NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

  Dariya ta kyalkyacemai dashi tana fadin”Uhmm Kaji masu ya”ya..”mirmishi yayi kawai domin karfin hali kawai yakeyi,jinta cikin Farinciki yafi mai komai dadi,gyara kwanciya yayi yana fadin”wasu sunaye zamu sanya musu..”shuru tayi kan tace”Macen asamata Sunan UMMI tunda dama mai kama da itane,Namijin kuma zabi na gunka angon karni..”Tafada tana yar dariya.

  Wani abu yaji aransa,Sunan Ummi,ashe har zahirah zata iya cewa asakama yarta data haifa da cikinta sunan Ummi,duk bayan dibim Abunda Ummin ta aikata mata,lalle zuciyarta mai kyau ne,cikin zubar hawaye yace”Nagode my Hirah da wannan kararramawa naki,kifadama shuriem yayi mata huduba da SUHAIMA ummina,sai Namijin yayi mishi huduba da MUHAMMED MOODU Abbana,duk da bantaba sakashi a idona ba,sai ahoto..”yafada muryansa tana bayyanar da kukan dayakeyi

   Itama saitaji kukan yazomata tace”Kabar kuka,ko nima yanzu nafara maka nawa.,yazamuyi Tunda Abunda Allah ya kaddaromana kenan ammh wlh ya mu”azzam bazan iya rayuwa bai dadi baka ba,kaine ginshikin rayuwar zahirah na har abada..”tafada tana share hawaye,dafe saitin kirjinsa yayi kafin yace cikin wani hali..”Nasani hirata,Nima anan bamgaren haka take,rayuwata zata lalace matukar baki dawo gareni ba” zahirah tana hawaye tace”To taya zan dawo gareka bayan saki uku kayiman..”wani numfashi mu”azzam yaja kafin yace”Bansani ba,wlh bansani ba hirah..Ki kwanta kiyi barci sai munsake yin mgana I LOVE U SO MUCH..”yafada yana kafafunsa narawa.

Jikinta na tsuma tace” LOVE U MORE AND MORE YAYANA..” tafada tana kamkame wayar kawai sai ta fashe da kuka shima kamkame wayar yayi yana mirgina bisa gadon yana zubar kwallah,jin yadda kirjinsa ke suyane ga saitin zuciyarsa na harbawa yasashi katse kiran.
 

  Kuka Zahirah ta fashe da shi,sai da tayi mai isarta kana ta hakura ta share hawayenta,Koda su hajiya suka dawo dakin shureim ya sake kiran wayar Dr.Nan Mu”azzam din da kansa yake fadamasa cewa ga sunanyen da zai ma yaran huduba dasu,yayi mamakin jin sunan Ummi abakinsa,ammh ganin uwa fa ta wuce wasa yasa yayi shuru da bakinsa,to hakan ta kasance ga kowa,duk wanda yaji yarinya taci sunan ummi sai yayi galala da mamaki ko bukar din ma yayi mamaki ammh sai zahirah ta shanyesu mamakinsu da cewa ita tace tana son Sunan,to wazai yi mgana Bukar yaji aransa shima yayi sa”ar samun diyata gari,koba komai ta rama sharri da alheri,kuma ya tabbata in taji sai jkinta yayi sanyi.
   

   Shureim yayi musu huduba da sunayensu,gidansu Baffa shettima suka koma suka kwana bayan Shureim ya ijiye musu Dubu dari biyu cash na wanda xa”a siyama yara ragunan sunan,da sauran abun amfani,bayan uban siyayyar daya narkamata bayan sun damkamata kayanta harda wayanta da sukazo dashi,shureim dakin baffa ya kwana Ushe kuma dakin kofar gida aka gyaramai ya kwanta aciki, itakuma hajiya dakin yakura ta kwana wanda sun kusa raba dare suna jajantama kansu dakuma yadda rayuwar masoyan biyu zata kasance,sundai yi fatan Allah ya yayyafama soyayyar ruwan sanyi Allah kuma ya kauda mummunar kaddara.

   Gari na wayewa karyawa kadai sukayi suka dau hanya wanda yakura taso su tsaya hajiya taki saboda aikin shi Shureim din,kuma da yadda suka baro jikin mu”azzam din babu dadi,ko gidan bukar din basu koma ba suka kamo hanyar komawa Abuja,sai Fatan Allah yakai lafiya,sunbar garin Ranar da”aka yankama yara firda firdan raguna yan”uwa da abokan arzuka suka taru ana shagalin taron suna,koda ma su Shureim basu zoba tuni bukar ya tanadarma yarsa komai itada yaran,ya siya musu kaya na alfarma shiyasa ranar ta dinga shiga tana fita,ammh duk wanda ya ganta sai yayi fadan maijego da rama,to bata wani cin abinci ga tsotson yara,duk da ma ana hada musu madara,Zahirah kuwa Ranta gabadaya wuni yayi ba dadi,data zauna tayi shuru sai kwalkwal kuka,babu wanda yayi yunkura hanata saboda ansa dalilinta na kuka,to yazatayi sai hakuri,tunda tahadu da uwarmiji mara imani ta maidata karamar bazawara,haka yan”uwanta keta cewa,haushin abun na damunsu suma arai kawai basa nunawane.

  Tuni yara Sukaci sunayensu SUHAIMA IBRAHIM MOHAMMED MOODU Da MUHAMMED IBRAHIM MUHAMEED MOODU Sai fatan Allah ya rayasu cikin tafarkin addinin isalama,da kuma fatan Allah ba maijego lafiya mai dorewa Amin,yan group din janaf novella sun hallarta dasu da yan Uwar mijina fans1,2and3 ammh basu wani samu tarba mai dadi ba jin daga tawagar Ummi ce sukazo babu wanda yayi musu kallon arziki ba don ma bukar ya kwaba ba yasin cikin gidan nan da ansamu mai chanza wasu daga cikinsu halitta saboda Yadda suka Fusata da wulakacin da akama yarsu,jagoran Tafiyan my Sisi ce Aisha Alto da sahibata hafsat hafnan,ai jiki ba kwari suka dafafo hanya fuskar ba Annuri saboda haushi biyawa gaida mu”azzam din dasukace zasuyi ma ba wacce tabada fuska,kowacce gidanta aka sauketa jiki a sanyaye????????????????


  Su hajiya kuwa koda suka dawo achan asibiti suka tarar da Ummi duk da sau uku arana ake barinta shiga,tunda yau da safe yafara cin abinci,to tea kadai ma yasha,shima bada yawa ba,saboda yadda bai iya jin dadin komai abakinsa,Ummi kuwa sai jidashi take tana wani riritasa shiko kallonta yakeyi yana jin haushi abunda takemai,ta riga tagama kashemai rayuwa kuma lallabansa metakeyi ai data barshi ya karisa mutuwa yahuta itama tahuta.

  Abunda ya dauremai kai zama tayi tana lallabansa da yayi hakuri ya kwantar da hankalinsa yana warkewa tayimai alqawarin auramai mace,wacce tafi zahirah sau dubu ,wacce zata dace dashi,kawai yabata lokaci sai ta sanyasa farinciki fiye da yadda baya tsammani,da toh kawai ya bita,ammh aransa yana fadin Ummi bata kaunarsa ya yarda to Wlh sai dai ta aurama kanta Auren ammh badai shi,shi in ba hiransa ba to yayi alqawarin dauwama haka har abada,domin duka sauran mata maza yake kallonsu Hiransa ce kadai ta fita dabam,komai nata dabam ne dana sauran mata,zuciyarsa tana cigaba da suya shiyasa cikin ransa ya yankema kansa mafita ya gwammace ko zai Mutu to yayi nisa da Garin ila ma da Kasar gabadaya ,don dai ya cigaba da zama anan har ya tsinci lbrin hiransa zatayi aure da wani to ya tabbata adaren zuciyarsa zata,buga ya mace.

   Kwana daya su hajiya suka kara suka wuce,batare da sunfadama mu”azzam yadda bukar yadau zafi ba,hajiya dai tayita lbrin yan biyu da gayyah saboda Ummi,wanda ko ajikinta don ko a mafarki ma bata kaunar ganin ya”yan duk da mu”azzam ya haifesu ammh batajin zata sosu domin tsanar uwarsu ta shafesu,shiyasa ma batama bi takansu ba balle ma hartaji harda sunanta akasa da hajiya tafara zata fice ta basu waje,tana wani cin mgani abunta,Sunkoma saboda aikin shuriem yana ta samun waya daga wajen aiki ga gida kuma ambar Zulaika ita kadai,daga ita sa yara,dole tasa suka tafi,bayan hajiya tayima Ummi fadan kiyayen harshenta,gadai da’n nata nan data ke Tunkaho kwance ba lafiya in ta gyara rayuwarsa ta gyaru ita kara batamawa itace zata sha wuya tadai amsa da taji kawai,ammh har aran Ummi wani kudiran ne ke ranta na dabam.


BAYAN SATI DAYA

  Zahirah da kanta ta kira Asma”u wacce kewaar zahirah ya isheta,tayi ihun murna sanda zahirah ke fadamata ta haihu da abunda aka samu,ammh tayi kukan jin sakin wulakancin da Ummi ta saka akama zahirah wanda har taci burin duk randa ta hadu da Ummi saitaci mata mutumci,Asma”u tazama so cool a mkranta ba zahirah gashi watanni kadan yarage su rubuta SSSE in ta tuna haka batasan sadda hawaye ke zubomata,Itakanta Mami ta tsausayama zahirah sosai tana fadin”Yarinya karama tahadu da jarabawa iri iri na rayuwa,mami da kanta tayi ma minista mgana zasu maiduguri,domin Kawance ai baice haka ba,nan da nan ya Amince suka tashi tundaga Abuja har maidguri da abun arziki niki niki Lalle yan maiduguri sunga kauna,don kwana biyu su mami suka musu kafin sukoma ,bukar yaji tsananin Farinciki ko bakomai zahiransa ba tazama wani abu,yau gashi ta dalilinta har diyar minista da matarsa suzo gidansa suyi kwanaki domin yarsa lalle Allah Abun godiyane,Zahirah ko taji dadin zuwan Asma”u ko bakomai tasamu wanda zasu tattauna matsalanta da ita,tayi kuka sosai Asma”u na bata hakuri,domin fa babu yarda suka iya kaddarace ta riga fata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button