NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

   Mikewa Ummi tayi hannu bisa kirji tana fadin”Kutumar uba,wata yarinyar kasa amkranta,kana hauka ne don Ubanka,yaushe kayi girman da zaka saka wannan yarinya a mkranta baka nemi shawarata ba” tafada tana jifansa da wani mummunan kallo,mirmishi yayi kafin ya riko hannunta yana fadin”haba Ummi na,tsaya kiji mana kibari kiji dalilina mana kafin ki yanke hukunci”Kallonsa tayi kafin ta fizge hannunta tana fadin”baka da Abunda zaka fadamin,”

   Dafe kai yayi yana fadin”Koda kuwa na shawarar yadda zan rabu da auren yarinyarne salin asalin batare da kowa ya zargeki ba balle ya zargeni” yafada fuskarsa tana bayyana tsantsan gaskiyansa kallonsa tayi taga yadagamata kai shiyasa sai tazauna tana fadin”Fadi naji wani hanyace, da sai,kuma sai anshiga mkranta”mirmishin gefen baki yayi aransa yana fadin”Ummi danja.

    Kallonta yayi kafin ya riko hannunta yana fadin”So nake na sanyamata mkranta tayi karatu koda Zuwa tayi candy ne,kinga daganan sai na roketa kan zan saketa,takoma gun iyayenta,bazata kiba,tunda mun taimaketa tayi karatu shiya zai sa kota koma bazata bari Baffa yaga laifinmu ba zatayi kokarin karewa saboda hallacin da muka mata kingane? Zuru Ummi tamai da ido tana kallonsa gefe daya tana nazarin mganansa,shikuwa kallonta yake yana ta addu”a Aransa Allah sa ta shiga buhun daya dingamata ko ya samu daman Dinketa aciki????

    kallonsa Ummi tayi kan tace”To ammh dole ne sai ka sata mkranta,why not kadaukan mata lesson Teacher yarinka zuwa gida yana koyamata,nifa bansan tayi hulda da kowa balle hartaji dadin Zama Agarin nan,”Mu”azzam yayi Saurin cewa”No Ummi ai inaga duk daya ne,kibari dai taje mkrantan ai matakan tsaro zan sakamata duk motsinta yana idona,”shuru Ummi tayi sai zuwa chan ta saki ajiyar zuciya kafin tace”To shikenan na Amince ammh da sharadin wlh tana kammallawa zaka sallami shegiya don wlh na tsaneta kamar mutuwa ta”Mu”azzam da murna takashesa yace”Dolen ta ma tabar miki danki Ummi na,da gudu zan korata garinsu da takardan sakinta”Jin haka yasa ran Ummi yayi fes tace”Inko haka tafaru nasan cewa Shettima zai dandani ko da kwatan Abunda ya dandanamun ne”Tafada fuskarta na fitar da Annuri.

   Shuru Mu”azzam ya mata itako Murna yacika fadi take”Ko kaifa,ai wlh duk abunda kaga inayi saboda kai ne Allah ne kadai yasan wahalan dana ci kafin ma kazo duniya,wlh da ason Ransu ne dayanzu nayi barinka”Tafada muryanta tafara chanzawa Rumgumo kafadunta yayi yana fadin”Karki damu Ummi komai mai Wucewa ne,yanzu abunda nakeso dake,ko fadan dakike mata,kidaina bani son Ta rainaminki domin ke ba sa”arta bane ki barni da ita tacika lokacinta zan sallameta takara gaba”Cikin Farinciki Ta rumgumesa tana fadin”Ina matukar sonka my Son,kana son Farinciki duk abunda zai batamin rai kana gujesa,Allah yamaka albarka.”Tafada muryanta na Fitar da amon Tsantsan Farinciki,rumgumeta yayi back yana mirmishin mugunta aransa yana ayyana cewa yamayi sakaci Tuntuni da bai hadama Ummi irin Buhun daya dace da ita ba,ya dinga sakata yana Dinkewa????zakaci kaniyarkane,in Ummi ta fahimci haka.

Su Lami Mu”azzam yakira suka dauki kayan suka shiga dashi dakin zahirah,wacce ke kwance kan cinyar karime tana mata hira,dukkansu mikewa sukayi suna binsa da kallo,lami ce tace”Yallabai yace ashigo dashi..’Ajiyar zuciya Zahirah ta sauke jin an ambaci yallabai domin wunin yau tayi kewarsa sosai,ammh abunda yadauremata kai Ummi batanan ne databari aka shigo da kaya dakinta,domin tasan cewa matukar Ummi na gidan nan ba wanda ya isa.


  Baisamu zarafin zuwa dakin zahirah ba sai bayan yadawo sallar issha”i lokacin har sunyi sallama Da Ummi ta shiga ciki ta kwanta ranta fes za”a ci Uban zahira,shiyasa bata damu da ita ba, balle hartasan metake ciki,Lokacin daya shiga dakin yana sanye da jallabiya mai Ruwan kasa,kansa babu hula fuskarsa tayi fayau da ita alamun ya samu kwanciyar hankali,Yana shigo bayan ta gaisheshi ta Fice zahirah ko wacce ya ritsa afalon tana zaune cikin doguwar rigarta atamfa A shape wacce ta fitar da Surarta,yana shigowa tafara sunkuyar dakai,tana sunne kai,shiko gefe yaja yana karemata kallo Taji ajikinta yana kallonta shiyasa taki dagowa gashi kanta ba dankwali,kitsonta ya bayyana wanda ya zubo mata har baya,ganin yadda takeyi ne takasa zama yasa yafara takawa zuwa gabanta sai jin mutum tayi gabda ita ya durkusa gwiwansa yana shafan Cinyoyinta kantasamu zarafin Matsawa ya saka hannu ya dago habansa yana fadin”Kunyan kuma ta mecece? Umh…”Yafada yana kuramata ido Runtse ido tayi ammh tana mirmishi har Beauty Piont dinta suka lotsa shagala yayi da kallonta saboda yadda kowani sashi na jikinsa ke amsa,mirmishin nata,lebenta yake kallo yadda yake fitar da maikon Liptick Shauki ne ya debesa har baisan sadda ya kai bakinsa ya sumbaci nata ba,saurin bude ido tayi,jin yadda wani abu mai Taushi ya jingina da lebenta sai kawai taci karo da Fuskar Mu”azzam gabda tata,wanda idanunsu suka sarke da juna kafeta yayi da wani siririn kallon wanda mutum daya ake mawa wanda zuciya da rai suka yarda cewa yes wannan Abun mallakinsu ne,idanunsa suka fara janza kala lokaci daya yaji yana neman durkushe,idanun yarinya suna tafe da wani sirrin na mussaman wanda duk sanda ta kallesa wlh tallahi baya sanin, sadda yake shagala da kallonta, wani mircle ne ke jansu sun kasa dauke ido akan juna,Zahirah kuwa jitayi wani yammm…”na binta ta ko”ina kanta ne yafara juyawa ammh kuma idanunta sun kasa dauke ido akansa jikinta ne yafara rawa lokaci daya kuma sai ga hawaye saboda yadda idanun Mu”azzam suka mata dabaibayi,ta yarda ta amince mu”azzam Namiji ne mai cikar zati da haiba,wanda in yaka idanunsa akan mace komin takamarta da isarta,koda kuwa tana fama da sarauta ko mulki lokaci daya zataji ta raina kanta da duk abunda ta mallaka.

  Ganin gangarowan hawayen ya sa yayi Saurin sakinta yana mikewa hannusa duka ya sanya cikin aljihun Jallabiyan yana kallonta bayan ya saki ajiyar zuciya yace”Kuka kuma..”To kinga share hawaye kiji wata mgana mai dadi’Jin haka yasa tasaka hannu ta share hawayen ammh bata bari sun hada ido ba,dan mirmishi yayi kafin yace’Ki duba kayan na,akwai na sakawanki na gida,am srry Tuntuni yakamata na siya miki bansamu lokaci ba,kana ki zama cikin shiri gobe zaki zama yar mkrantan Nurul Bayya International Academy.

  Jin haka ya ta dago ta karfi tare da zaro ido tana fadin”da gaske ya mu”azzam…”Tafada da dukkan Farincikinta lokaci daya tabayyanar da fararen hakoranta waje kai ya gyada mata yana fadin”Insha Allah..”Ai da hanzari ta mike shidai kawai sai ji yayi tafado jikinsa kikam tana fadin”Ngd sosai ya mu”azzam Allah ya saka ka farinciki kamar yadda kake sani,Allah yakareka aduk inda kake yakuma sama Aikin Albarka ngd..”Tafada idonta sunyi kwalkwal da kwallah..

Wani dadi ne mai sanyi yake kwarara azuciyar mu”azzam cikin saurin ya saka duka hannunwansa yazageye kugunta dashi yana kallon kwayar idonta yace”Karki bari wa”innan hawayen naki su zubo..In baka hakaba nace na fasa”Jin haka yasa tayi saurin hadiye kukan mirmishi yayi yana shafa kumatunta yace”Naji dadin addu”anki but,kin manta abu guda daya baki man ba”kallonsa tayi kan tace’meye shi,kafada insha Allahu zan yi maka..”Yana yar dariya yace”Alkwari..’ta amsa da cikawa..’Kunnenta yakai bakinsa yamata rada bansan meyace ba nadai ga tazaro ido lokaci daya tana kara dunkule kanta bisa faffadan kirjinsa daya yimata Rumfa tana dariya kasa kasa tace cikin shagwaba”Ni..ni..A”a..Kachanza wani”Dariya yasaki mai kayatarwa yace”Ba chanji,kinga kuma kin dau alqawarin,kuma kinsan hukunci wanda yadau alqawari bai cika ba ko”yafada da son razanar da ita kwalkwal da ido tayi tana kallonsa dariya ta kusa kamasa sai ya basar yana kallon gefe yace”Jiranki fa nake zanje na kwanta ne..”jin haka yasa tayi kukan kura ta dage kafa tunda yafita tsawo ita iyakarta kirjinsa,ta sakarmai kiss A kumatu ammh bayan ta rintse ido tamau kamar wacce taga abun tsoro.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button