NOVELSUWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL

UWAR MIJINAH COMPLETE HAUSA NOVEL BY JANAF

Zahirah kuwa tana daga kwance tun sadda Dr Abduljabar yace wai tana da ciki taji gabadaya Na”urorin jikinta sun daina aiki gabadaya jikinta ya Hau rawa,ciki kuma ita ke da ciki? Ummi..? tafado mata arai sai da jikinta ya amsa saboda razana tuni ta tattara duka karfinta ta saki wani marayan kuka mai tada hankalin wanda yaji.

Atare Mu”azzam da Dr.Abduljabar suka isa gareta suna tambayanta lafiya,mu”azzzam Rumgumeta yayi yana fadin”My Hirah Allah ne kadai zai iya biyanki dukkan alkhairinki gareni,Ubangiji yasa kigama da duniya lafiya kingamamin komai tunda zaki haifamin yara..”Yafada yana shafa maranta,buge hannunsa tayi tana kuka take fadin”wlh bazan zauna da cikin nan ba.’tafada da karfi galala mu”azzam yayi yana kallonta bayan yadago ya kalli Dr Abduljabar baisamu zarafin mgana ba tacigaba da cewa”Wlh in Ummi taji lbri yankani zatayi ya Mu”azzam don girman Allah ka rufamana Asiri kasa azubarmin da cikin nan don Allah…”
tafada cikin ban Tsausayi tuni mu”azzam ya fahimci inda zencenta ya dosa kallon Dr yayi yana fadin”Plz Dr dan bani guri nayi mgana da ita..”Rausayar kai kawai Dr.Abduljabar yayi yana fadin”Ok.

Bayan Fitansa Mu”azzam yakurama zahirah ido yana kallon yadda take kuka,matsowa yayi yana riko hannunta yace”Zahirah..”Yakira sunanta cikin muryan amo dago kanta tayi hawaye jabe jabe bisa fuskarta,kawai sai taga mu”azzam yayi durkuso da gwiwowinsa bakin gadon Stil hannunta na cikin nashi..Yafara mgana cikin wata murya mai tsuma duk mai sauraro.

“Haba Zahirah,ashe zaki iya butulcema Allah game da kyautar daya tsamo mu acikin dubu yayi mana ita,karki manta nikadai Ummi tahaifa agidan Duniya,baki Tunani dalilin wannan cikin Ummi tayi alfahari damu gabadaya..’yafada yana kallon cikin idanunta.

Damke ido tayi hawaye suka gangaro mata,tace cikin shakakkiyan murya..”Nima zan so haka ya Mu”azzam don akullum burina Ummi ta yafema mahaifiyata to ammh Wlh Ummi bazata taba kyalemu ba,baza ta barmu ba, in tagano ina da ciki,kamanta tace zata iya yankani ko mgana takamani inayi dakai,to balle kuma ciki,ciki ma na haihuwa,wlh inajin tsoro inajin Tsoro ya mu”azzam”Tafada tana kara damke hannunsa tana kuka da Sauri ya mike ya rumgumeta yana fadin”Babu abunda ta isa ta miki indai ina raye,wlh tallahi Zahirah na shirya fito na fito ga duk wanda zaiyi yunkurin salwantar min da gudan jinina koda kuwa UMMIN CE DA KANTA..'”yafada cikin zafin Zuciya dagowa tayi tana kallonsa yadda zuciyarsa ke harbawa sai da gabanta yafadi ta runtse ido takara lafewa bisa jikinsa tana ji ajikinta akwai babban aiki agabansu.

Sai yammah kana Dr Abduljabar ya sallameta bayan ya rubuta mata magungunan karin jinin,kuma yace banda aiki mai Nauyi,kana tacigaba da cin abincinta it normal babu,komai Brr yana mai godiya suka baro asibitin zuwa gida,ko amota shuru sukayi kowanne na saka abunda ke ransa.

Ushe ya dannan Hon maigadi yazo ya bude musu suka sulala zuwa cikin gidan,a parking space ya faka motar,mu”azzam shiya kamo Zahirah saboda haryanzu jikinta babu kwari,suna gabda shiga falon,ta kwace jikinta bakinta na rawa take fadin”Um.mii….”Kallonta yayi kan yayi mgana ma tayi gaba tana layi kamar zata fadi, Take mata baya yayi suna shiga falo suka ko ci karo da Ummi,wacce ke hakimce kan kujera ta dora kafa daya kan daya tana binsu da kallon raini,Dukawa zahirah tayi tana fadin”Ina yini Ummi..”Tafada dakyar saboda yadda jiri ke dibanta,a kaikace ta kalleta kafin tace”Da ban wuni ba dabaki ganni ba,har saunawa zance in ina zaune kidaina zuwarmim gaba da sunan gaishe ni.”Tafada tana hararanta kan tace”Tashi ki bani waje kafin ki batamin mood dina…”Mikewa tayi a hanzarce zata wuce kawai jiri ya kwasheta tayi luuu..Zata fadi sai ji tayi ta fada jikin mu”azzam yana fadin”Kiyi fa hankali…’yafada cikin kulawa.

Ummi dake zaune sai ta daskare a zaune Da hanzari ta mike tana fadin’Kai don kaniyarka mai zan gani,..Ehe..’?”Tafada cikin tsawa gyara tsayuwa yayi bayan ya saketa yana fadin”Zaki iya tafiya zuwa daki..”Gyada mishi kai kawai tayi ya saketa ahankali ta taka ta shige daki,Ummi dake tsaye tayi wani kukan kura isa gabansa sai ji yayi ta daki kafadansa tana fadin’Kaci ubanka,ina mgana kana jina kana cigaba da yi kuma,yaushe kafara kula ma wannan yarinyar ne.”Dafe kansa yayi yana Fadin’oh my god haba ummi wai bazama ki tambayi meyafaru ba tukun nan ba sai fada kikeman…”Yafada shima cikin Fushi.

Ganin ya hasala ne yasa ta sassauta murya tana fadin”Shine ai na tambayeka ko” bata rai yayi yana kama hanyar shashenshi yace’bata da lafiyane nima daga mkrantarsu aka kira ni nazo na dauketa a asibiti ta wuni dawowarmu kenan..”tsaki Ummi taja tana fadin”mtseeaww..To tama mutu mana uban wa ya damu,karkadai sake riketa kaji ma na fadamaka in ba so kake na saba maka acikin gidan nan ba,kaji ko baka ji ba..”Naji..”Yabata amsa rai babu dadi yayi shigewarsa ciki ya barta nan tana ta fadanta tana fadin”Shegiyar yarinya ta iya makirci harda wani yi baya zata fadi,ai da kabar banza ta fadi naga wanda zai damu..”Haka taitayi kafin takoma ta cigaba da kallonta.

Zahirah ko na shiga daki ta koma ta kwanta saboda jikinta babu karfi kwata,kwata tana kwance babu mataimaki sai Allah dakyar ta iya rarrafawa tayi sallolin dake kanta ta bude fridge ta dauko sauran ice cream dinta tasha kafin takoma ta kwanta tana tsausayama kanta domin bata hango nasaran Da ya mu”azzam ke fadin yana hangowa game da Ummi ba domin kwata kwata abun na Ummi cigaba yake ba ci ba baya ba.

Shiko mu”azzam yana daki ammh zahiran tana ransa,koda yadawo sallar mangariba Ummi ta haura sama yin sallah shiyabashi daman shiga dakin zahirah tana kwance idonta biyu zama yayi kusa da ita yana riko hannunta dagowa tayi ta kallesa idonta ya ciko da hawaye sharemata yahau yi yana fadin’Kiyi hakuri My hirah insha Allahu komai yakusa zuwa karshe kinji ko..”Dagamasa kai tayi kafin ta wuce zuwa kirjinsa rumgumeta yayi yana ransa na kuna,ace baida ikon kula da gudan jininsa sai aboye,shida kanshi yaje gun su karime ya karbo mata abinci yazo ya bata taci tasha mgani tare sukayi jam”in sallar issha”i gabadaya ya kashe wayoyinsa ya rumgume yar matarsa suka kwanta ya cire tsoro aransa duk da yasan Ummi bata shigowa dakin zahirah.

Itako Ummi,batama karabi takansu ba,kanta ne ya mtsamata da ciwo tasha paracetamol ta kwanta kuma takira wayar mu”azzam din akashe kawai sai ta kyalesa bataso tafadamai hankalinsa ya tashi,itama da wuri ta kwanta bata nemi,kowa ba.

Ko washegarima hakan ne ta faru mu”azzam shi yayima zahirah wanka ya shiryata shi yabata breakfast dinta abaki yabata magungunan yakaita bisa gado yarufeta da blanket yace tayi barci don likita yace ta rinka samun hutu kafin ya barta yaje dakinsa ya shirya kafin ya wuce sai da ya haura saman Ummi nan take fadamai da ciwon kai ta kwana cikin rudewa ya hau yimata sannu da tambayan jikin nata da sauki tace,da yaso tazo su tafi asibiti ammh tace taji sauki dole ya kyaleta,har bakin motarsa ta rakosa tana mai fatan dawowa lafiya.

Saboda zahirah karfe2 ya dawo gidan saboda bai bar ma kowa sallahu ba,shiyasa ya dawo wannan karon ma shiyabata abinci yakuma bata mgani kafin yaje ya kira karime ya zaunar da ita tunda tamkar Ummi yake kallonta yafadamata abunda ke faruwa,yakuma damkamata amanar kula da zahirah da abunda ke cikinta,bayan ya gargadeta da karta fadama kowa,ko su uwani baice tafadamawa ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button