NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

Mikewa hajiya tayi tana fadin”Maza tashi Shureim bama zauna ba,tashi mudau hanya kada suce munyi banza,tunda ga yadda al”amarin yakasance mu sai muje muyi barka mukuma bada hakuri..”jin haka yasa mu”azzam dagowa yana fadin”nagode hajiya..,dan”uwa kafin ku tafi kace karime tashiga dakin hirah ta kwasan mata kayanta na sawa harda wayanta duk ta baku ku kaimata”Yafada wasu zafafan hawaye na zubomai,hannusa shureim ya riko yana fadin”karka damu dan”uwa anything will be alright kaji kacire damuwa aranka insha Allahu kamar kai da kanka ne kaje”yafada yana share masa hawaye gyada masa kai kawai yayi kafin ya runtse ido,ko takan Ummi basu bi ba, suka wuce,gun Dr.Abdujabar sukaje,suna magana da shureim,nan hajiya tace”maza ya tura Nurse taje tace Ummi ta fito saboda yana bukatar hutu,saboda wlh aka barta sai ta karisashi kafin su dawo,dariya kawai Dr,yamata kafin ya amsa mata da toh.

Aiko suna tafiya ya tura Nurse tayi waje da ummi wanda,daman suna fita ya mata barcin karya don yanaji tana ta kiran sunanshi yayi mata banza,kamar yayi barci,don shi yanzu babu abunda ummi zatayi ta burgesa,lokaci kawai yake jira ya aiwatar da kudirinsa,don babu yadda za”ayi ya iya rayuwa agarin da babu hiransa ba.

Saida,suka biya suka karbi duka kayanta,wanda karime ta hadamata akwati sai da ta cika harda ko wayanta aka hado da ita,suka damki hanya ushe ne ya tukasu,don shureim bai dogon Tuki,wajajen karfe daya suka damki hanya bayan sun biya wani shagon kayan yara shureim yayi barnar kudi,ya siya kayan sai da booth ya cika,dayake basu wani yi tsaye tsaye ba shidda na yammah sai gasu akofar gidan shettima wanda sai dai suka gansu kwatsam sun shigo,hajiyace kan gaba tana rafka sallama da yakura suka fara cin karo wacce tarike baki tana kallonta kan tace”Hajiya baraka..”

Tafada wit ful suprise Afuskarta.

My Sisi of Life AISHA ALTO,Jinjinarki ta dabamce sisina,wlh har cikin raina nake farincikin haduwata dake, masoyiyata,Allah ya cigaba da dafa miki,kamar yadda kike dafamin,tanque so very much ina yinki tawan over wlh

DON”T FORGET TO VOTE,COMMENT AND SHARE..It me Janafi
UWAR MIJINA…!
(Soyayyah,Sadaukarwa,hakuri tare da biyayyah mai tsanani)

       Mallakar:JANAF
       Wattpad:Janafnancy12

Dedicated to my blood Sisters JANAF

Intelligent writer’s Asso

Your limitation..Its only ur imagination
push urself,bcus no one else is going to do it for u..,Sometimes later becomes Never….Great things never come From comfort zones…
Dream it,…
Success doesn’t just find you…The harder you work for sometings The greater you’ll Find when you Achieve it.

NOT EDITED????

             NO 26

      
Itama hajiya cikin murna tace”yakura..”tafada tana mata mirmishi sauke hannu yakura tayi tana musu maraba ganinta ba ita kadai ba,daki suka shiga tana musu sannu da zuwa sheetima dake xaune gefe kan sallaya ya dago yana amsa sallamansu.

    Tabarma yakura ta shimfida musu kan kafet din dake tsakar dakin tana musu maraba,zama sukayi Shureim ne ya mikama baffa hannu sukayi musabaha,suna gaisawa kafin yajuya kan hajiya su shiga gaisawa gyara zama hajiya tayi tana fadin”Kunganmu da yammh ko..? yakura ta kadai kai tana fadin”ba abun  mamaki bane hajiya,ganin ai maiduguri ma gidace agunki..”tafada tana dan dariya.

  Mirmishi hajiya tayi tana fadin”kwarai kuwa,gidace agunmu balle yanzu da mukayi jikoki zuwa kam sai an gaji damu..”Tafada cikin murna yakura tace”aikam hajiya sabuwar amarya na nan na jiranki,dakuma sabon megida”tafada tana dariya cike da zolaya,dariya hajiya tayi tana fadin”Sai dai nayi maraba da sabon miji ammh banda sabuwar amarya kam..”dariya sukayi gabadaya hadda shettima.

  Ruwa Yakura ta kawomusu da lemo hajiya tasha ruwa kafin tagyara zama tana fadin”ina maijegon ne,banji kamshi kunun kanwar masu jego bane?..”yakura tace”Ayyah ai masu jego suna GRA mahaifinta tun washegarin haihuwar yazo yatafi da yarsa..”Tafada ranta babu dadi,kada kai hajiya tayi tana fadin”ikon Allah,to haka kuma akayi,sai hakuri shettima wlh ba laifin mu”azzam bane,yaron ma yana chan agadon asibiti rai ga hannun Allah..”,tafada tana share kwallah.

  “Ashhh….”shettima da yakura suka fada suna masu jimami kafin shettima yace”subhanallahi…,Allah ya bashi lafiya,bakomai hajiya nasan ba laifinsa bane,ni azatona Suhaima ta manta baya ta fuskanci gaba,ashe ita haryanzu bata manta da abunda ya faru ba..”yafada cikin karaya gyara zama hajiya tayi tana fadin”Shirme ne,kawai ammh ina amfanin mugun riko kamar ba musulma ba,wlh Shettima bani da lbrin abunda Suhaima ta aikata sam,bakaji yadda naji danaji lbri ba,don Allah kuyi hakuri haka Allah yaso..”

  Kada kai shettima yayi yana fadin”Babu komai hajiya kaddararce babu wanda ya isa ya gujema kaddaransa..Allah ya shigemana gaba..”da Amin suka amsa kan hajiya ta cigaba da bama yakura hakuri,shiko shettima yana jinsu bai kara cewa komai ba,saboda yadda abun ya dakesa lokaci daya,ga kuma ciwon da”akace mu”azzam yana fama dashi.

Basu wani jima ba,sallar mangariba kadai sukayi, yakura ta rakasu har gidansu zahirah,bukar na gidan yadawo yana falo yana cin abinci suka shigo,bawani sanin hajiya baraka yayi ba shureim dai ya gane,yakura ne tayimai bayani,am amshesu Fuskar dai bawani Annuri mussaman bukar,suna gama gaisawa hajiya ta zube kasa tana fadin”don Allah bukar kayi hakuri ka yafema yaron nan,ko daya kada ka kullacesa ba laifinsa ba,laifin mahaifiyarsa ne,da mugun rikonta yaron ma yana chan tunda abun ya faru bai kara lafiya ba..”Tafada tana matse hawaye.

    Jinjina kai bukar yayi kafin yace”Ban kullacesa ba hajiya ko kadan,kawai haushin danaji boyemin halin da yata takeci da yayi,ai ba A aure dole dai ya sakomin ita tadawo gida ba cemata akayi na gaji da ita ba,ko kuma bata da gata ba,kawai bazan iyama baffa musu bane,ammh harga Allah ni banso Aurar da diyata ma alokacin ba..”yafada cikin takaichi kafin ya cigaba da cewa”Banda ma jahilci meye ruwan zahirah da gabanta da baffa,inace mahaifiyarta ta rasu da dadewa,ammh ace shi bawa bai manta ba,saboda rashin imani tasaka asakomin y’a cikin dare bayan danta kuma ya dirkamata ciki,tsakani ga Allah hajiya anyi adalci,ko kene ya zakiji aranki in akama diyarki haka..”yafada ransa na kuna.

  Kada kai hajiya tayi tana fadin”bazan ji dadi ba ko kadan bukar,toxarcin ai yayi yawa,shiyasa nazo dakaina,in bada hakuri,wannan dan”uwansa ne ya wakilcesa tundashi yana chan baida lafiya,don Allah kuyi masa aikin gafara..”shuru bukar yayi kafin yace”Babu komai hajiya hakuri duka namu ne,Allah ya kyauta gaba ya’ce tasa ansakota kuma na karbi kayana,tana arba”in zan daura mata aure taje inda ake sonta dakuma darajata,danta kuma ta jika tasha..'”Yafada da son nuna abun bai damesa ba,hajiya dai hakuri tayi ta bashi shikuma yana cemata babu komai ammh yana yabamata mgana cikin mgana ga duk alamu dai an Tunzura bukar matuka.

    Maghana ya umarta data kai su dakin da zahirah take,shikuma shureim waje ya fita ya umarci Ushe daya shigo da kayan da sukazo dasu,haka ko akayi tuni yayi ta jidan kaya yana jibgewa afalo,kayane nagani na fada kamar za”a bude shago,bukar yana tambayan daga ina Shureim yace”Su suka zo dashi..”ada yaso yace su koma dashi ammh kuma girman hajiya yasa yayi shuru da bakinsa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button