MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL BY Janafty

Shafa addu”anta tayi kafin tace”Muntashi lafiya? sai ina naganga cikin Shiri kamar wanda akace gawani dan fashi chan? Dan mirmishi yayi kafin yace”Kaji hajiya,yo mu ai basai mun jira ance ga Dan fashi ba,mu da kanmu muke Fita nemansu,Tunda kinsan bazasu kawo kansu ba..”

gyada kai tayi tana Fadin”Hakane kuma toh Allah yayi jagora..”Da Amin ya amsa kafin yace”Hajiya zan Wuce,nazo ne nayi miki tuni kan mganarmu ta jiya,wlh am serious don Allah ki matsama Abbi yaje yanemanin Aurenta plz..”Kai tsaye hajiya tace”Ina zanyi sanya,ai dolensa nema yaje,Abunda muke ta nema kuma Allah yakawo to me zamu jira?karka damu insha Allahu zaka aureta Tunda na lura kana sonta..”

Dan cije baki yayi baiyi mgana ba,saima Kallon agogon fatan dake hannunsa yake,kafin ya mike yana Fadin”Zan Tafi hajiyata,nidai kiman kokari kome ke nan,zamu waya..”bata tashi ba tace”Toh Allah ya tsare…”Da Amin ya amsa kafin ya Fice.

Daga Dakin Hajiya ko Dakinsa bai koma ba,yayi waje,motarsa ya Fada yamata key yana zuba hon,da hanzari maigadi yazo ya budemai get yana mai Fatan isa lafiya,babu wanda yasan Tafiyarshi agidan sai hajiya,shiyasa har sai da  akazo breafast ne,aka Farga saleem bashi agidan lokacin da Marwan ke tsiyan yasan Abunda yayi yaki Fitowa Hajiya ce tace”,Wa..? Salihu ai ya dade da isa zamfara yanzu…”ba su kadai ba hatta da Ummi sai da Abun na Saleem yafara bata mamaki babu dai wanda yace kanzil kowa ya barsa da Abun Tunda ganin Shikanshi mai gidan bai ba mganar wani muhimmanci ba.

shiko Abbi yaki bada Fuska ne saboda kada sumai wata mgana mussaman Ummi wacce Tun daren jiya taso tatadamai Tsiyarta yaki bata Fuskar yin hakan,data fara zencen ita bata yarda ba,kuma shima kada yabiyema Saleem,haryanzu yaro ne baisan inda ke mai ciwo ba,ammh ita bazata bari Akawo mata wannan Tsinanniyar yarinyar amtsayin Suruka ba ko alama.

  Shikanshi Abbi ya Shiga dogon Tunani game da bukatar Saleem,duk shima yana da lbrin yarinyar kaf bamai dadi bane,toh ammh yayi Duba zuwa ga wani Abu,duk wanda yayi sanadiyar Shirriyan wani Shima yana da lada,sai dai kuma kafin ya je wajen Mahaifinta sai ya kira Saleem ya tabbatarmai ba saboda Dukiyan mahaifinta yakoson aurenta ba,duk yana da Shaida sosai kan tarbiyan ya”yansa,.

Baya da Haufi kan Saleem domin yafi Shakuwa dashi fiye da marwan,wanda baima yi karatunsa a nageria ba,kuma yana da masaniyar Jarumi ne na karshe,wanda zai iya tankwasa ko wacce mace indai tana karkarshinsa ne,kuma aure ba haramun bane,sunnar ma”aiki ne kuma Dukkansu akanshi sukazo Duniya,shiyasa batare da shawara dakowa ba ya yanke zai kai ma Alhaji malik ziyaran Farko tun bayan kammallah jami”ar Dan Fodiyo basu kara samu zama sosai ba,sai dai haduwa sama sama,wanda bayan yazama IGP sun hadu sau biyu wajen taro wanda shima agayyaceshi ne yaje suka hadu,suka gaisa duk da kowa yana da nombar kowa,ammh basa mgana awaya,saboda yanayin aiyukan kowannensu.

Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan MALIKA MALIK Akan Naira 200 kachal????,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar 09069067488 Sai kun zo ina maraba daku masoyana..

Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal????shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani

07065481260..Ko kuma 09069067488

JANAFTY

????MALIKA MALIK????..!
(Sai na rama..)

ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ????

Mallakar:Janafty????

6

Monday

monday Tushen aiki ko bature na tsoronta,Tun safe Abbi ya Shirya bai sanar da kowa ga inda zashi ba,ko Ummi bai sanar da ita ba,saboda tana Fushi dashi Tun safe ma ta Fice zuwa babbar kotun data ke aiki A higher suprime court Abuja.

Karfe 10:00am na Safe suka dau hanyar katsina dagashi sai Direbanshi,Wanda marwan yaso ya tukosa,ammh ya dakatar dashi saboda bayason kowa yasan inda zashi.

kokafin 12 da wani abu,suna kofar gidan Alhaji Abdulmalik Dankasuwa dasuka zuba hon cikin motarsa kirar vibe2k19,Da megadin ya leko sai da yatambayesu,ko suna da ganawa dashi Alhaji Abdulmalik din ne? amsa Abbi yabashi da cewa “A’a baisan da zuwanshi ba,ammh asanar dashi wani tsohon abokinsa ne daga gombe…”

  Koda Alhaji Abdulmalik yaji  Haka Abun yabashi mamaki,don baitaba kawowa Cewa Kabir kumo bane,sai ya bada Umarnin abarsu su shigo,koda suka shigo cikin babban Falon gidanshi na kasa,aka sauke Abbi wanda yaji kayan alfarma kamar baza”a mutu ba,ko kafin kace kwabo ancika gabansa da kayan lashe lashe da shaye shaye.

Yafi minti goma zaune kafin Alhaji Abdulmalik ya Shigo sanye da shadda gezner fara riga da wando,Abbi zaune yabama kofar Shigowa Falon daga cikin gida baya,shiyasa har Alhaji Abdulmalik ya kariso yana Fadin”Barka da zuwa…”

  Juyowa Abbi yayi yana mirmishi yace”Yauwa….”Yafada yana mai kayatattacen mirmishi,Sake baki Alhaji Abdulmalik yayi,kafin ya rike bakinsa yana Fadin”Kabir kumo…? Yafada yana nuna shi,shima Abbi nunasa yayi yana Fadin”Na”am Abdulmalik Sa”ad..”

yafada Fuskarsa da yalwa da Fara”a Rumgume juna sukayi suna mai murnan ganin juna kafin su saki juna mamaki bai bar Alhaji Abdulmalik ba,kara rike hannunsa yayi yana Fadin”Am very Suprise dana ganka agidana kabir,alhalin ni yakamata na fara kawomaka ziyara? garin yaya haka IGP guda yana yawo babu wasu masu tsoron lafiyanshi..? yafada yana dariya.

Kafadansa Abbi yadaka yana Fadin”karka damu kanka Abdulmalik,gashi na nafara zuwa,mganar zuwa da Masu tsorona kuma,ni na dakatar dasu saboda bani son kowa yasan nazo ne,so nake ka ganni amtsayin Kabir kumo dina ba IGP Ba..”Dariya suka saka kafin su koma su zauna Alhaji Abdulmalik na Fadin”Am so happy wlh..Ya hanya..?

Nan suka shiga gaisawa,sai kuma hirar yaushe gamo tatashi,dakuma tambayan iyalai,nan Abbi ke sanar dashi ya”yansa Uku maza biyu mace daya,Shikuma ya sanar dashi Yarsa dayace aduniyan nan,yana ta bashi kadan daga cikin nasarorin Daya samu atafiyar shi kasar England.

Alhaji Abdulmalik dakanshi ya shiga cikin gida yakira Hajiya binta tazo suka gaisa da Abbi,wanda suka gaisa cikin sakin Fuska,kafin takoma ciki,nan da Alhaji Abdulmalik ya Umarci Da a shirya Abinci mai rai da lafiya ga Amininsa Kabir kumo,wanda suka baje suna ta hiran yaushe gamo,suna Tuna rayuwarsu ta mkranta suna Dariya Abun gwanin ban sha”awa.

Malika bata Fito daga dakinta ba sai around 2 na rana koda ta Fito tana sanye da wani damammen wando pencil,wanda ya Fitar da duka suran cinyoyinta,rigar jikinta kuwa bata da hannu,wanda dakyar ta Rufemata cibi saboda rashin tsawo,kanta babu dankwali dama bata saba sawa ba,sai gashinta wanda ta daureshi daga tsakiya da band,ta saki jelan yana Mata yawo abayanta,Ear phone akunnenta wacce take jin waka da faskekiyar wayarta.

Dakin Daddynta tashiga ta iske baya cike,da sassarfa ta sauko Falo tana kwalama Hajiya kira,tana kichen suna aiki da Atika,ta Fito tana amsawa karo sukaci da ita tana Fadin”Hajiya ina Daddyna..? na dubasa dakinsa baya ciki..? ta Fada tana Wani yamusta fuska,tana mele baki wanda yaji wani pick din jambaki.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button