NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

  Tana zaune akan gado tana bawa Maccen nono,sanye take da riga da zani na wata holland mai ruwan ganye,kanta na kasa tana kallon yarinyar yadda ta bude ido tana kallonta,Namijin ko na gefenta shima yana wutsil wutsil yanaso yayi kuka,su hajiya sukayi sallama suka shigo maghna ne agaba,kana hajiya da Shureim dake take mata baya.  

   Da mamaki zahirah ke amsa sallaman hannuta abaki tana fadin”La..Hajiya, yaya Shuriem..”Tafada tana bayyana mamakinta lokaci daya tana cireta anono bayan ta maida rigarta karisowa sukayi lokaci daya hajiya tana zama kusa da ita tana fadin”Allah sarki diyan nan baki yi Fushi damu ba ko.?.”tafada tana daukan maccen dake jikinta ta mikama shureim itakuma ta dauko Namijin tana fadin”Allah sarki Allah kenan mai yadda yaso alokacin daya so…”Tafada lokaci daya tsausayin zahirah da yaran ya dabaibayeta harda na mu”azzam din shikanshi.
   

Sunkuyar dakai zahirah tayi tana wasa da kwalliyar rigarta batayi mgana ba ammh idanunta sun cika kwallah,kallonta shureim yayi yana fadin”ya jikin ki..”? yafada cikin kulawa kanta na duke tace”naji sauki,kunzo lafiya” ya amsa mata da lafiya kalau,hajiya ce keta kallon ya”yan tana fadin”Suhaima kin zalunci kanki,kin kori ni”imar ubangiji daga gidanki,ina zaki kai hakkin yaran nan,ki rabasu da ubansu gashi sunzo duniya ammh bai samu ganinsu ba..”take ta fada tana share kwallah kan ta kalli zahirah tana fadin’yan”nan kiyimana aikin gafara don Allah,wlh banda masaniyar aikin da suhaima ta aikata gareki,harga Allah tamkar mu”azzam haka na daukeki,Allah yabaku ikon cinye jarabawanku,yakuma baku juriya da hakuri…”tafada tana dafa kanta.

  Wasu hawaye masu zafi suka zuboma zahirah tayi saurin gogewa ammh ina wasu nema suka kara bulbulowa tana so tayi mgana ammh takasa saboda yadda ranta yake mata daci ,in ta tuna da tarabu da mu”azzam rabuwa na har abada,kuka ne ya kwacemata ta kife kanta tana rerawa,kuka mai ban tsausayi ga wanda yake saurare,mikewa hajiya tayi ta fice dauke  da yarinyar tana hawaye dominn tsausayin zahirah bazai barta tacigaba da zama ba,shureum dake tsaye ya kalleta yana fadin”Sai hakuri ,shima din yana chan cikin halin ciwon tun bayan barinki,yanzu haka yana kwance a asibiti tun jiya..”

  Da hanzari ta dago idanunta jawur tace”Yana asibiti kuma..”? tafada cikin tashin hankali gyadamata kai shuriem yayi yana fadin”shiyasa bai samu zuwa ba,saboda abunda ummi tayi yasa ya samu hrtfailure..”hawaye suka gangaroma zahirah tace”Don Allah kakira minshi awaya,nima wlh ban kara kwanciyar hankali ba,tun bayan tahota,kowani dakika yana raina,wlh ya shureim bazan iya rayuwa babu ya mu”azzam ba,ganagar jikina ce kenan maiduguri ammh Ruhina da zuciyata suna Abuja wajen ya mu”azzam..”Tafada tana fashewa da kuka.

   Shureim dake tsaye saboda tsausayin masoyan biyu sai da yaji kwallah ta tarun mai, “Don Allah kakira minshi ka taimakeni indai kanaso hankali na ya kwanta..”Tafada cikin wani yanayi ganin yadda take kuka ne yashashi cemata”is ok stop craying share hawayenki bari na kira wayar Dr.Yakai masa don babu waya atare dashi..”jin hakane yasata sauke ajiyar zuciya tana share hawaye.

mikamata yaron yayi yana fito da waya lokaci daya ya lalubo Dr.Abuduljabar bugu daya ana biyu ya dauka,bayan sun gaisa yanemi alfarman sonyi magana da Mu”azzam,sai da Dr.Abduljabar yayi shuru kafin yace’Ok..ya dates kiran,minti biyar shureim ya bashi ya sake kira sai ga mu”azzam yadauka murya shake yana fadin”Dan”uwa kun isa ne..? yafada cikin halin ciwo

  Gyada masa kai yayi kamar yana ganinsa yace”eh tun dazu gani ga twis wlh so fine dasu dan”uwa sai ka gansu ma..”rau rau mu”azzam yayi kafin yace”da gaske..? wlh Kuwa,zan dauko ma hotonsu macen wlh yadda kasan photocopyn ummi ce..”Wani yarr mu”azzam yaji kafin yace”Allah na godemaka,ina mamansu..”yafada gabansa na fadi,shuriem yace”Gata nan,itama ta matsa sai an kira mata kai,ammh plz dan”uwa try to be a gentle man kadai san Condtion din dakake ciki ko..”?Nasani..”yabashi amsa muryansa cikin karaya.

    Mikata yayi wanda dama tuni ta zaku ji take kamar ta fizge wayan tana karba ta saka akunni lokaci daya tace” Ya mu”azzammmmm….”Tafada cikin karyewan murya kafin kuma kawai ta sanyamai,kuka shuriem dake gefe yayi saurin ficewa saboda bazai jure ganin wannan masoyan ba masu neman mutuwa kan juna.

   Mu”azzam dake kwance wani yanayi yaji yana shiganshi muryan hiransa dabam take acikin mata,ko cikin dubu ta fita dabam,kwallah ta tarunmai a ido yana so yayi mgana yace ta bar kuka ammh yakasa saboda kowani dakika kukanta cinmai rai yakeyi gani takiyin shuru yasa yayi karfin halin cewa..”Zan kashe wayar indai bazaki daina min kuka ba..”yafada muryansa tafara hardewa shima kukan yakeson yi.
  

  Jin muryansa cikin halin ciwo yasa ta danne kukanta takoma tana ajiyar zuciya dan mirmishi yayi kafin yace”maman Twins..”yafada cikin kasala tura baki tayi kamar yana ganinta tace”Ni ba wannan ba ya jikinka..”? rausayar dakai yayi yana fadin”Ni lafiyata kalau,wayace miki banda lafiya.”yafada cikin dauriya.

  “Ya shureim yanzu yace kana ma asibiti tun jiya..”Girgizamata kai yayi yana fadin”Ba gaskiya ne,ni ina gida abuna..”rausayar dakai tayi tana sharan kwallah tace”mezaka boyemin ya mu”azzam? wlh tallahi halin daka ke ciki shi nake ciki,zuciyata tana zafi duk sadda na tuna mun rabu kenan,..”Tafada tana kara sakamai kuka.

   Runtse ido yayi jkinsa na rawa yace”yi shuru Hirata bamu rabu ba,kuma bazamu taba rabuwa ba har abada..”yafada hawaye na gangaromai kafin yacigaba da cewa”basan haka zuciyata ta kamu ta mtsanancin sonki ba hirata,sai da kika barni bansan haka jikina ya shaku da jikinki ba,sai da kika barni,wlh tallahi rayuwata bata da wani amfani matukar baki cikin zahiri na,Baki ganni ba na lalace akanki wlh ummi batasani bane takusa rasaniii….”Yafada muryansa na fitar da amon kuka,zahirah ma kuka take tana fadin”ni wlh bazan yarda arabamu ba, kazo ka daukeni mu gudu muje mucigaba da zamanmu..”Tafada cikin kuka.

Abunda tafada din ya bashi dariya har saida ya murmusa yana fadin “Zanzo hirata insha Allahu kidaina kuka kinji,share hawayenki matar mu”azzam..”yafada cikin sigar lallashi,tura baki tayi kan tace”to shima mijin zahirah yadaina kuka..”tafada cikin shagwaba har sai da tsigar jikinsa ya tashi,da sauri yacemata “Na bari Allah hirata..'”Yafada yana goge hawayensa.

   Gefe tayi dakai Tana fadin”Don Allah kabar damuwa,saboda kaga baka da lafiya kaji,kayi ka warke kazo kaga kyautar da Allah yayi maka..”Lumshe ido yayi ya bude yana fadin”Toh zan daina ammh sai kema kin min alqawarin zaki cire damuwa aranki,kikular da min yarana lafiya..”hawayen idonta ta share tana fadin'”Na maka alqawari yaya..”tafada da son tabbatarwa.
 

  Namijin dake hannunta ne yashiga tsandara kuka mu”azzam na jinsa,tuni jikinsa ya sake mutuwa,kirjinsa na wani zafi cikin karfin hali yace”Ki daukesa mana..”tace”ai yana ma hannuna ne fa yaya,kawai rigimarsace ta motsa,yafi,macen rigima fa..”dafe kai mu”azzam yayi dayake neman rabemai gida biyu yace”Ki bashi abincisa malama,yunwa yakeji shine zaki fake da rigimarsace tatashi ko..”Yafada da sigan zolaya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button