MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL BY Janafty

Sau daya tataba zuwa malumfashi,ammh sai da tayi danasani saboda gabadaya garin bai mata ba,kama daga yadda aka dinga kallonta kamar anga wata bakuwar hallita,saboda yanayin shigarta uwa uba babu kallabi akanta sai gashinta data daureshi ta baya ta bazoshi,ba mutanen garin ba hatta dangin Abdulmalik ranar sunyi tir da Dabi’un Malika da suka mata mgana tayi musu Rashin mutumci ta zagesu tas tayi tahowarta,da suka kira mahaifinta suka sanar dashi sai ya goyi bayan yarsa yakuma ce ko suzo subata hakuri ko kuma ya cire hannunshi akansu,sanin da sukayi in ya cire hannunshi akansu sun bani sun lalace don basu da kamarsa yasa sukayi mota guda suka zo suka ba ma Malika hakuri wanda sai da baban yasa baki kana tace ta hakura,Tunda ga lokacin kowa yake kiyayewa saboda ita bata ganin kowa da daraja sai mahaifinta bandashi kowa zata iya takashi saboda kudi,tana ganin Duk wani mikamin Duniyan nan bashi da wani amfani in ba kudi ba.

Malika ta zarce Duk Tunanin mai karatu ba yarinya bace shekaranta 27 Aduniya ammh in ka ganta sai kace yar Shakara 20 ce saboda yadda ta mori jiki,babu gidan Talabijin da gidan Jaridun da ba”ayi hira da ita ba,shiyasa sunanta yafi na mahaifinta shahara aduniya,malika ko abinci bataci da kanta bata akeyi ko wanka sai anyi mata saboda gata komai da kuka sani yimata ake,saboda tace matukar kudi na mganin komai to zasu mata mganin dukkan mtsalanta,Dawowarta Nageria basa ta rage zuwa clubs da party wani lokacin sai tsakiyar dare take dawowa  Akullum Alhaji Abdulmaleek Dankasuwa yana takaichin hallayar Malika musaaman ma n zuwa club da party,ammh bashi da yarda zaiyi da ita,don baya iya tsawarta mata ba, kana tana da wayau bata da yarda ko kadan,ko ma”aikatan ta da excort din ta bata yarda dasu ba,tana ankare dasu kuma tana bibiyan dukkan motsinsu.

Abu dayane batayi Shine Zina,Malika bata yarda Akala tashiga tsakaninta dawani Namiji ba,sai dai in ta kasuwanci ko kuma abota,shima tun barowanta US rabonta da abota da Namiji,kuma tun alokacin ne da Sunan Abota take yarda tayi kiss da mutum sai dan Abunda ba”a rasa ba,ammh bata yarda wani yaketa mata budurci ba,saboda tana da bala”in wayon tsiya shiko mahaifinta tunda ya samu ya yakiceta da zuwa coci da karanta bible hankalinshi ya kwanta,sauran abubuwan datake kuma ko Abun na damunshi bai iya mata mgana Saboda yadda yake matukar sonta da kaunarta,so daya yataba kwantatan yimata Fadan ta rika sanya kayan hausawa,kuma ta dinga mutumta Hajiya binta, da malika tayi Fushi sai dai kawai yasamu waya kan cewa tana England takoma wajen dangin mamanta hankalinshi yatashi sai da yaje da kanshi dakyar da lallashi ta yarda zata dawo ammh da sharadin bazai kara takuramata ba,dole ya yarda da haka saboda yana Tsoron kada watarana Malika tayi Ridda takoma Kafura,duk ko ayanzu marabanta da kafurci ne kadan ne,banda sallah bata wani Abu na bautar Ubangijinta.

itama sallar ba da kyau takeyi ba,ko Fatiha banajin tagama iyawa Saboda lalace babu Abunda tasaka agaba sai Duniya tanaYin duk Abunda tagama dama,ko dabi”ar Tubewa zindir wasu matan nayi miki wanka,Ai dabi”ar yayan Turawa ne wadanda basu san addini ba,ammah kome malika ta zama Aduniya sanadin yana wuyan mahaifinta domin Tun farkom gina Ginshikin samunta bai bi yarda Addinin mu ya tsara ba,koda aka umarceka ka auri Ahlul baiti bai chanchanci bayan haihuwar malika ya mikama Turawa rikon yarsa ba kuma yana sane da cewa sudin ba musulmai bane,taya zasu so malika ta koyi addininshi,shiyasa suka koyar da ita duk dabi”unsu da addininsu saboda ko gaba kada ta barsu.

Ranar da suka hadu da Saleem har ta mareshi ta dawo Daga kaduna ne,wani party ne na ya”yan manya marasa jin mgana da”aka Shirya to daya daga cikinsu Friend dinta ne,Tun suna US shiya gayyaceta taje,shine da zasu dawo sukayi dare har su Saleem suka taremata motoci,Tun sadda Abun yafaru batakara Tuna wani hallita ba balle ta damu da Furucinsa na sai ya rama, ita tana ganin Shirmene da yarinta da kuma talauci da rashin nayi ke damunshi yasa,tun awajen ta tararrashi ta watsar ta cigaba da harkan gabanta,duk a iya tsawon wannan Shekarun babu Abunda ya ragu na Hallayar malika saima Abunda ya karu,Hajiya binta ko bacin kashin da bata gani har marinta malika tatabayi,ammh Alhaji malik bai dauki mataki ba,ita da banza Duk dayane,kallonsu kawai take tana jiyema Alhaji Ranar da zaiyi nadamar Turban daya dora Tilon yarsa akanshi.

Tsakanin Malika da Joda ko basu da wani kyawawan alaqa,duk da ba sosai sukayi haduwa ba,wani lokacin in Malika na gida Malumfashi Joda ke Tafiya saboda ita yarinya ce mai hankali da gudun zuciya ga natsuwa,gata bata hayaniya,itakadai sai ta Shige daki tana kuka,in taga cin kashin da malika kema mahaifiyarta.

Abun na damunta ammh bata da yarda zatayi sai hakuri saboda ko ita bata da bakin mgana, Saboda akwai lokacin da Makila tama Amminta rashin kunya,sao tayima malikan mgana,shikenan ta juyowa ta kasheta da mari,ta kuma sanya su Peter suka Dauketa chak suka Fita da ita daga gidan,tace kuma zamanta yakare agidan,sai dai Hajiya binta ta bita wajen tabata kudin mota tace ta tafi malumfashi Abun yamata bakinciki,sosai datatafi malumfashi tadade wajen Dangin babanta kafin ta dawo,shima saboda Ammin nata ne,ammh daga Alhaji Abdulmalik din har Malika ba wanda ya nemeta,sai ma goyon bayanta da yayi lokacin da hajiya binta ke sanar dashi Abunda tayima jodan,tabe baki yayi yace tayi Daidai Domin tana da iko da gidan Ubanta,Shiyasa Tundaga lokacin ta kiyayi kanta da malika.

Iyakarta da malika sannu daga haka wata mgana batataba Shiga tsakaninsu ba,sai suyi kwanaki agidan ammh wlh ko zasu hadu sau goma ne ba wacce zatama wata mgana,ita malika tana ganin tafi karfin joda,saboda gidan mahaifinta take zaune,kuma take ci tasha tayi Sutura daga Dukiyar ubanta,to tana ganin tafi karfinta tsakaninta da ita kamar nisan kasa da sama, ne.

Itako Joda tana kiyayewa ne Tun Abunda yafaru Amminta tajamata kunni sosai kan Malika,shiyasa tafita harkarta in taga damane ta gaisheta randa bata ra”ayi kuma tayi kamar bata ganta ba.

CIGABAN LABARI

Washegari

Saleem Tun bayan da suka dawo sallar Asuba da Abbi da ya marwan bai yarda ya kara haduwa dakowa ba,ko masallacin ana sallame sallah yayi Wuf ya Fito,saboda kada ya marwan ya tareshi da wata mgana,don bai shirya amsama kowa tambayanshi ahalin yanzu ba,sai ya aiwatar da gudirinsa akan Malika

Yana dawowa ya Shirya domin komawa bakin aiki,ada yaso yabari sai gobe monday,ammh don gujema Fuskartar wasu barazanq mussaman ga Ya marwa da Ummi,shiyasa ya Shirya komawa batare da ya sanar da kowa ba.

Karfe 7:00am na Safe ya Fito daga Dakinsa yana sanye da Uniform dinsa,sai wayarsa da makullin motarsa,Falon Tsit babu motsin kowa sai Ashura mai goge  goge ce kadai afalon tana share share,sama sama ya amsa gaisuwanta ya nufi koridon da zai sadashi da dakin Hajiya babba,domin itace kadai hope dinshi ayanzu.

Koda ya Shiga dakin nata,tana zaune akan darduma tana laziminta na safe,domin a akidar hajiya in tayi sallar asuba bata tashi awajen sai  Rana ta Fito.

Tana jin sallamarsa ta dago tana kallonsa,saboda yadda uniform din suka amsheshi ko ita sai da yayi ma kwarjini sosai,mirmishi ya sakarmata kafin ya karisa gabanta ya zauna bayan ya cire takalmansa daga bakin kofar dakin,yana Fadin”Hajiya barkanmu da Safiya..?

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button