NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

Suma da zasu koma sunga karramawan dangin Zahirah don suma sunhada musu komai iya karfinsu suka rabu suna godiya,sun cigaba da waya da Asma”un zumuncinsu ko saima yafi da karfi.


Sati daya Mu’azzam yayi a asibiti kafin asallameshi ya dawo gida,bayan yasha dokokin likita,na cire damuwa aransa,kuma yadaina zurfafa tunani da yawan zama shuru,yakuma kiyaye duk abunda zai bata maasa rai ko na mutum kona Tunani,duk ya gujesu dakuma samun ishasahen hutu,dakuma shan mgani bisa ka”ida,Duk ya amsa da toh ne kawai ammh shi yanzu taya zai iya daina tunani ai har abada an gayyato Tunani,ckin rayuwarsa ne Tunda aka rabasa da hiransa.

    Kwana uku da dawowansa gida Ummi tana ta bare baren kula dashi ,karewartama dakinsa tatare ko tari yayi tadinga tambayan lafiya kenan,jama”a nata zuwa gaishesa expecially yan wajen aikinsu,gaskiya babu laifi ya samu sauki sosai tunda bai fara tsallake dokar likita ba,shima burinsa ya mike ga kansa,saboda ya aiwatar da kudirinsa domin babu gudu ba ja da baya.

Satinsa daya da dawowa gida ya tuburema Ummi shi zaikoma office,to ganin yadda take kan lallabasa tasamu ya manta da tsinanniyan yarinyarnan shiyasa ta yarda yakoma Aranar,wanda daman shima ba aiki zai kaishi ba letter ya rubuta musu na barin aiki na dan wani lokaci ma”ana Leave without pay kenan,matukar razana ma”aikatar ta razana da ganin sakon mu”azzam ko abokan aikinsa sunyi sunyi sun janyesa daga kudurinsa yaki,yace musu zai tafi karo karatu ne,to ammh abunda yabasu mamaki shine ita da kanta ma”aikatar in taga chanchantar mutum takan Turashi da kanta karo ilimi ammh shi farat daya kuma lokaci daya yace zai tafi abunda da mamaki,babu yarda suka iya illah binsa da fatan alheri.

DON’T FORGET TO VOTE,COMMENT AND SHARE..It me Janafi
UWAR MIJINA…!
(Soyayyah,Sadaukarwa,hakuri tare da biyayyah mai tsanani)

       Mallakar:JANAF
       Wattpad:Janafnancy12

Dedicated to my blood Sisters JANAF

Intelligent writer’s Asso

Wannan Shafin kachokan mallakinku ne JANAF NOVELLA..mussaman masu sharhi,Fadila falalu maska(my Adila)????,My Ummu kursoom(Abulkursoom)????,my juwairiyyah Rogo❣,Mum khady(Kakata)????,Malika masoyiyata❤,Suwaiba Husna,Aisha,Fatima,Abida mahamood(Anty momi)????,Queen Aisha,Aysher,Safiyyah buhari
????, Raliya mk,zainab Abdullahi,Anty khadija,..Kunada yawa wanda baki bazai iya furtaku duka ba,ammh duk wanda ke cikin group din Na janaf novella,ina mika godiyata garesa Allah yabar zumunci da soyayyar na har abada

NOT EDITED????

                  NO 27

   Koda yadawo gida ko Afuska bai Nunama Ummi ba,illa ma biyemata dayayi sunata hira,ya warware kamar bashi ba,Ummi taji dadi rantayayi fari, tana fata Addu”artane taci na mu”azzam yafara manta da mayyar yarinyarnan data tafida kurwansa maiduguri.

    Washegari duk wani shiri nasa ya kammallah sa,kaya ko kala daya bai dauka ba,daga shi sai briefcase dinsa ya fito cikin shigansa na American Suit masu ruwan toka,ya mtse wuyansa da tie kafafunsa sanye cikin Rufaffun takalmana na fatar damusa,hannunsa kuma sanye da agogo na kamfanin Rado,fuskarsa babu Annuri ga idanunsa da suka kumbura saboda kukan daya sha jiya da daddare,har Ga Alla ba”a son ranshi zai yankema Ummi wannan Hukuncinba,domin tunda ya girma yayi wayau baitaba nesa da itaba,Tare suka rayu,akwai shakuwa da soyayyah ta uwa a tsakaninsu mai girma,wacce dalilin hakan yakeji kamar bai kyautama Ummi ba,ammh kuma zuciyarsa tana bukatar hutu,zaman agarin nan Tamkar dawo da hannun agogo bayane,zai Nesa da Ummi da kasar gabadaya ko zuciyarsa zata dawo da aiki daidai kamar yadda takeyi ada.

    Lokacin Da Ummi tayi Tozali da mu”azzam sai da gabanta yafadi ganin yadda idanunsa suka zurma,kallonsa tayi kafin tace,”Son meya sameka a ido ne?,naga sun chanza kalane..?”shafa sumar kansa yayi kafin yace”Babu komai Ummi,wani abu ne yafadamin a ido,dazu da zan dawo sallar Asuba..”yafada yana kallon kasa baiso ya kalli Ummi taga kwallar data taru a idanunsa.

  Bata dai yarda ba, sai ta rausayar dakai tace”Ayyah Srry muje kayi breakfast kafin kawuce kasan bansan zama da yunwa..”tafada tana riko hannunsa,dojewa yayi yaki binta waigowa tayi tana kallonsa kan tayi mgana ya rigata da cewa”Allah Ummi banajin saka komai abakina yanzu,but i promise u da na isa office zan sha tea..”Kuramai ido tayi ita duk sai taga yau ya chanzamata,bayason kallon kwayan idonta batasan dalili ba ,sai ta gyadamai kai tana fadin”Karka zauna da yunwa don Allah son u know ur condition ko.?.”

gyada mata kai yayi yana damke hannunta kafin yace”ki yafemin Ummi na…”yafada idanunsa sun kawo kwallah,matse hannunsa tayi kafin tace”Nayafemaka Duniya da lahira ibrahim,da laifin daka aikatamin da gangan da wanda ka aikatamin cikin rashin sani duk na yafemaka su har abada..”jin abunda tafada yasashi fadawa jikinta kuka na neman kwacemai Rumgunesa tayi tana fadin”Shiii..insha Allahu kukan ka ya kare son kaji..”Tafada tana shafa bayanshi,kokarin dannen kukansa yake,ammh hakan ya gagarara sai da ya sakarma Ummi wacce ta razana da yadda ya kamkameta yana kuka,ammh sai tayi la”akari da abunda yafaru,ta hau lallashinsa da bashi baki,har yayi shuru,ita da kanta ta rakasa har bakin mota ta budemai ya shiga kafin Tarufe tana mai addu’an adawo lafiya har motarsu ta fice daga gidan.

Suna Fita mu”azzam ya Runtse ido yana fadin”Ki yafemin Ummina…”yafada wasu zafafan hawaye na zubomasa kafin ya sanya hannu ya share basuyi wani nisa ba ya umarci Ushe daya paka motar cikin mamaki ya samu waje yayi parking fitowa mu”azzam yayi tare da briefcase din dake hannunsa ya mikama ushe wata marar takarda yana fadin”gida zaka koma,ka kaima Ummi wannan takardan, na manta ban bata ba kafin mu Fito,kada kadamu dani zan hau Taxi na karisa..”yafada cikin bada Umarni.

   Ushe da mamaki ya sandarar dashi don tunda yake tuka yallabai haka bata taba Faruwa ba, ko mantuwa yayi sai dai ya maidosa ya dauko,ammh yau gabadaya yallabai ya chanza kamar wani bakon al”amari keson Faruwa dashi,Jikinsa a sanyaye ya karba yana fadin”Ammh yallabai daka bari na dawo sai mu karisa tare..”hannu mu”azzam yadagamai da cewa”Karka damu zan karisa,kai dai kayi hanzarin kaima Ummi sakon dana baka..”

Badon Ushe yagama yarda ba yafada mota yayi Reverse,yakoma hanyar gida,sai dabMu”azzam yaga kulewan Ushe kafin ya juya yana dauke hawayen idonsa,Karamin siririn glass din dake makale gefen aljihun rigarsa ya ciro ya saka,kan ya saka hannu ya tsaida Keke napep din daketa wucewa,nan da nan ko daya ya tsaya batare da bata lokaci ba yace”Airport zaka kaini..”hau muje yallabai..”yabashi amsa,Cikin azama yafada ciki,mai keken yaja suka fara Tafiya,basu wani jima ba,mu”azzam ya zaro wayarsa ya ciro layin dake ciki, ya saka abaki ya Tauneshi kafin ya Furzar dashi ta waje,ya kashe wayar gabadaya ya maidata aljihu.

  Tafiyan minti talatin ta sadasu da Airport din ya sauka ya biyashi kudinsa ya karisa cikin Airport din,yana zuwa kuwa yasamu Jirgin da zai Tashi nan dan lokaci shine wanda zai yada zango a lagos,bayason bata lokaci nan da nan ya siya Tikiti yazauna zaman jira,domin ya kagara yafara nisa da garin Abuja,sai duba agogon Fatar dake hannunsa yake bayan kowani dakika.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button