NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

   Kwanansa biyu shureim ya taho wannan karan shida iyalansa yazo zulaika da yara,sungaisa da Abbie khamis sosai,tunda yana ganinsa ya fahimci shine dan”uwan da mu”azzam ke yawan fadi tare suka wuni suka kwana suna tattauna yadda zasu bulloma al”amarin neman mu”azzam din,wanda Abbie ko Afuska bai nuna yasan inda mu”azzam din yake ba.

Sai awashagari suka dauki hanyar maiduguri mota biyu sukayi,motar Shureim shike driving gefensa kuma Abbie ne sai yaransa dake bayan mota motar da ushe kejanta kuwa,hajiya ce da Ummi sai zulaikah suka yi wannan Tafiya,dayake sun taso da wuri,kuma sunyi gudu koda karfe 2:00pm tayi suna cikin gidan shettima wanda suka gansu kwatsam,shettima kuka yake yana rike khamis yana neman gafaransa,wanda shikanshi khamis din sai da yayi kwallar tsausayin yadda rayuwa tajuyama shettima baya nan yakara tsorata da duniya matuka,suna nan sai ga bukar yazo,nan shima aka taru akamai bayanin Abbie khamis suka gaisa cikin fara”a mutumta juna lokaci daya Abbie na kara bashi hakuri,Bukar yace,’babu komai,wlh komai ya wuce,da Abbie yanemi ganawa da zahirah yakuma ga jikokinsa Shuriem ne cikin takaichi yake shaidamasa tayi aure kuma tatafi da yaran,tunda tana shayar dasu ne.

  Matukar razana Abbie khamis yayi saboda tuna yadda sukayi da mu”azzam akan laillai laillai yaje ya duba masa hiransa da yaransa don Allah,harda kwallansa alokacin,yanzu ya zaiji inyaje masa da lbrin bai ganta ba,kuma ma hartayi aure tatafi da yaran gidan mijinta,bai da wannan karfin gwiwan na fadama mu”azzam haka,sai da yasan me zai fadamai,fatan zaman lafiya yayimata daganan aka shiga hirar duniya.

  Kwana daya sukayi suka juyo suka dawo gida bayan sun cikasu da abun arziko,ko wannan zuwa shureim yazoma dasu little Umm,kaya da madaransu,da kudi har 30k yace abama zahirah ko suna bukatar wani abu,bukar din dai ya karba yace zai Tura mahgana ta kaimata,zulaika ma taso taje gun zahirah ammh kemekeme shureim yahanata zuwa,shifa har zahirah haushinta yakeji balle,bukar da kallonsa kawai yakeyi,saboda yadda yabada goyon baya aka ketama dan”uwansa gona.

   Kwana daya Shureim yakara yayi sallama dasu yakoma shida iyalansa,bayan sunyi sallama da Abbie khamis shima gobe zai tafi,inAllah ya yarda,ummi kuwa hada kayanta tayi tsaf tace sai Sudan don zamanta yakare a nageria,hajiya data saki baki da mamaki,ta tambayeta gidan da dukiyar danta waxata barnawa,ummi tace ita zata barmawa ita da Shureim, zata bi khamis takoma inda tafito wato gidan marayun da’aka riketa,wannan kalamar saida ta sanya hajiya,kuka na tsausayin Suhaima,itafa amaraici tatashi batasan kowani gata ba,sai na moodu wanda bai dade tare da ita ba,Allah yakarbi abinsa,sai mu”azzam wanda yakoremata duk rashin wannan,yau babu shi,dole Suhaima ta rasa sukuni.

  Abbie ne yayi ta bata hakuri kanta zauna harjaye ya dawo yayi mata alqawarin dawowa nan da lokaci kadan,ga nombar wayarsa data handline din gidansa duk yabata don dai ta yarda,dakyar to Ummi ta hakura ammh tace in ya dawo wlh kafarta kafartshi,ita tagama zama akasar Nageria tuni,tunda mu”azzam dinta ya barta taji kasar ta ficemata aka.

  Sati daya yayi cif,washegari Ushe yakaisa Filin jirgi tare da rakiyar hajiya da Ummi,sai da jirginsu yadaga kana suka koma gida,sunajin kewa ko bakomai mutum ma rahamane,balle Ummi datake ganin Abbie khamis kamar wani alahalinta ne.

    Kuyi manage plz,banjin dadin jikina ne,u pryers iz needeed*

       Jamilajanafty

UWAR MIJINA…!
(Soyayyah,Sadaukarwa,hakuri tare da biyayyah mai tsanani)

       Mallakar:JANAF
       Wattpad:Janafnancy12

Dedicated to my blood Sisters JANAF

GIFT TO:Hussain80k

Intelligent writer’s Asso

              NO 35

      “””Abbie ya isa kasar Sudan Lafiya kalau,wanda mooh da mu”azzam da lubna harda mom suka daukosa daga Filin jirgi zuwa gida,bai samu zama dasu ba ,saboda gajiya sai da yayi wanka yaci abinci ya huta,kana suka zauna,mu”azzam Ummi yafara tambaya yatake,? wani hali take ciki? tana lafiya?

  Abbie yafadamai Ummi tana cikin wani hali na kewa,da muradin ganinsa,dakuma kadaichi da nadama,nan yake yafadamishi ummi tayi matukar nadaman Abubuwan data aikatamai,tana bashi lbri tana kuka,Abbie yafadama mu”azzam cewa Ummi na bukatarsa ainun kodon tallafan Rauninta,don tama yanke shawaran biyosa takoma gidan marayun da”aka riketa.

   Dukar dakai kawai mu”azzam yayi yana tsiyayan hawaye,hakika babu wacce takai uwa mahimmanci arayuwar da”hakika duk da tarin laifin Ummi gareshi daidai da rana daya baitabajin soyayyarta da kaunarta dayakeyi ta ragu ba,kullum kwanan duniya sai ya fidda hawaye saboda tuna ummi ko karyawa bata iyayi,sai ta ganshi ta tabbatar da lafiyansa kalau take iya sukuni,to yanzu yana tunanin yaya zata iya rayuwa bashi,wlh tallahi ba ason ranshi yatafi ya bar Ummi ba,babu yarda zaiyi ne,alokacin baya da zabi sai nesa da Ummi da Komai na rayuwarsa alokacin.

  Abbie bai boyomasa ba,harta Rashin lafiyan Shettima,da zuwansu maiduguri da yadda Shureim ya damu  yanata fafutukar nemansa ko”ina,tsausayi tare da wani bakinciki suka tarun ma Mu”azzam ranar sai da ciwonsa yayi kamar zai tashi,don nan take tarin ya sarkeshi ya shiga yi ba kakkautawa,Lubna ta rude rikosa tayi tana jeramasa sannu,Abbie bai kyalesa ba yayi ta masa nasihan yarda da kaddaran ya cire abunda ke ransa yayi Shirin komawa ga mahaifiyarsa,wacce take bukatarsa,Fada yayi masa sosai kuma da alama Nasihan tayi tasiri ga mu”azzam domin koda yakoma daki shuru kawai yayi,shibama takansa yake tunanin halin da Ummi ke ciki yafi damunsa,ga hiransa Abbie baice mai komai ba kuma yanajin Nauyin Tambayansa,lokaci daya yaji yana kewar gida,ga Tsausayin Halin dan”uwansa ke ciki,ga son gani ya”yansa dayake kwana dashi ya tashi dashi,dole ya daurema zuciyarsa,yakuma yarda ya amince haka Allah ya tsaramai bazai kara samun wani jin dadin rayuwa ba.

Shiko Abbie yaki dago zencen zahirah ne,saboda kada mu”azzam ya tambayeshi,game da ita shikuma bazai iya gayamasa tayi aure ba,saboda sanin Halin dayake ciki,duk akantane,to ya zaiji indan Akacemai tayi Aure,shiyasa yaki mai mganar ma gabadaya shi soyake ya barma Allah komai yakoma gida gun Ummi yakuma cigaba da aikinsa Abunda yafaru ba shikenan Tsinkewar rayuwarsa ba akwai saura,in yayi hakuri in sunada rabon zama sai su zauna.


Maid

  BAYAN SATI DAYA

       “Yau takama asabar ne,lokacin karfe 11:30am,na safe ne,zahirah na cikin dakinta tagama yimasu Little Ummi wanka kenan,ta shiryansu cikin kayan sanyinsu,wanda cikin sakon da mahgana ta kawomata tace sakon Shureim ne,nan take fadamata zuwansu dakuma zuwa Abbie khamis,jikin Zahirah yakara sanyi ta tsnke da al”amarin duniya,mganar Lbrin mu”azzam kuwa koda ta tambaye Mahgana cematayi bawani lbri haryanzu dai ana cigaba da addu”ne,bata nunama maghna komai ba sai bayan ta tafi,ta tasa su moodu tana kuka,kukan data rasa dalilin yinsa,ammh tafi karkata hakan da tsausayinta kanta datakeji data ya”yanta domin haryanzu batasan menene ma makomarta acikin gidan ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button