NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

Wannan kenan.


Akwanakin nan kwatakwata zahirah takasa gane kanta domin yanzu cin abincinta yayi over sai taci abinci sau biyar arana,kuma tsakani babu tazara datagama ci zata ji yunwa ,ga son cin kayan kwalama ko mkranta aikin ta kenan shan kankarar madara itace siyan wanan cin wannan,Asma”u abun yafara bata tsoro da wannan sabuwar dabi”ar ta kawarta har sai da tamata mgana itama zahirah tace batason dalili ba,har Asma”u ke cemata ko pills din kiba tasha,dariya tayi mata kafin ta rantse mata ita batasha komai ba,hhhhhh..Asma”u taci wake ne fa????

Shikanshi mu”azzam yalura da haka don kullum duniya yana hanyan siyomata ice cream don in ya dawo bashi wlh bazata iya barci ba,shiyasa baya rabo dashi roba biyar har fiye yake siyomata tasha saura tasaka a fridge na gobenta,dashi take zuwa mkranta in tadawo tasha kafin ya kare ya siyomata wani,shibaima taba maida kai ba,shi azatonshi kawai kwadayi ne irin na matan aure shiysa baiwani damu ba da bincikarta ba sha”aninsa kawai yakeyi domin ba karya zahirahn nasa takara sugar kwantar dakai yayi yana ta amfana da Ni”imar arziki babu abunda ya dameshi.

Su kansu su karime sunyi mamakin wannan kwadayin uwar dakin nasu ammh dayake su manyane tuni sun harbon jirgin meke damunta,sunyi murna ammh zullumunsu daya Ummi,in Ummi taji wannan al”amari akwai tashin hankali mai girma wanda Allah ne kadai zai iya tsaidata sun dai roki Allah koma miye Allahya kawosa da Sauki.


Yau amkranta Asma”u tazo da wainar kwai da madarar hollandian, bayan antashi break ta daukomata Zahirah ita wainar kwan kawai takeci saboda yadda takesonshi yanzu shiyasa don itama Asma”u ke zuwa dashi kullum,ita madarar ta dauka ta bude kenan Zahirah taji shaki kamshim kamar wasa zuciyarta ta hau tashi,yamutsa fuska tayi tana kallon Asma”u….

Tace” Don Allah ki rufe madarar nan wlh zuciyata tashi take kamar zanyi amai..”shekeke Asma”u ta kalleta kan tace”Topha! sabon salo Yau kuma shi hollandian din ne bakison warinshi ko”? tafada tana mata kallon kina raina min wayau.

Kwalkwal zahirah tayi da ido tana fadin”Allah da gaske,bakiji kina budewa ba,yadda zuciyata ta hau tashi…”Dariya Asma”u tayi kafin tamike tana fadin”Allah ko,ke wallahi ko mai ciki bazata nuna miko tsirfa ba’tafada tana karamata madarar abaki tana mata dariya tureta zahirah tayi, jin yadda gabadaya cikinta ya yamutsa kan ta samu zarafin mgana aman ya biyo baya,nam tashiga kelayawa kan benci tanayi tana rike cikinta kaf ta amaye Wainar kwan dataci harda ice cream din datasha da safe kafin tazo mkranta.

Asma”u na ganin yadda zahirah ke amai cikin galabaita sai ta rumtuma da gudu zuwa school clinic tafada da hanzari aka hadata dawata sister ta biyo bayanta zuwa cikin class din ganin yadda Zahirah ta jigata ne,yasa sister tace ma Asma”u takamata su kaita chan clinic din,haka ko akayi suka kamata suka karisa da ita cikin clinic din,aman ya galabaita ta shiyasa suka sanyamata drip tare da mata alluran barci,dayake clinic mkrantan gaskiya suna da kayan aiki,Sister da kanta tabi Asma”u suka je suka kai report ga hukumar mkaranta Tare da Sunan zahirah nan take akama Mu”azzam waya wanda yake office yana tsaka da aiki kiran hukumar mkrantar tasu zahirah ta shigo wayarsa da lbrin abunda ke faruwa.

Ai hankali sa atashe ya rabo office dinsa,direct ushe ya daukesa sai mkrantar su zahirah,suna zuwa office din shugaban mkranta akamai jagora har clinic din inda zahirah ke kwance ana karamata ruwa,wanda yama kusa karewa,ga Asma”u zaune gefenta ta zabga tagumi.

Kawai sai ganinsa tayi ya fado dakin hankalinsa atashe,sau daya tataba ganinsa ammh ta shaidasa,mikewa tayi tana gaisheshi ya amsa yana kallon zahirah wacce harta fada na rana daya kawai innalillahi kawai yake maimatawa kafin ya kalli Asma”u yana fadin”wai meya sameta ne,garin yaya? yafada cikin tashin hankali.

Asma”u tasunkuyar dakai tana share kwallah ta shiga sanar dashi duk abunda ya faru har kawota clinic din datayi,jinjina kai yayi yana maimata amai acikin ransa,bai wani tsaya ba yafadama hukumar mkranta zai tafi da ita,basu da tacewa kalulan aka ciremata tunda haryanzu bata farka ba,cak ya dagata sai mota ya sanyata Ushe yaja suka fice daga mkrantar Asma”u na daga musu hannu idanunta sun ciko da kwallah,haka ranar ta wuni ba karfi sukusuku da ita ana tashi ita ta tafin ma Da zahirah school bag dinta zuwa gida,tunda an manta dashi.

Suko daga mkratar direct specialist hospital yace Ushe ya wuce dasu,suna zuwa ya fito yakara daukanta bai direta ko”ina ba sai bisa madaidaicin gadon dake office din Dr Abduljabar wanda ke tsaka da duba patient ganin yadda mu”azzam ya shigo cikin tashin hankali yasa ya sallame,wanda yake dubawa yataso yana kallon zahira wacce ke sauke Numfashin wahala,kallon mu’azzam yayi wanda ke rike da hannunta ya kuramata ido cikin tashin hankali.

Gyaran murya yayi yana fadin”subhanallah brr,meya sameta kuma..”?Dagowa mu”azzam yayi cikin damuwa yana labartama Dr Abdujabar lbrin da Asma”u ta bashi yakara dacewa”Lafiyanta kalau fa da safe,don n ijiyeta a sch kafin mu wuce office,ammh yanzu ba da dadewa ba,aka kirana ake fadamin abunda ke faruwa” ya kareshe fada kamar zaiyi kuka.

Kuri Dr Abdujabar yayi mai da ido kafin yadan murmusa kawai yana fadin”It Normal ai brr,karka damu bawani abu ne natada hankali ba”Yafada yana ficewa sai gashi yadawo da wata Nurse ya umarceta data diba jinin zahirah babu bata lokaci ta diba,wanda shiyayi sanadiyar farkawan Zahirah tana nishi,Mu”azzam ya riketa yana mata sannu,kallonsa Dr Abduljabar yayi yana fadin”Yauwa ka mata ku je tiolet tayo Fitsari ana bukatarshi”Yafada yana mika mishi wata yar kwalba,amsa yayi yana kamata suka shiga bayin ya taimaka mata tayi fitsarin suka fito ya bawa Dr.Abduljabar wanda ya amsa ya mikama Nurse din yana fadin”Kuje dashi lab yanzu ku dawo min dashi..”Yafada ciikin bada umarni karba tayi cikin girmamawa tana fadin”ok Sir..

Comment,share and vote

Janaf fans one luv❤
[18/08, 14:18] 80k: ????UWAR MIJINA..!????
(Soyayyah,sadaukarwa,hakuri,tare da biyayyah mai tsanani)

  *Alkalamin:JANAF*
  *Wattpad:Janafnancy*

Dedicated to my blood Sisters JANAF

Intelligent writer’s Asso

I Dedicated dis page to u all BA”ARE FAM????…

NOT EDITED????

       *NO 21*

Ba”a wani dauki lokaci ba sai ga Nurse din tadawo da wata farar takarda a nannade,ta mikama,Dr Abdujabar cikin girmamawa,ya karba yana warwareta shiko mu”azzam hankalinsa ma baya kan Dr yana gun,Zahirah wacce keta faman mai kukan shagwaba shiko yagama susucewa yana ta faman lallabanta.

Dr Abduljabar nagama karanta Takarda yayi wani kayatattacen mirmishi,saboda shi daman yasan za”a rina,lalle Brr,shegen kayane shida yace Rainonta zaiyi don mai garinsu yanzu cikin ta ruwa tasha,mikewa yayi ya isa garesa yana mika masa hannu sukayi musabaha bakin Dr.Abduljabar yaki rufuwa ya furta cikin murna da Farinciki.

“Congratulation Brr,Ibrahim Moodu ur wife is 4month pregant..”Yafada yana kara jinjina,hannunsa,wani yanayi mu”azzam yaji kamar amafarki yawani zabura yana fadin”Eh….Dr…?”Yafada yana bayyanar da duka hakoransa waje saboda murna Gyada masa kai Dr.Abduljabar yayi kafin yace”kwarai da gaske nan da wata biyar zaka zama baba..”ai dawani hanzari Mu”azzam ya zube kasa yana kwararo godiya ga rabbil izzati wanda shikadaine, yake iya saka bawa cikin wannan Farinciki mara misaltuwa,yakai wajen minti biyar kafin yadago Fuskarsa tana bayyanar da tsantsan Farinciki,rumgume Dr Abduljabar yayi yana Fadin”Alhamdulillah…Allah shine Abun godiya..”Dariya Dr kemai yana buga bayansa yake fadin”Tabbas domin shikadai ke iya bawa wanda yaso kuma ya hanawa wanda yaso,so congratulation Once again.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button