MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL BY Janafty

Hajiya Binta ta bishi da kallo tana kada kai,idonta ya ciko da hawayen takaichi da kuma haushin iyayenta da suka biyema Rudin Duniya da kuma tarin Dukiya suka kawota inda ba”a san mutumcinta ba,daga Uban har yar duk basu da mutumci babu wanda ke ragamata.

Dauke hawayenta tayi tana mirmishin karfin hali,Tuna duk mutuwa ce taja mata wannan Tonon Sililin,da”ace Abban JODA na raye ta tabbata da bata auri Alhaji Malik ba,balle har tazama Abun wulakantawa awajensu.

Mikewa tayi rike da wayarta tashige wani korido tana kwalama Atika mai aikinsu kira,domin ta umarceta ta shirya lunch bisa Dinning area.

Katon Falo ne,wanda yaji kayan alfarma,Tunda tashiga tafara yadda kayanta,Tacire vail ta Wurga ta cire band din kanta,ta warware gashin kanta bayan ta Fara cire botir din Rigarta gabadaya halittun kirjinta dake jikin beriziya suka bayyana,Peter ko da joy suna tsaye kyam,don madam bata basu daman Tafiya ba,Indai Tsiraicin Madam ne,Su Tuni sun dade da haddace kamminshi don bata da kunyan idon maza,Hatta Swining pool in zata wanka tare dasu take zuwa tayi Tsirara daga ita sai pant agabansu ko gefen gyalenta.

Murya ta saka tana Fadin”Merry…Dose…”Take Fada cike da Fushi sai gasu sun Bude wata kofa sun Fito da gudu agabanta suka zube suna Fadin”Srry madam…SrrrY…”Wani Wulakantattacen kallo take binsu dashi kafin ta sanya kafa ta shuri merry sai da ta kifa,lokaci daya ta gaurama Dose mari tana Fadin”U too u are Animal,..”Take Fada tana huci Baya sukayi suna kuka suna bata hakuri da hannu ta dakatar dasu kafin tace”,last chance…”Bata gama Rufe baki suka mike daya tafara kokarin ciremata takalmi daya kuma tafara kokarin karisa balle mata botir din Rigarta bayan ta ciremata Coat da hannu tayi musu peter alamu, sai kawai naga sun nufi wani kofar glass,wanda sai  da ta dauki hoton Fuskokinsu ashe Na”urace awajen kafin ta bude musu su Shiga,sun Shiga ba dadewa sai gasu,sun Fito wanda kafin Su Fito sai da Na”uran tagama cajesu tsab ta tabbatar da basu tare da komai kana ta barsu suka Fito,suna Fitowa tayi directing dinsu da hannu alamar su Fita,kai tsaye suka bude kofa suka Fita,bayan su merry sungama cire mata duka kayanta,harda bra da pant tsiraranta haihuwar uwarta suka dagata tsab,sai cikin katon bedroom dinta inda katon Tiolet dinta yake,wanda yaji kayan alfarma kyace baza”a mutu ba,cikin jazucci suka sakata bayan suncikashi da wani Ruwan kumfa,Dose ce ta Fice ita kuma merry ta fara Yimata wanka tana kwance ta lumshe ido ko agefen gyalenta..

Niko nace KUTUMAR UBAN CHAN????

Dose na Fitowa takoma kayattacen Falon ta kwashe duka kayanta,kafin takoma Toilet din ta watsasu cikin wani dogon kwando na tara kayan wanki,Fitowa tayi kafin ta isa wani makeken Abu wanda ke dauke da glass,ashe Na”urace Sai da Ta tantance Fuskar Dose kafin wata yar kofa ta bude,Kayane jere cikin tsari iya kallonka mallam,dogayen Riguna,riga da wando ne,suit ne mini sikat da mini wando,Duk sagale cikin hanger,kai kace ka shiga bouitque ne,Wata yaloliyar Doguwar Riga ta daukomata wacce marabanta da Tsirara kadan ne,saboda tasan yanzu barci zatayi kuma iyakarta gwiwa,ta Fito mata dashi kafin kuma wajen ya Rufe kansa,Sun dauki tsawon minti talatin atiolet din kafin Dose ta kuma suka daukota wacce suka nannade da wani katon Towel,suka zo suka ijyeta kan wani dogon Stool,ban gama mamaki ba,sai da naga tana ta Shafemata da mayuka masu tsada itako tana zaune idonta na lumshe,har tagama ta fesheta da body sray,Dose ta matso kusa tana gyaramata zaman gashinta wanda yadan jike kadan da Ruwa,tana kokarin kunna Hand drayer,ta dakatar da ita,da hanzari ta dauko yar Rigar data dauko ta ziramata wacce ta Fito mata asalin tsarin kirjinta,tunda babu bra babu pant,Dose ita kadai ta dagata bata sauketa ako”ina ba sai akan wani gado,mai kama da alkaki saboda yadda yake amulmule,wani karamin Filo fari dake gefe ta Rumgume tana lumshe ido,Katon blanket ta dauka ta Rufamata shi har zuwa Kanta

Gefe suka koma ko motsi basuyi suma dana kallesu suna sanye da Riga fara,sai bakar biri da wando,sai Hula akansu kace wasu ma”aikatan hotel,sai da tasha iska kafin tadaga  musu hannu,da hanzari suka kada kai suka Fice suka jawomata kofar,nan kowaccensu ta maida hannuwanta abaya,domin akidar madam in tana barci babu mai tashinta sai ta tashi da kanta,kuma zata iya bukatan wani Abu,kuma in tamaka kira daya baka zo ba,korace sudinma tana daga musu kafa ne don tana jin dadin zama dasu.

   _____

ABUJA

“”Duka iyalan gidan sun hallara bisa babban Dinning area,mai kama da Fili guda,ajiyane da daddare suka kara samun Zuwan wani dan gidan,bayan Saleem,wato Ya marwan wanda yake aiki alagos,Zaune suke dukkansu suna breakfasrt suna dariyan hajiya wacce ta sanya kujeranta kusa data saleem,Ummi na kokarin saving dinta,tayi Saurin Tsoma hannu a filet din gaban Saleem,wanda yake cike da Soyayyan dankali da kwai,bata Fuska yayi kamar yayi kuka,itako hajiya ta cika baki hartana maida Saura a Farantin,Ummi tana Dariya tace”Hajiya ki barmishi kayanshi bari na zuba miki naki..”..

Hajiya ta gyara zama tana Tsungulin Saleem tace”Barni Aisha yau tare da Ja”irin nan zan karya..”Tafada tana kara saka hannu ta cika baki,har miyau dana baki suna biyowa,Kauda Fuska Saleem yayi yana Fadin”Na Shiga uku Ummi,kalli harda miyan bakinta take sakamin..”Dunguremai kai tayi tana Fadin”An saka din,don kaniyarka,Wlh in kaja tsiya zan maka kaki yanzu nan,kuma wlh na matseka saika hadiye,..”Tashi yayi da Sauri yana kakaro amai,tako damke hannunsa gam,taki sakinsa,Ya marwan dashi da Saleema suna ta tsintsiran dariya Abbi na zaune yana kallonsu,don yasan koyayima Hajiya mgana baji zatayi ba,Ummi ko bata saka baki ba,sanin halin hajiya in Tafara Abu bata iya bari,Saleem din ne kadai mganinta.

Gani yayi tasaka karfinta tana Rikeshi tana neman ta maidashi inda yatashi,Ganin haka yasa ya rike mata hannu yana Fadin”Sakarni kiji wata mgana..”Hararansa tayi tana gyara daurin dankwalinta tace”Anki din,ni zakama wayau,ai wlh yau in har ba lbrin kasamu matar aure zakamin ba,ko ubanka kabiru bai isa ya kwaceka ba,sai kasha majina na..”Tafada tana kebe Fuska,Ummi ce ta rike baki tana bin Fuska Saleem da kallo…

Shuru yayi yana bin Hajiya da kallo kafin yace”Really,,? kina son nayi aure kenan hajiyata..,?”Jin haka yasa ta washe baki cike da goro tace”Sosaima Haba Salihu,kunfa girma kungama balagewa asannin haihuwarku a kumo harda masu mata biyu,bama daya ba..”Rausayar dakai yayi yana Fadi cikin Ransa” Dis iz d right Time….”Yafada kafin yakalli hajiya yana Fadin'”,kamar ko kinsani Hajiya mganar auren ce tadawo dani wannan weeked din..”

Kowa dake wajen yadauka yanamata wasa ne don ta sakeshi,shiyasa harda Ummi amasu dariyan,kura masa ido tayi kafin tace”Da gaske kake Salihu..? Gyada mata kai yayi kafin yace”Eh da gaske nake Hajiya ina son kisa baki Abban yaje nema min auren yarinyar danike so..”

Jin yadda yayi mganar babu alamun wasa yasa kowa yadaina dariyan dayakeyi hatta Abbi dake ta cin abinsa sai da yadago yana kallon Saleem,wanda ya kurama waje daya ido,Jansa kan kujeran daya tashi Hajiya tayi bakinta yaki Rufuwa tana Fadin”Alhamdulillah Allah yakarbi Addu”a ta,to maza ga kabirun nan,sanar dashi wata yarinyace,Allah sa dai yar gidan Mutumci ne..?Bai wani Damu ba kai tsaye yace””Ba wata bace illah Diyar shahararran Dan kasuwan nan wato ALHAJI ABDULMALEEK DANKASUWA…”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button