NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

Dr Shureim na tsaka da duba patient kiran Dr.Abduljabar ya shigo wayarsa,har ga Allah yaji faduwan gaba sanda kiran ya shigo,cikin mutuwar jiki ya dauki kiran yana fadin”Dr,brk da safiya..”Cikin tashin hankali Dr.Abduljabar yace”Dr.Shurein akwai mtsala,komai kakeyi ka barshi kutaho yanzu kaida hajiya zuwa Abuja..”yafada cikin nuna damuwa,saurin mikewa yayi yana fadin”Subhannallahi Dr.Wani abu ya Faru? ko jikin dan”uwana ne ya kara tashi.?.”cikin wani yanayi Dr.Abduljabar yace”Komai ma ya rikice Dr.Mganar bazata yuyu ta waya ba,ammh ga Ummi an kawo asibiti ba yarda take,sannan ma”aikatan gidan suna fadamin wai brr,ya tafi ya bar Ummi shine sanadin shiganta halin datake Ciki..”Kadan ya rage Dr.Shureim bai fadi ba sakamakon Saurin dafe tebur din dake gabansa dayayi da hannu daya, zufa na ketomai ta ko”ina yake fadin”Allah gareka muke,kuma gareka zamu koma…”yafada lokaci daya yana datse wayan,yadafe kansa yayi yana ta kiran sunan Allah tuni idanunsa suka kada sukayi jawur cikin wata murya yake fadin”wayyo Ummi kin cucemu kin Cucu kanki,kin raba kanki da dan’ki da kanki,kin rabani da dan”uwa na,wanda tunda muka taso bamu taba rabuwa ba,koda da rana daya ba,kaichon ki Ummi,kaichonki Ummi..”yafada wasu zafafan hawaye na zuraromai,Cikin zafin nama ya tarrara kayansa ya fice domin patient din dayake dubawa tuni takama kanta tayi waje taga likita da kanshi na hawaye.

  Cikin wannan yanayin yajema hajiya zubemata kawai yayi yana kuka fadi yake”Shikenan Hajiya,Burin Ummi ya cika ta rabamu da mu”azzam” yafada yana fashe mata da kuka,iya rudewa Hajiya tayi rude,ganin kukan da Shureim yakeyi gakuma kalaman dayake fada cikin tashin hankali da Firgici tace”Badai Mu”azzam ya rasu bane Shureim..? girgizamata kai yayi kafin ya hau fadamata abunda Dr.Yagama fadamasa,hannu hajiya tadora akai tana kiran Sunan Allah kafin tace”Shikenan kurunkus kan kusa,Dama Abunda suhaima takeso kenan,kuma gashi ya faru,ohni baraka Allah kabamu ikon cinye wannan jarabawan na rayuwa dakake jarabtanmu..”Tafada kwallah na ziraromata.Shiko shureim kokarin kiran mu”azzam yake awaya ammh shima ana fadamai layin akashe yake,dafe kansa kawai yayi yana digan hawaye lokaci daya yanajn tsausayin mu”azzam yakamasa domin yafi kowa sanin waye mu”azzam Tunda yace yatafi to ya tafin ne,kuma sai Abunda Allah yayi.

  Duka gidan suka tarraro harda zulaika da yaran,suka nufo Abuja cikin tashin hankali wanda baya misaltuwa,Koda suka isa asibitin suka wuce direct,sun ma tarar da Ummi harta farfado tana ta wasu sambatu tana kiran sunan mu”azzam tana so asaketa ta fita,dole Alluran barci aka garkama mata,dole duk wani mai imani yaga halin da Ummi take ciki sai yayi mata kwallah,agabansu hajiya komai ya faru,hajiya waje takoma tana sharen kwallah tare da fadin”Allah mun godema ka,daga wannan sai wannan,ya Allah kabamu karfin kirjin daukan wannan al”amari..”Taketa fada tana kuka,zulaika ma hawaye take sharewa tana matukar tsausayama wannan ahali mussamman Hajiya da Ummi ga kuma mijinta wanda baya da wani wanda zai lallashesa.

 
Shikan Dr.Shureim daga office din Dr.Abduljabar mota yadauka Ya fice zuciyarsa na kuna,domin abayanin da likita yake masa Ummi tasamu tsoracewa ne da Firgici shiyasa take wannan zaburan kuma adokar matukar ta kara farkawa cikin wannan halin tofa sai dai ayi hakuri domin kwakwalwarta tasamu mtsala sai kuma abunda Allah yayi,yana tuki yana sharan kwallah,Maitama ya isa,yayi hon sani maigadi ya bude masa get ya sulala ciki,koda ya fito Fuskarsa babu Annuri yayi cikin gidan su lami ne da Uwani xaune afalo suna ganinsa suka mike suna mai Sannu da zuwa,da hannu ya amsa musu kafin ya Nufi farar takardan daya gani bisa center table din dake tsakar dakin domin ko da baisani ba itace silar komai

Warwareta yayi yafara karantawa kafin ya gama hawaye sun jika takardan,rumgume takardan yayi yana kuka,kafin ya dunkuleta ya sanyata cikin aljihun,dakin mu”azzam yafada,komai na nan a muhallinsa,makullayen gidajen dayace ya gani da kudin daya barma ummi,kana ga keys din motocinsa da Katin nan bankisa masu muhimmancu,wanda yake tara kudi masu yawa ya barmata,kenan da guda daya ya tafi,kuma yana kyautata zaton wanda ya tafi dashi bashi da yawan kudin da wa”inda ya barma Ummi kedasu,ya duba kayansa sunan ko kala daya bai dauka ba,banda takardun mkarantarsa dana aikinsa masu mihimmanci su kadai ya tafi dasu,saboda tsausayin Mu”azzam Shureim baisan sadda ya fada bisa gadonsa ba yana rumgume blanket dinsa yana shakan kamshin Turarensa yanajin wasu hawaye na kwararamai yake fadin”where are u dan”uwa? plz come back home we miss u so much dan”uwa..”yafada sanda ya saki kuka da muryansa saboda yadda zuciyarsa ta tsinke lokaci daya daya Tuna halin da mu”azzam din ke ciki.


Koda Flight dinsu mu”azzam ya saukesu a babban Filin jirgin dake birnin na ikkon tashar taxi ya dauka zuwa wani babban Hotel dake garin na lagos yakama daki yayi kwanciyarsa,kafin zuciyarsa tagama shawaran inda kuma ya nufa,shima kamar yaji ajikinsa haka ya zauna yana ta kuka,acikin briefcase dinsa ya bude ya Fito da hotuna guda biyar,guda daya Na Ummi ne wanda suka dauka tare dashi Saudiya tasaka jallabiya baka,shima bakar jallabiyan ne ajikinsa yayo harami da farin yadi akansa,yana rumgume da Ummi suna dariya hoton yayi bala”in kyau an saka shi cikin Frem anyi babbam elegement dinshi.
  

  Sai guda daya wanda suka dauka da Shuriem ne Abuja sanda aka yimsu brr calling,Suma dukkansu suna sanye da American Suit na kamfanin Armani ne,ammh shi mu”azzam yana sanye da rigansu na lauyoyi da hula sun,daki kadafan juna suna mirmishi,hoton shima anyi babban Elagement dinshi an sakashi cikin Frem,sai guda daya na Zahirah ce tana sanye da kayan mkrantarta complete harda da safa da takalmi da jakarta sabe abayanta,tana dariya aka dauketa hoton da alamu kamar ma batasan sadda akayi mata hoton ba,Gabadaya beauty Point dinta ya bayyana Fuskarta tana bayyanar da Farincikin datake ciki,hoton mu”azzam ya dauketa ne ranar da zata fara zuwa mkranta.

Sai guda biyun kuma na ya”yansane wanda Shureim,yadauko masa su  ahoto ya kawo mai yagani shine ya turasu duka awayarsa yasaka aka wankemai su kowanne an mai babban kati anyi elagement dinsu cikin Frem,wanda suke sanye cikin kayan sanyi na alfarma fuskarsu tar suna fitar da Annurinsu na jariran dake cikin kwanciyar hankali da Ni”imar ubangiji,duka yahada hotunan ya kamkame yana wani kuka mai cinrai,tuni saitin zuciyarsa ya fara zafi,yana tangadi ya tashi ya bude fridge din dake dakin ya dauko ruwa yazo ya zubo da magungunansa dayazo dashi ya hausha cikin rashin hayyaci da kewar wanda sukama mutum nisa.

  Allah ya taimakama farkawan da Ummi tayi ta farka cikin hankalinta,tadaina fizge fizge takoma yin kuka,mai cinrai kamar ranta zai fita,shigowar hajiya shiya kara  tsinkema Ummi jiki tana so tatashi takasa cikin sauri Hajiya takarisa gareta tana fadin”Bari kokarin Tashi Suhaima,baki da lafiya..”Tafada tana kallonta yadda tadawo cikin wuni daya kawai,cikin kuka da wani irin tsoro Ummi ta kamkame hannun hajiya tana fadin”Hajiya mu”azzam yana gunku ko? tare dashi ma kukazo yanzu ko? don Allah karki ce da gaske ne mu”azzam yatafi ya barni don Allah karki cemin dagaskene,duk abunda ya faru..”Tafada cikin shidewar Numfashi cikin hawaye Hajiya tace”Da gaske ne Suhaima mu”azzam ya zabi yayi nisa damu saboda hallayanki da taurin kanki,dakuma rashin yafiyarki,abunda nayi ta guje miki kenan,nafada miki suhaima inbaki zubar da makamanki ba,to watarana ma Da’n naki dakike takama dashi zai zo ya kubcemiki,kika kiji,yanzu waya gari ya waya,kifadamin tsakanin keda Da shettima waye ya fadi,kuma waye keda riba..”Tafada kwallah suna zuraromata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button