MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL

MALIKA MALIK COMPLETE HAUSA NOVEL BY Janafty

Afalo ta tarar da Momi zaune cikin yauki da Murna tace”Momi ya iso fa..”,Da kallo ta bita kafin ta mike tana Fadin”Masha Allah,ki mishi sannu da zuwa,Ammh don Allah ki natsu Kinji zahra..”,Tana yar dariya ta Rufe Fuska tana fadin”To momi..”Tafada tana wucewa zuwa kofar da zata sadata da haraban gidan.

Tundaga nesa ta hangeshi yana jingine jikin motarshi yana latsa wayarsa,takowa take gareshi cikin wani taku,kamar wata hawainiya,ammh duka idanuwanta na kanshi harta kariso gabanshi bai sani ba,sai da yaji wani Sihirtattacen kamshi ya dukeshi kana ya dago suka hada ido da ita,Ajiyar zuciya ya sauke ya maida wayarsa aljihu yake Fadin”,Madam sai yanzu,? bayan kingama shanyani awaje..?

Wani mirmishin dariya tayi tana kulle idanuwanta da tafukan hannunta take Fadin”,Am srry,Barka da zuwa jahar kano,koda mai kazo an Fika…”Dan mirmishin yake yayi yana binta da kallo afaikace kafin yace”Au! haba..?Ashema hakane..”Yafada cike da dan barkwanci,dariya tayi mai sauti kafin ta juya tana Fadin”,Yanzu dai duk ba wannan ba,mu shiga Daga ciki..”Bai yi gardama ya fara binta abaya ita ko jin kamar yana kallonta,sai yasa salon tafiyar da Nadira tagama koyamata duk sai ta rude ta fara hardewa kamar zata fadi.

Shiko Saleem idonshi kur akanta cikin mintina ya kare mata kallo,Mele baki yayi aranshi yana ayyana Malika ta Fita komai na cika amace,ammh kuma duk da hakan zai iya maneji,ammh Shegen rawan kanta ne ke bashi haushi,domin ta gwadamai har suka isa falon bakin ta nuna mai daya Daga ciikin kujerun Falon,ya samu waje ya zauna yana binta da kallo,ciki ta koma sai kuma chan ta dawao tazo ta zauna akasa suna kara gaisawa tana tambayanshi ya mutan gidan.

Basu jima ba sai ga Nadira da yar aikinsu sushigo da manyan Farantai shake da kololin abinci,daya kuma shake da jugs na Lemukan da suka hadamai,Nadira ta zauna suka gaisa sosai harda dan barkwaci yayi mata,kusan dai mutumin naku shima in yaso wasa toh babu wanda yakaishi iya barkwanci da Raha.

Fita tayi ta basu waje suka cigaba da hiransu,wanda duk rabin hiran Zahra keyi,shiko sai jefi jefi zaiyi dan dogon mgana,ammh daga gyada kai sai mirmishi in yazama Dole,ada bai yi niyyar cin komai ba,ammh zahra ta nuna bataji dadi ba harda hawayen karya tayimai,shiyasa yace ta sanyamai Sinasir,da miyar ganye,wanda yaji manshanu da naman Rago yaji kuma dayawa saboda Dama sinasir mutuminshi ne,shi da waina yana sonsu sosai.

Lemun kuma kunun ayan yasha sosai,sai zobon shima dai baisha da yawa ba,sun sha Fira har anan yake sanar da Zahra cewa Basu rabu Da malika ba,kamar yadda Duniya ta dauka,so yanzu hakama tana zamfara tare dashi ya sanar da ita  hakane saboda yana ganin kila yayi maneji da ita,Sanda ya sanar da ita taji ba dadi ammh soyayyarshi ta Rufemata ido,ta sanar dashi babu komai,ko da’ace Itace ta hudu tana sonshi ahaka kuma zata aureshi yaji dadin mganarta ya sanar da ita da zarar ya koma gida sai Tuntubi mahaifinshi yadda suka yanke zai sanar da ita ta waya,Ai murna kamar Zahra ta Shide,sai kace ance gobe ne bikin.

Sai After 4 kana yayi Shirin tafiya,bai Tafi ba sai da zahra ta shiga dashi babban Falon gidan ya gaisa da momi,wacce ta yaba dashi sosai Fiye da Tunaninta,domin bata zata cewa zaben na zahra ya Wuce tsara ba haka gashi kuma dan manyan gida ne,cikin Fara”a da kunyar Diyar Fari ta amahesu suka gaisa kafin yayi musu sallama Su Zahra da Nadira suka rakosa har wajen mota,suna karayin sallama kenan sukaji hon,megadi ya bude get,sai ga wata bakar motar BUGATTI,Ta sawo kai cikin gidan,kusa da motar Saleem aka faka motar kafin direban ya Fito da gudu ya bude bangaren baya Alkali bukar mada ya Fito yana gyara zaman babban Rigan jikinsa.

Zahra ce tace”La..Shikenan ma Nadira ga Abba nan..”Tafada cike da murna,shiko saleem gabanshi ne yafadi,gaakiya bai so sukayi arba ba,ganinsu tsaye yasa ya kariso yana kallon Saleem cike da mamaki,Tunkafin yayi mgana Saleem ya rankwafa yana gaisheshi,hannu ya bashi suka y musabaha yana kallon su Zahra tun kafin yayi mgana Nadira tayi karaf tace”Yauwa Abba gwara daka dawo,Saurayin Zahra ne yazo ACP SALEEM KABIR KUMO..”

Abbah yace”Masha Allah,..”Yana mirmishi yana kuma kallon Saleem,Zahra ko Fuska ta Rufe tana juyar dakai,Yar dariya Abbah yayi yana Fadin”Hakane..? to ku koma gida zan yi mgana dashi..”Nadira ce tace”To Abba ashigo lafiya..”tafada tana jan hannun Zahra wacce ke dagama Saleem hannu afakaice,sai da suka shige kana Abbah ya dawo da kallonsa kan Saleem yana Fadin”Sannu da zuwa..”Kan Saleem na kasa yace”Yauwa Abba,mun sameku lafiya..”Ya karba da lafiya lau.,daga ina kake,ma”ana waye mahaifinka..”

Bai yi gardama ba ya Sanar dashi sunan mahaifinshi,cikin jin dadi Abba yace”Masha Allah,tafiya tazo da sauki,ai Mahaifinka ba boyayye Bane,ikon Allah,munsan juna chan abaya gaskiya,kodai mene zan tabosa ta waya insha Allahu..”Yafada yana bayyana murnansa Afili,Saleem yayi kasake yana jin Bukar mada na Shirin ballo masa ruwa,Abbi da baisan da wata mgana ba,yanzu in ya samu lbrin mai zai ce mai..? Shiyasa har sukayi sallama ba cikin dalin rai ba,Wani karin fargaban ma,shi da kanshi ya umarceshi daya bashi nombar Abbi,kuma ya sakamai yana jin cewa yagama yawo,Abunda yafi bashi tsoro shine har yana sanar dashi ya kwantar da hankalinsa kamar ya samu zahra yagama.

Har yakai zamfara yana Tunanin irin matakin da Abbi zai dauka akanshi in yaji lbrin yana neman wani auren batare da saninshi ba,bai shiga gida ba sai da ya biya yyima Malika takeway,koda ya koma gidan bayan sallar mangari ne,Ta idar da sallah kenan ya Shigo,bai jira ma tayi mgana ba,bayan amsa sallaman datayi ya ijiyemata lodojin daya Shigo dasu ya Fice zuwa dakinsa yana jin jikinsa agajiye kamar wanda akayima mugun Duka,yana shiga dakinsa ya Tube ya Fada wanka yana jin Barci yana Lumshe mai Ido.

Abunda Saleem yake gudu shi ya Faru,don bayan dawowarshi gidansu Zahra da kwana biyu yana office da rana tsaka ya samu kiran Abbi,wanda sai da gabanshi ya Fadi,ya daga yana mai sallama Abbi sai ya karba sallaman kafin ya zarce da Fadin”Ashe kuma aure kake nema bamu da lbri…?”Wani yam yaji,kunya da tsoro duk sun kamashi,Sosa kai yafarayi kafin yace”Injiwa Abbi..”? Ya dakatar dashi da Fadin”Inji uban yarinya,jiya da yammah Tsohon Alkalin Alkalai ya kirani Bukar mada,ya sanar dani cewa kun ma daidaita kanku kaida yar wajensa,daga karshe ya jadaddamain ya baka Auren yarshi Duniya da lahira..”

Wani zufane ke ketomai ko tako”ina Dakyar ya samu zarafin Cewa”Tsaya kaji Abbi,wlh sau daya na…”Yimin Shuru mallam ba wannan na Tambayeka tunda kanunama Duniya bamu da daraja awajenka Saleem ai Shikenan,da ka boyemana ni ko Aisha akwai wanda ya isa ya hana ka kara aure ne? wlh babu saboda haka na kira ne na sanar dakai Sati mai kamaawa zan kira kumo,Baffa zai zo mu tafi kano ane ma maka aurenta…”Daga haka ya yanke kiran.

Tsaye saleem ya mike yana Goya hannunshi abaya,gashi da Abunda ke ranshi ne,kuma wanda yake bukata Abbi ya sanar dashi,ammh yaki farinciki baisan dalili ba,baya Farinciki da Auren Zahra kwata kwata arayuwarshi ga kuma Abbi ya dau Fushi dashi,ganin bashi da mafita ne ya kwashi rawan jikin kira ya marwan yana sanar dashi Abunda ke Faruwa,baki ya rike yana Mamakin me Saleem zai zama age dinshi yaron da ko 30 bai gama cikawa ba,Har zai ijiye mata biyu da ya jefamai tambayan ina zai kai mata biyu..? Kasa bashi amsa yayi don bazai iya sanar dashi rataye Malika yayi ba Shiyasa yake son kara aure,shidai rokon shi daya Ya kira Abbi da Ummi yabasu hakuri ya sanar dasu abunda yafaru,ganin ya damu ne shiyasa ya lallasheshi da cewa yanzu zai kira Abbin suyi mgana.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button