KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVEL

KYAWUNA JARABTA TA COMPLETE HAUSA NOVEL BY M SHAKUR

Abba yacigaba. “Alhaji kai mahaifine haka nima mahaifine, yanzu wani yazo yana tareda yarka har a kusa bikinsu sai yaga kanwarta yace yafasa aurenta kanwar yakeso zaka yarda kabashi”? Abba yamai tambayan shiru Baban Muhsin yayi yakasa amsa tambayan, Abba yace “duk wani abinda zai raba kan y’ay’ana ko family na bazan taba yinshiba, gwara afasa auren gabadaya da inbaka wata, dan haka I am sorry idan maganata ko amsata bata kuma dadi ba amman bazan iya baku auren Du’a ba, as for kayayyakin dakuka kawo duka in sha Allah zamu aiko muku dashi, Allah yasa hakan ne yafi alkhairi”

Kafinma Baban Muhsin yayi magana Muhsin ya rarrafa da gudu zuwa gaban Abba, kneeling yayi yahade hannayenshi biyu muryanshi narawa kaman wanda zai fasheda kuka yace “Abba Abba wlh wlh wlh na rantse da Allah bawai dan cin mutunci ko toxarci kodan inci zarafin Nana nai hakaba, wlh kawai Abba azuciyata naji bana sonta wlh tunda nasa Du’a a idanuna nake so ko kulkewa nayi saina ganta, Abba kataimakamin dan Girman Ubangiji” tunda yake maganan daga Abba har Hamad kallonshi sukeji, ahankali Abba yasa hannayenshi yakama hannun Muhsin dayake rokonsu dashi yace “Son kayakuri kotayaya zaka roken I don’t think I can risk my family for this, I can’t stand naga kan family na ya rabu sabida one bad decision dazanyi ba, bazan iya baka Du’a ba, it’s final” to Abba biggest suprise kawai yaga Muhsin yafashe da kuka sosai, daura kanshi yayi kan cinyan Abba cikin kuka yace “Abba wlh idan baka bani Du’a ba zan iya mutuwa dan Allah kayakuri, I am sorry if I hurt you sabida nace banson Nana….”

Iyayenshi kasa koda motsi sukayi, sunsan Abba made the right decision dankosu basuso sunzo ba mugun so da gatan dasukema Muhsin dinne yasa sukazo su gwada luck dinsu.

Ganin yanda Muhsin ke kuka yasa zuciyan Babanshi yafara breaking shifa baida wanda yakeso kaman Muhsin aduniyan nan, kallon Abba yayi yace “Alhaji name anything dakakeso wlh zan maka indai zaka bama dana Du’a dinan dayakeso, kaga wlh zan iyasa acireka daga matsayin HOD dinan abaka Deen na BUK gabaki daya, idan bakaso zan baka aiki akasan waje, wanan gidan na chanza maka nabaka lafiyayyen gida anan GRA kano, mota kudi koma mekakeso just name it zan baka inda zaka hakura kabama yarona wacce yakeso kaganshi nan shikadai gareni kataimakamin please” sake tashi Muhsin yayi daga jikin Abba fuskarnan nashi hawaye ya wankeshi yahade hannayenshi yana kallon Abba, dan murmushin manya Abba yayi yace “I am happy da position da dukiyan da Allah yamin a rayuwa bana bukatan kari, nariga nayi maganata idan babu matsala zan haura sama inada y’a mara lafiya naduba, Hamad you can see them off okay” gyadamai kai Hamad yayi Abba yatashi, sosai Muhsin yafashe da kuka, kanin Baban Muhsin Alhaji Mubarak yatashi yay wajen Muhsin yace “Kato dakai kana kuka, ga matanan agari kaman ledan pure water kodaga kasan waje kakeso kayi aure Babanka zai auromaka tashi mutafi” kintashi yayi saifada sukayi da gaske suna dagashi sanan suka fitardashi daga falon Hamad yatashi yarufe kofa jikinshi a sanyaye.

koda Abba yatafi sama dakinsu Nana yabude yashiga, bin kowa nadakin yayi da kallo Nana na kwance kaman mara lafiya idanunta a lumshe sai Hawwa ce idanunta biyu, tana ganin Abba tace “sannu da zuwa Abba” gyadamata kai kawai yayi yakalli Du’a dake barci har lokacin sanan yajuya yafice yakoma dakinshi, ko zama baiyiba Mum tabude kofa tashigo dakinshi, juyowa yayi yakalleta sanan yazauna akan kujera yana ganin idanunta kadai yasan taji duka maganganunsu a falo dan idanunta sunyi ja kaman ma hardan kukan bakin ciki tayi. zama yayi kan kujera yana kallonta, daurewa tayi tahadiye abinda ya tsayamata arai tace “yakukayi dasu Alhaji” jaridan shi dakekan table yadauka ya gyara zamanta akan hannunshi sanan ya kalleta yace “idan Allah yakaimu gobe duk wani abu na gidansu Muhsin ki tattarasu tass zansa azo adauka amayar musu” wani irin faduwa da rawa gabanta keyi dan babu kalan burin dabata dashi akan auren Nanan ta da Muhsin, finally yarta zatai rayuwa gidan masu kudi shine tashi daya kaman aradu zancen aure yamutu, daurewa tayi tace “does that mean babu zancen aure? Ba za’ayi auren Nana da Muhsin ba kenan?” bude jaridanshi yayi zaifara karantawa yace “eh babu zancen aure, Allah yabata wani mijin nagari” yay maganan tareda gyara zama kan kujera yana karatun littafin shi dakyau sosai take kallonshi jitake kaman tarufeshi da duka tsabagen bakin ciki, wai ace anfasa auren yarsu 26yrs finally year student din yarsu, yarinyar dayasan tanason Muhsin dinta yau all of a sudden amman this guy is still acting kaman it’s nothing, jitayi idanunta sunjuya sama wutan bala’i nacimata zuciya tajuya fuuu tafice ko tsayawa kulle mai kofa batayiba tana fita tacikaro da Hamad daya hauro sama zaizo yaduba Du’a, idanunta kadai yagani yasan ba lafiya hakan yasa yajuya dasauri zai koma dasauri cikin mugun ihu tace “dan ubanka wlh katafi saina tsinemaka albarka agabanka aka fasa auren yarka bakai komi dan taimakon lamarin ba dawonan” juyowa yayi ahankali sanan ta shiga kwalama yaranta kira. “Amal Asiya” dasauri suka fito daga dakin su harda Aneela yar Mami, jin ihun Mum tasa Mami itama tafito, kama hannun yaran tayi tawani irin tura kofan dakin yaran, yanda kofan yay mahaukacin kara yasa Du’a ta firgita sosai ma tabude idanunta, shigowa Mum tayida Hamad da Amal da Asiya, sanan ta kalli Nana da Hawwa daduk ita suke kallo tace “Nana saurareni kiji anfasa aurenki, Muhsin har kuka yake yakama kafan ubanki yana roka abashi wanan yar Aljanun” tanuna Du’a, dasauri Hamad yace “Mum please stop all this bahaka ake handling situation like this ba sokike zuciyan Nana yabugu eh”? Cikin bakin masifa Mum tace “buguwa na nawa kuma” tasake juyawa takalli Nana da kallonsu kawai take kaman gunki tace “Nana Muhsin yace bazai aureki ba yanzu haka ubanki yace ahada komi nasu harda akwatin dasuka kawo naki amaidamusu abinsu gobe dasafe” kokarin yunkurowa take tatashi tasauko daga gado kawai jiri yadebeta ta yanke jiki zata fadi dawani irin sauri Hamad yatareta yace “Nana Nana” juyowa Mum tayi takalli Mami data tsaya daga bakin kofan tana kallonsu kawai saitaikan Mami shakumo Mami tayi tace “wlh saina kasheki duk abin nan dake faruwa dadi kikeji yarki ta kacema y’ata miji har celebration kike kikaji Babansu daki kina cinshi da rana tsaka” ganin Mum ta shako Mami yasa dasauri Hamad yasakinma Hawwa Nana yatashi daga Du’a har duka yaran kuka suke. “Hajara!!!” Abba yakira Mum da mugun karfi daidai lokacin da Hamad ke cire hannunta daga wuyan Mami datahau tari sosai, Abba cikin fushi yace “tattara yinaki yinaki kibarmin gidana” wani kallo tamai tace “naji zan barmaka gidanka amman wlh saidai nabar gidan da daddaren nan da yarana duka dan bazan taba barinsu da wanan yar Aljanun dakuke raina agidan nanba dansaita hana yarana aure” cikin fushi Hamad yace “Mum wai what is all this eh haba Mum? Auren Nana has nothing to do with Du’a kawai Allah ya kaddara ba mijinta bane, kidena kiran Du’a yar aljanu, Mum this isn’t right mekike koyama su Hawwa ne, haba Mum haba” nuna kanta tayi tana kallonshi tace “ni kake gayama magana Hamad eh” saikuma tafashe da kuka tace “kana gani sabida Du’a anfasa auren kanwarka sanan kace babu ruwanta ba laifinta bane, kanwarka tasami miji gidan arziki gidan hutu kasan gwalagwalai nawane aka samata a akwati eh, har mota ya siyama Nana ranan da aka kaita yace zai bata yarinyar chan tai amfani da tsafin jikinta ta kwacema kanwarka miji kace kaza kaza, nagode Hamad” tashi tayi ahankali tana kuka sosai tawuce tashiga dakinta, zama dirshan Mami tayi akasa takife kanta akafafunta, ahankali Abba yatako yashiga dakin Nana yakalla da Hawwa ta yayyafama ruwa ta farfado sosai take kuka shiru kawai yayi saiyajuya, Du’a yakalla data farka itama tana kuka sosai tana goge idanunta da bayan hannu, fice wa kawai yayi daga dakin. Ranan banji akwai wanda yayi kyakkyawan bacci agidan ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button