan family su na aljanu” tai maganan tana bude kofa tafice abinta, gabaki daya duka abinda tafadi yajisu.

Ajiyan zuciya yasauke ahankali tareda fuzarda iska daga bakinshi yadade ahaka zaune sanan yatashi kaman an tsikareshi, bude kofa yayi yafice, hanyar dakin Mami yayi, ahankali yasa hannu yabude dakinta wani kamshi ne yamai sallama, shiga ciki yayi tareda maida kofan yarufe, tashi tayi tsaye daga kan gadon datake zaune idanunta sunyi jajir takakalo murmushi tace “sorry Dadyn Hamad bankawo maka abincinka ba” tazo da sauri zatabi ta gefenshi tawuce hannunta yakamo sanan yajawota jikinshi fuskanta ya tallabe yace “you’ve been crying ko jibi yanda idanunki suka kukkumbura” girgizamai kai tayi zatai magana saiga wani kukan kuma hakan yasa dasauri yasata ajikinshi yana bubbuga bayanta batare dayayi magana ba, tadade ahaka sanan tadago ta kalleshi tace “Abban Hamad kafin muyi aure ai kokai saida aka tabbatar maka dana warke ko naji sauki, babu any form of jinn ajikina, bana wasa da azkar safe rana da dare, yau shekara nawa muna tare ba kara having any form of attack ko mafarki ba, but yau nafara tunanin kodai sune baban Du’a di…….” hannu yadaura mata akan baki yace “shiiiiii banson maganan nan, kintaba ganin jinn sun haifi mutum? nine mahaifin Du’a, kawai Allah yabamu y’ace daban damu nothing more nothing less” girgizamai kai tayi tace “what if Muhsin da gasken yafasa auren Nana Yaya zamuyi? how are we going to explain this to the family Yaya zamuyi” saiga wasu sababbin hawayen, yatsanshi yakai yasharemata hawayen daya zubomata yace “when we get to the bridge we will know ta yanda zamu tsallaka shi karki damu kanki kinji” gyadamaikai tayi ahankali wasu hawayen na zubo mata tace “Dadyn Hamad Du’a batajin magana, we’ve grounded her for years now tundaga JSS3 har zuwa yau, amman kwanan nan tasoma sneaking tana fitowa, hakanan inaji araina something is about to happen, what if tasake samin attem………” hannunshi yadaura kan lips dinta yace “stop talking, and stop thinking negative, idan tafarka nida ita we will have some serious talk, yanzu all abinda nake bukata is natsuwa dan banda ita ko kadan, ina bukatan natsuwa sanan nasamu nayi tunani, bari nasami natsuwa dake” yana maganan yadauketa zuwa gado bashi yafito daga dakinba sai wuraren 5 ya chanza kaya zuwa jallabiya fuskanshi tayi wani annuri alamun akwai full natsuwa taredashi yasauka zuwa falo, Mum na zaune a falo tadauke kai kaman bata ganshi ba.

Saukowa Mami tayi taci sabon kwalliya Mum tabita da harara tace “kidaiyi kigama gobe zan karbi girkin” serving Abba tayi sanan tazauna gefenshi tana bashi duk wani abu dayake bukata.

???? KYAWUNA JARABTA TA ????

               ✍️M SHAKUR 

Free page
EPISODE 6️⃣

Bayan sallan isha’i Abba baima dade da dawowa daga masallaci ba shida Hamad dasu Muhammad ba mai gadi yayi sallama izini Hamad yabashi yashigo, shigowa yayi har gaban Abba yace “barka da hutawa Alhaji, kanada baki, sunce wai Alhaji Ibrahim mai tabarau ne” kallon Abba Hamad yayi yace “Baban su Muhsin ne Abba” tashi Mum dake zaune afalon tayi ta kalli su Muhammad tace “yara kuwuce mutafi sama Abban ku yay baki” binta yaran sukayi sukai sama, kallon mai gadi Abba yayi yace “kamusu iso” Maigadi yawuce yatafi, Hamad yakalli Abba dayaganshi anatse yace “Abba yaya zamuyi idan dagaske Muhsin yake”? Murmushi Abba yayi bai bashi amsaba yace “just stay here and learn, duk randa bani kaine zakai making decision akan kannenka mata” gyadama Abba kai yayi daidai lokacin mai gadi yay sallama yabude kofa yashigo dasu hakan yasa Abba da Hamad suka tashi don agaisa, wasu Manya manyan attajirai ne su uku sai Muhsin dake taredasu kana ganinsu you don’t even need an explanation kasan masu hannu da shuni ne, hannu Abba yamika musu cikeda girmamawa suka gaida dan mahaifin Muhsin ne Alhaji Ibrahim maitabarau sai kannenshi guda biyu Alhaji Isyaka Maitabarau sai Alhaji Mubarak Maitabarau, sosai Abba yagaisa dasu cikin mutuntawa yasa suka zazzzauna Muhsin shima ya gaida Abba cikeda girmamawa ya amsa, Hamad ma yagaidasu suka zauna cikeda girmamawa, shigowa Uwani tayi takawo drinks da ruwa sanan tawuce falon yay shiru.

Gyaran murya Mahaifin Muhsin yayi yace “To bari mufara da kalamai mafi kyawu wato da Sunan Allah Mai Rahama Maikuma Jinkai, Alhaji kaganmu agidanka da dare haka kuma unannounced ko, bawani yakawomu nan ba sai wanan yaron” yanuna Muhsin dake gefenshi da kanshi ke kasa, sanan yakara sauke ijiyan zuciya yace “wlh Alhaji idan nace namasan ta yanda zanmaka bayanin nan kafahimta tonamaka karya amman bari nafara da tantance gaskiyan lamarin kafin nakoro bayani” yay dan shiru kafin yanisa yakalli Abba kaman yanda shima yake kallonsu yace “Alhaji wai dan Allah kanada y’a mai sunan Du’a ne? Danni wayanda muka sani shine wanan Baban dan naka wato Hamad, Aisha, Hawwa, Amal, Aneela, Asiya da Muhammad da Mudasir, dan Allah katabbatar min da gaskiyan lamarin nan kanada y’a mai sunan Du’a ne wacce duk bamusanta ba”? Shiru Abba yayi yana kallonsu kaman bazaice komiba danhar dagakai Hamad yayi yana kallonshi sanan yadan nisa yace “eh inada y’a mai sunan Du’a” ahankali Baban Muhsin yace “to Alhamdulillah, nasan banida wanan hurumin dazan tambayeka maisa baka taba ambato mana itaba ko wani abuba dan nasan kanada dalilinka nayin hakan, daman tabbatarwan kawai ita nake bukata tunda yanzu ka tabbatarmana kanada y’a mai sunan Du’a toga dalilin da yakawomu wurin ka da daddaren nan” ya sakeyin shiru sanan ya numfasa yace “shi so hallitan ubangiji ne, danhaka so gaskiya ce hakama ki, Alhaji d’ana yazo gidanka jiya sai cikin iko irin na Ubangiji yaci karoda yarka Du’a kuma Allah ya jarabceshi da sonta ainun aranshi danyau haukace mana kawai ne baiyiba ga kannina nan katambayesu kaji, yace shiyabarma Nana duka abubuwan dayamata amman yafasa aurenta dan baya sonta Allah yahadashi da Du’a ita yakeso itakuma yakeson Ya aura inhar ka yarda zaka bamu” tunda suke maganan Abba yake kallonsu babu ko kyafta ido, yakai kusan minti biyar ahaka baice komiba dakin tsit kakeji sanan yay gyaran murya yace “to Alhamdulillah naji dadi yanda kukazo kukasamen, shi gaskiya dayace koda batada dadin ji, naji dadin yanda kuka sanardani gaskiya batare da kwana kwana ba ko kuma boyeboye ba danhaka nima zan sanardaku gaskiya Alhaji” yay maganan cikin mugun hikima da ilimi sanan yace “it’s very okay idan danku Muhsin yaji bayason y’ata bazai aureta ba shi aure daman yagaji haka ko anyi ana rabuwa, amman gaskiya itace bazan iya bama Muhsin wacce yaji yakeso dinba wato Du’a” dasauri Muhsin yadago kanshi yakalli Abba idanunshi sunyi jaaa sosai.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button