NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

  Da baya Zahirah Tadawo tana kallon Yagana kafin tace”Kai ammah naji dadi,ni wlh kin ma taimakeni,domin ko azamin jahiliya banyi kama da kalar wacce zatayi zaman kishi dake ba,nagde miki sosai bisa asirin dakikayi Alhaji ya sakeni dama burina kenan,kinsan Allah aiki yayi kyau,da badon bani na bada aikin nan ba,ai da nabaki kudi kin kara ma mallam din.”tafada tana zagbamata harara kafin tayi tsaki tawuce abunta,Da kallon mamaki Yagana tabi zahirah aranta tana fadin dama tana mgana,kada kai tayi tana fadin”koma miye daga baya kenan,aje dai gaba,abi wani Sarkin..”

   Tana Zuwa tasanya Dayan akwatin abooth Bukar ya rufe booth tazagaya ta shiga gaba tana kallon Zulai tace”To Zulai nagd Allah kaddara saduwa..”zulai takasa mgana sai kwallah,Bukar ya tada mota suka fara tafiya kafin lokaci daya zahirah taji kwallah na ziraronata tasa hannu ta share kafin tadagama Zulai hannu wacce ke dagamata itama tana share kwallah.

  Sai da Suka dau hanya kana Zahirah tadago tana fadin”ina kwana bahna..”kallonta yayi kafin yace”lafiya kalau yahna,kiyi hakuri da jarabawar Ubangiji Abunda Allah ya tsarama bawa bai isa ya kaucemasa ba”yafada cikin tsausayi da soyayyar mai dorewa,moodu ne dake kan cinyarsa yafara kuka,sai ta sanya hannu ta daukeshi tadorasa kan jikinta tana share kwallah tace”A iya tarbiyan daka bani bahna,ka gayamin cewa kaddara da jarabawa Musulmin kwarai ake yawan jarabta dasu,ko ahaka na tsaya zan godema Allah,domin yamin ni”ima,ta haihuwa ya”ya har biyu,ko banjin dadin zaman Aure ba,ina fata agaba in Sun tashi sunji lbrina suji kaina bahna..”tafada tana zubar kwallah

   Hawayen Farinciki,ya kwaranyoma bahna bai damu da sharewa ba yace”Hakika ke ya”ce mafi soyuwa awajena,Kankatar shekarunkin sunyi kadan da hangen nesanki,Ina rokon Allah ya cigaba dayima rayuwarki albarka tundaga yanzu har karshen Rayuwarki,kuma inaji ajikina Lokacin Farincikinki damu kanmu yazo,Allah yayi miki albarka”Zahirah na mirmishi tana sharan kwallah take amawa da Amin,haka dai yayi ta mata nasiha har suka iso,sai da mahgana taga zahirah kwatsam Bukar na shigowa da akwatuna tsalle tadaka ta rumgumeta lokaci daya tana sakin guda.

  Da kallon mamaki Bahna ya bita kafin yace”ke miye haka,mutuwar auren kikema guda..”dariya mahgana tayi kafin tace”eh wlh,Allah ya rabata da wannan kaddaran gidan,da bakar kishiya mai bakar aniya,sai taci kanta..”da mamaki Bukar yace”To in kina murna ta rabu da nan din,gaba kinsan inda zata”mahgana tace tana riko hannun Zahirah”Ai ba bakon waje bane,Mu”azzamu ne Uban ya”yanta kuma na tabbata kasan abunda yake jira kenan,Ai mu kan muna murna da wannan Sakin..”

Zama bukar yayi yana fadin”Hmm,mata mata Sha”aninku sai dai abarku,yanzu shi Sakin Auren ne,kuke ma murna,kun manta Allah da kanshi ya halarta saki,ammh in akayi sai al”arshin Allah ya girgiza ammh ke dadi kikeji”Yafada yana kallonta,Mahgana tace”hakane ammh wannan Sakin dabam ne..”

    zahirah dake gefe ta tura baki tace”Ni fa mahgana babu inda zan koma,Ai ya mu”azzam din yayi aure ya manta dani saboda haka,nima bazan koma ba,Zama zanyi agida na kula da ya”yana..”Tafada tana wani zakuda kafada,baki mahgana ta saki kafin tace”Allah,karya kikye yarinya bazaki iya rayuwa babu Mu”azzam ba,kamar yadda shima bazai iya rayuwa baki ba..”

  Mahgana Tabude baki zata karayin mgana,Bukar ya dagamata hannu da fadin”plz mahgana kirabu da ita haka,taje ta tayi wanka,tayima yaran,kibata abinci taji takwanta ta huta,nayi alqawarin bazan kara takuramata ba,abunda ta zaba shi zan bi,koda kuwa na zama har abada ne batayi Aure ba.”Da kallo mahgana tabishi na mamaki,dole tayi Shuru ta bakinta saboda yadda bukar ya kauda kai itako Zahirah Dakinta ta fada dauke da little Ummi,moodu na hannunta,dukkansu babu wanda yakara bi takan Mahgana balle maganarta,itama dole ta fice zuwa kichen Ammh matakin da bukar keson Dauka bamai bullewa bane.

Srry ooo..,Ba yawa,yau dinma, don Typing din na amarsune shiyasa kuka Samu,via wit me Janaf Freeking Fans Luvs u Wujiga wujiga????Lodi lodi????mazga mazga????Bhahoot Bhahoot ya Habibaties

Comment,share and vote

       Janafty
UWAR MIJINA…!
(Soyayyah,Sadaukarwa,hakuri tare da biyayyah mai tsanani)

       Mallakar:JANAF
       Wattpad:Janafnancy12

Dedicated to my blood Sisters JANAF

GIFT TO:Hussain80k

Intelligent writer’s Asso

Dis Page iz Dedicated To u my MOMMA..,HAUWA S ZARIA(mmn Uswan)My mommah Ina matukar Kaunarki har cikin Raina,Zuciyata tana dabbaka alherinki,bakina baya gazawa wajen ambatan kirkin ki,Idanunawa Suna darajaki,gangar jikina tana matukar girmamaki Mommah,Allah nake roko Ya iya miki Abunda kika gaza,bayan ya dafa miki gaba da baya,Ya Allah ya raya miki Zuru”a cikin Tafarkin Addinin musulunci ya karemin ke daga Sharrin mahassada da makiya,Allah yayima Rayauwarki Albarka datamu gabadaya Ameen…,UR DOTA LUVS U MORE MORE UWA TAGARI????????✌????

NOT EDITED????

                  NO 42

    “”Mahgana Abunda zahirah tace da yadda mahaifinta ya goyamata baya,ya tsayamata arai,dakanta ta zuboma Zahirah abinci taje ta dibo Ruwan zafi tazo tayi masu little wanka,zahirah sai dataci takoshi kana tayi wanka tabi lafiyan gado tana barcin data dade batayi Irinshi ba,moodu ne yayi barci,little ko tana hannu Ummi afalo,bukar kuwa tuni yayi wanka ya fice Abunsa.

     Mahgana ita takira yakura tana fadamata Abunda zahirah tace,kuma ga yadda bukar yace”Mirmishin gefen baki yakura tayi kafin tace”Ah wasa takeyi mahgana,Zahirah ce tace da bakinta bata komawa gidan mu”azzam din?mahgana Tace”Wlh kuwa,wai ai shima yayi Aurensa ya manta da ita,kuma inajin Tsoron bukar,kan kafiya,in yace eh to hakane bamai sashi ya chanza ra”ayi”tsaki yakura tayi kafin tace”Duk wasa suke,ita zahirah kishi ne ke damunta Shikuma bukar abunda ya Faru ne,yasa bayason kara mata dole,kimanta dasu don Allah,tadai gama iddar tukunnah”dahaka suka rabu da yakura,koda zahirah tatashi daga barci mahgana bata kara mata mgna,Ko bukar din daya dawo,batakara tadamai mganar ba,tabi Shawaran yakura,ta kyalesu har Zahirah tagama iddah,komai ke akwao ayi daga baya.


BAYAN KWANA BIYU
    

      “”””Mu”azzam cikin kwanakin jiyake,kamar yayi Tsuntsuwa daga Abuja zuwa maduguri,kullum ya kwanta barci mafarkin Zahirah yake da yaransa,ammh haryanzu Ummi batace komai ba,gaskiya ya gaji yau Tun safe yayima Ummi dirar makiya adakinta ko Tashi batayi ba,Tana cikin bedroom dinta akwance,ya shigo,mikewa zaune tayi tana yaye blanket dinta,lokaci daya take fadin”Son,wht happen naganka ealry in d mrning haka? Kariswa yayi kusa da ita yayi yana hawa bisa cinyarta ya yada kansa yana fadin!”Haba Ummi ,yanzu shikenan sai kiyi banza dani,tun yaushe akayi sakin nan,ammh haryanzu baki kara cemin komai ba..”yafada yana lumshe ido.

    Hannu tasanya bisa kansa tana shafawa lokaci daya tana murmusawa kafin tace”Ho,Son kana da rigima Wlh,bana ce kayi hakuri muji ta bakin mahaifinta ba,kuma ko zata dawo gareka basai tagama idda ba,kuma kana sane da Sai ankara daura Muku aure,so Sauri bana ka bane,kaji son..”Tafada tana kai hannunta kan Fuskarsa tana shafawa,runtse ido yayi kafin ya riko hannunta yana fadin”i know Umm,buh i want to see her,Wlh in banganta ba yadda zuciyata keyi mutuwa zanyi..”ido Ummi ta zaro kafin tace,”Mutuwa Son..? tafada cikin Tsoro.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button