NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

Kamkameta mu”azzam yayi yana fadin”Allah sarki kowani bawa danasa kaddaran sai yanzu nagano dalilin Sakin da Ummi tasa nayi miki,dakuma dalilin Aurensa da kikayi,Bakomai my hirah,kamar yadda ya sadaukarmin da Abunda yafi daraja awajena,nikuma nayi masa alqawarin basa abu mafi Soyuwa agaresa”Da Sauri Zahirah ta kallesa kan tace”mezaka bashi..”mirmishi yayi kafin yace”Sai lokaci yayi zaki gani..”jin haka yasa bata kara mgana ba ta rabu dashi ammh aranta tana Tunanin meye wanan Abun Shikuwa da ya mu”azzam keson bama Alhaji wanda zai zama mafi soyu agaresa,ganin bata da wannan amsan yasata ta share zencen.

  Dakyar ta lallabasa tayi mai wanka ta shiryasa cikin wata gezner Brown colour ta sanyamai Hula ta fesamai Turare,duk da komai take karfin hali ne,domin ta karfafamai Gwiwan yin adalci Atsakaninsu,koda ta riko hannunsa suka fito falo babu kowa Ummi tana samanta Lubna na dakinta,wajen Ummi tafara kaisa tana cema Ummi”Kisamai albarka Ummi,zan rakasa dakin Amarya..”Washe baki Ummi tanayi Tana fadin”Kai masha Allahu diyata,kin ko kyauta,to kai Ciroki haka ake zuwa dakin amarya babu ledan yar kaza..”tafada da zigan zolaya bata fuska yayi kafin yace”Kai Ummi yanzu nine cirokin..? yafada harda wani buga kafa,mikewa tayi ta isa garesa lokaci daya ta riko hannunsa tana fadin”Wane ni,Bakai bane Son,maza kutafi kar Lubna tagaji da jira,ngd Sosai Diyata..”tafada tana kallon Zahirah mirmishi kawai zahirah tayi kafin tace”Bakomai Ummi Yiwa kai ne”Turo baki mu”azzam yayi kafin yace”Ni Ummi bazaki man godiya ba,sai ita kadai.”dakuwa Ummi tamai kafin tace”kaga nakanan,ka wuce ku tafi dare nayi..”Bata fuska yayi kafin yawuce yana fadin “Shikenan Ummi Tunda yau dai korata kikeyi.”ficewa yayi zahirah tabi bayanshi tana mai dariya yana kallonta ammh yamata banza yawani hade rai,har cikin bedroom din Lubna tarakasa ,sun isketa ita dasu little sunata mata kiriniya tana biye musu tana ganinsu tashiga musu sannu da zuwa cikin mamaki.

  Shi daga bakin kofar bedroom din ya coge hannunsa duka ya rumgume akirjinsa,itace ta karisa har bakin gadon tana fadin”Sai kika ganmu da ango ko? Dariya Lubna tayi kan tace”Wai ango..”cikin zolaya,zama zahirah tayi gefenta tana fadin”da gaske angonki na kawo miki,yau adakinki zai kwana sai yayi bakwai..”Rike baki lubna tayi kan tace”Haba Anty bana aza sai yayi sati akungi ba”Zahirah tace”A”a ko a al”ada kwana uku zanyi tunda ba budurwa bace ni,kedai zaki kwana bakwai”Sadda kai Lubna tayi zatayi mgana Zahirah tace”Karki ce komai,ki kula dashi kawai..”

Gyada kai tayi tana dan mirmishi,Mu”azzam dake coge yace”kai wai tsaya naga kowacce  naneman kai dani ne..”yafada yana kuresu da ido,saurin  mikewa zahirah tayi tana fadin”Wanemu muneni kai da maigidan kan gida guda,sha zamanka dan lelen amarya,bari na dauki Su little kada su takuraku..”tafada tana daukan moodu bayan Ta riko hannun Ummi take fadin”Kanwata asha amarci lafiya..”Tafada sanda ta karisa kusa da mu”azzam,cemasa tayi”Ango asha amarci lafiya,ammh abinmun kanwata a hankali don Allah…”Rankwashi ya sakarmata bisa kai yana fadin”Allah kin rainani yarinyarnan..”Dafe kai zahirah tayi tana fadin”Wash.kafasamin Kokon kai,daga Abun arziki sai kuma kaci zalina..”bai mata mgana ya damki hannunta yana fadin”Zo ki wuce bani son Taimakon..”Tana dariya ya turata waje ya rufe kofan,kofan tabi da kallo tana yar dariya domin tasan ta kunno mutumin nata,Dakinta takoma dasu little tayi musu wanka,itama tayi,koda Abun yanaso yadameta sai tayi Sauri ta kaunda Tunanin haka,dataga shedan yana mata hudubarsa sai ta lallaba su Moodu,sukayi barci Kafin tafada tiolet ta dauro alwala tazo tayi nafila,bayan tagama ta dora da karatu alqur”ani har wajen biyu na dare kafin ta kwanta,nan da nan Barci mai Nauyi ya kwasheta.

  Abangaren Lubna kuwa koda zahirah Tafice tana gefen gado takasa tashi,Kanta na duke tana wasa da zoben hannunta,mu”azzam na gefen yana binta da kallo,kafin ya karisa shigowa dakin yana fadin”kiyo alwala..”yafada yana kariswa kusa da sallayar dake Shimfide achan gefe,Tashi tayi jiki asanyaye ta fada Tiolet,koda bata dade da wanka ba,sai da ta sake yi,koda ta fito yana tsaye yana jiranta,hijabi kadai ta sanya tazo tabishi sukayi sallar raka”a hudu sai addu”o”in dasuka biyo baya,koda suka kammallah bai mata mgana ba,illa mikewa dayayi ya isa kan gado ya kwanta bayan ya rigar jikinsa ya bari daga shi sai dogon wando da farar Singelet,Itako ganin baimata mgana ba yasata zama awajen har na tsawon wani lokaci sai da tagaji da kanta ta mike ta isa ga wardrope ta dauko Rigar barcinta wata pick ce mai budewa tagaba,ta sanya hijabinta takara sawa kafin tazo ta raba gefensa ta kwanta jikinta na rawa,shiko yana kallon ta duk Abunda takeyi,Lumshe ido yayi kamar mai barci bayan ya juyamata baya,ganin yadda ya juyamata bayane Zuciyarta tayi Rauni batasan sadda ta fashe da kuka ba,ganin yadda take kuka haryana Fitowa,yanajinta ganin takiyin Shuru ne yasashi Saurin juyowa ya mirgino yafado jikinta yana riketa yace”Wht do u wht Lubna..? yafada yana Rikota jikinsa,jinta ajikinsa yasata kara tsananta kukan ta,rumgumeta yayi kamkam yana fadin”am Srry plz if wht i did hurt u.Ba laifi na bane..”yafada yana Shafa kanta har zuwa bayanta alaman lallashin ganin taki daina kukan ne,yasa ya dago kanta yana sharemata hawaye lokaci daya ya zura harshensa cikin bakinta yafara bata wani Sumba mai wuyar ganewa,Tuni Lubna tanemi kuka Ta rasa,dole zuciyarta da gangan jiknta ya saki tare da karban sakon da mu”azzam ke bata,kan kace kwabo Mu”azzam ya rikita Lubna da salonsa,yakuma rabata da rigar barcin dake jikinta yana mata wani tafiyan Tsutsa ako”ina na jikinta,Yadade yana wasa da gangar jikinta kafin yanemi hanya,tanaji yana karanta addu”ar saduwa da iyali kafin ya nemi shiga,sai lokacin lubna tayi kokarin dakatar dashi,ammh ina ta makaro domin bakinsa yasa ya toshe mata baki,ya dau hanya daga Shi sai mai Tsaron gida,lokacin daya samu nasaran Shiga da karfinsa tuni lubna ta kamkamesa hawayen azaba na zubomata bata yadda zatayi illah kukan zucci domin mu”azzam kam yayi nisa bayajin kira.

Washegari kuwa dakansa ya taimakamata tayi wanka tare da wankan Tsarki,Albarka ko tashashi gun mu”azzam ya tarairayeta sosai wanda sai da yasa Lubna yin kwallah,bata taba tsammanin Rana mai kama data ranar zatazo ba,sai gashi tana kwance kan kirjin mu”azzam yana Rumgume da ita yana lallashinta meya jawomata hakan, BUDURCI koda bayasonta taci Darajar Mutumcinta data tattala har ta kawomai gashi yabata wani mtsayi wanda bata taba zato ba.

  Koda suka fito da Rana zahirah bata nuna musu wani abu ko Afuska ba,Saima Tashi datayi Ta rumgume Lubna tana fadin”Sannu da Fitowa kanwata..”Harara mu”azzam ya sakarmata yana fadin”Son kai,kanwarki kadai kika gani baki ga mijinki ba ko? Kallonsa tayi kafin ta murgudamai baki tace”eh din ni kanwata nagani banga wani miji ba..”cije baki yayi kafin yace”Zan kamaki ne zakiyi bayani..”yafada yana daukan Little Ummi,moodu ma ya matso duka ya hada ya dauka ya fice dauke dasu,zuwa dakin Ummi suka gaisa tana sakamai albarka,dadi kamae ya kashe Ummi tana kara godema Allah da yasota da idon Rahama tagane Kuskuren datayi,lokaci bai kuremata ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button