SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL
SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:32 – ????????????: Ranan sai na wuni sukuku ina tunanen zancen mu da Amma wanda bata fito fili ta baiyana min shi a baiyane ba amma daga baya da muka zauna da murja mukai maganan sai na fahinci hjyn su yaya tana farautan rayuwana da rayuwan aurena ne ashe wanda hakan yake yawan haddasa min mafalkin su ko wani lokaci.
Saidai magana irin wanan bai taba shiga tsakanina da yaya ba ko kadan sai yanzu da nake jin zancen a bakin Amma.
Abinda dai na sani da wuya ayi sati daya banyi wanan mumunan mafalkin ba da ita wanda sai yanzu naba abin ma,ana.
Idan hakane ai garama ta raba auren da takeso ta barni da lafiyana zaifi min sauki don duk ranan da nai mafalkin haka zamu kwana rikice da yaya wani lokaci kuma shine maiyin mafalkin bani ba.
Dabi,ana ne bana fitowa gajal sai na dan gyara jikina kuma ban wuce takwas na safe banyi wanka har yara mun kitsa jikin mu har yan aikina bazaka zo gudan ka samay mu ba dadin gani ba komai sammako mutum kuwa.
Ina shirin fitowa yaya ya shigo dakina da sauri yana fadin zarah fito ga kawun ki yau gidan mu.
Kawu na ambata a fili ina mamaki yace harda su baba balarabe ai kin san dole suzo gidan nan tunda na dauko masu tsohuwar su ai.
Da sauri na biyo bayan shi zuwa falo inda muke jin hayaniyar su suna dararaku a lokacin.
Fitowan mu yasa suka dan tsagaita suka mayar da hankalin su garemu a cikin kunya nakai wurin tare da tsunguna kasa ina gaida su kawu gaba daya su.
Kawu balarabe ne ke fadin gamu mun biyo ku tunda ku bakuje gaida mu ba umar baka san gidan mu ba balle iyalin ka yanzun kuma ka dauko muna uwa zuwa gidan ka.
Yana dan dariya yace baba ba dauke ta nayi ba muma nan muna da bukatantane na dan lokaci a tare da mu.
Ja,iri abinda zai fada maku ke nan ai ya daukoni ya kawoni nan ko tana bana gani sai dadi yake cika min a cikina ba dare ba rana ko nayi barci sai yaron nan ya tayar dani ya bani naci.
Dariya suka kwashe dashi kawu mustapha yace Amma ai hajiya kin canza gaba daya wallahi da gani ba sai kin fada ba.
Daki na mike na shiga na fito da yaran dukan su na kawo su wurin su kawu har yanzu basu son sake jiki da kowa a ckin dabara suka koma jikin mahaifi su suka kara makaleshi.
Allah ya albarkaci zuria kawu balarabe yace yara haka tubarkalla masha Allah yau ina jummai dataga wa yan nan yaran da ina zata kai alhakin hana auren da taso yi nasu.
Kai ke nan da kasan wanan kake fadin haka Amma tace don ita har yanzu ba wai ta saduda bane ta bangaren ta.
Har yanzu tana kan bakan ta ke nan kawu mustapha ya tambaya da mamaki.
Ta nan wallahi yanzu haka halin da ake ciki akan matsen lamba take kan sai yaron nan ya saki yar nan bata barsu hakan ba ta kwashi maganan komai ta fada masu hankalin su ya tashi matuka da jin wanan maganan.
A hankali na mike na bar gurin don ba zan iya jin kalamin su na manya akan sarakuwar tawa ga dan ta a gurin ya dukar da kanshi kasa yana nuna yanayin rashin jin dadi ga kalaman da ake mata din lokacin.
Kawu sani ma baiyi magana ba a lokacin shiru yayi kamar mai nazari a zuciyar shi.
Barina gurin shima ya mike tare da yaran shi zuwa hanyar waje abinsha na umurci mai aikin mu ta kawo masu da dan abin motsa baki duk da safiyane sosai a lokacin.
Kwana biyu da zuwan su kawu gidan mu muka shirya zuwa ziyaran yan uwa damu dashine gaba sai sultana dana rike su Abdul suna baya tare da maria da murja sai Amma.
Ziyaran yayi kyau sosai don yaya yaiwa dagi alheri sosai a wanan dan ziyaran da mukai masu lokacin kayan mu sun iso na rabawa kowa daya dace a cikin dangi tsaraba har wanda ban zataba saida ya samu alokacin.
Ranan da Amma ta cika sati uku muka mayar da ita gida tunda safe kowa sai yaba kyawon da Amma tayi a gidan mu akeyi.
A nan ya wuce ya barmu zan wuni sai dare zai dawo ya dauke mu yace a part din Amma muka yada zango kafin in koma wurin mamu in zauna.
Tare da maria mukazo don laluran yaran na shiga wurin hjyn su yaya na gaida ita muka dan zauna ta barmu nan zaune falo nida yara da maria ta shige daki daga ita har nafisa.
Sai dan autan su yayane ya zauna tare damu yana hira tare da kulawa da yaran karshe dai da zaman ya ishe mu naga hjy bata da niyar bamu lokacin tane na fito na koma wurin Amma daga baya kuma na dawo wurin mamu.
Har akai sallah azahar mukaci abinci ashe hakan danayi kuma wai ya batawa hjy rai matar da anan ta barmu zaune taki kulamu ko yan jikokin nata bata kalla ba balleni da maria.
Sai bayan la,asar yaya ya shigo gidan direct wurin mahaifiyar shi ya nufa inda ya samu ta cika ta hau tayi fam dani.
Yana zama yake tambaya nafisa zarah fa tana inane wai ?
Uwar ta kalleshi tace wa zaka tambaya ita a nan tunda ba wurin mu tazo ba tana gurin uwarta mana yaran da kake kira da jikokina ina zata yarda su rabeni tunda a na daukana mai mugun hali.
Mugun hali kamar ya mama ko ya kike ai bata isa ta rabaki da yan jikokin ba yanzu ni ba gashi amma yau ji nayi kamar kada ta dawo na ba.
Ina ji da kunnuwa yaran nan suna tambayar ta kakasu tace bani bace kakarsu tana can part din ta tana rikesu kada suzo wurina a gaban idona ta nuna min banda hadin komai da yaranta yanzu.
A hasale ya mike bai gama sauraren ta tana fadin ina kuma zaka yanzu iyayyenta su taru suce ban kaunar zaman lafiyan ka da matarka.
To amma mama daidaine ta shigo gidan nan ta hana yaran nan zama a wurin ki bazan taba lamuntar hakaba gaskiya ko ina hakkuri da komai ba zan iya daukan wanan ba gaskiya.
Na daice ka barta harku koma gida kuyi shi can don gaskiya abin bai mun dadi ba nima amma tunda kai kaji ka gani kan zama da ita yaya zanyi da kai.
Ya kalli mahaifiyar rai bace kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru ba tare da ya furta komai ba ya zauna ya dan jima zaune ya mike yana mata sallama.
Kofan part din mamu ya tsaya ya tura dan wurin hjy maryam ya kirani yaron ya shigo ya gayar damu muna zaune ana hira yake fadin ga yayan mu a waje yace ki fito ku tafi.
In fito mu tafi shida yace sai dare zamu tafi kuma na taso na leka har ya fara tafiya nace yaya ya waigo kace mu fito kuma eh kawai yace yaci gaba da tafiyan shi.
Dan jim nayi ina nazarin shi kafin in koma ciki rai bace nacewa maria ku taso mu tafi yana jiran mu a waje don maria taji dadin zuwan mu gidan ta sake sosai a gidan.
A mota muka samay shi zaune yana jiran mu har muka shiga yaran na surutu bai kula su ba nidai naja bakina nayi shiru ban tanka masu ba.
Muna isa gidan ganin yanayin da yake yasa ban tsaya falo ba na wuce zuwa cikin dakina don nasan halin shi idan yai fushi baison aimai magana lokacin.
Muryashi naji a bayana yana fadin meya hanaki shiga dakin mama ki zauna da yara ?
Na juyo da mamaki jin abinda ya fadi nace waya fada ma ban shiga na gaida ita ba ?
Wani lalataccen kallo ya jefini dashi kafin yace za, ai maki karyane kike son fada min ko may ?
Sai maganan ya bani mamaki kafin kuma ya bata min rai saidai na danne nace hummm wani sabon sheri da munafunci kuma ake kokarin kulla min ko may ?
Ai ba munafunci da sheri ya kamata ai min ba kamata yayi ace ban kai karshen magana naba naji ya kwasheni da wani gigitacen mari a fuskana saida na duka don zafi.
Kafin yace ke har rashin kunyar taki yakai ki kalli idona ki karyata mama a gabana har kina kokarin zagin ta.
Na dago ina dafe da gefen fuskana inda ya mare ni ina watsa mashi kallon tsana karara idona yana fitar da hawaye.
Yaci gaba da fadi a daidai lokacin da Abdulsalam dake bayan shi ya yanka wani irin ihu shi kuma yana fadin .
Don kawai kina dauka ina auren ki yanzu sai ki zagi mahaifiyata a gabana har kina kokarin karyata karya zatai maki komay ?
Jin ihun Abdulsalam ya jawo hankalin sauran gaba daya sukayo kanmu suna kuka lokaci guda sultana ta kankameni tana wani irin ihu.
Nace ka maraini yaya ba tare da ka tsaya kayi bincike kan wanan maganan ba na barka da Allah wallahi dakai da duk wanda ya zugoka a kaina.
Bai tsaya ko kallon yaran ba ya juya ya barmu a gurin tsaye muna kuka muryan maria naji tana fadin madam mai yayi zafi haka yau tsakanin ki da Oga ?
Kallon ta nayi na juya zuwa dakina rike da hannun yarana dake kuka har akai magariba ban fito ba har yaran sai maria dake sintiri don laluran yara a lokacin.
Faisal autan su yaya ya shigo yana sallama ga tv na aiki a falon saidai babu kowa a gidan ganin haka ya juya zai wuce sai ga yaya ya fito daga dakin shi zai tafi masallaci ya ganshi.
Jin motsin fitowa ya juyo yana gannin yayan nasa ya fara gaida shi tare da fadin anty Fatima fa da su Abdul dazu sunce in sayo masu ball na dawo gida shine na samu ance sun wuce shine na kawo masu yanzu.
Kallin yaron da suke da shigen yanayi daya yayi yana fadin suna ciki wurin maman su ina gani daga nan ya tsaya yana kwallawa maria kira ta amsa don tana dakin su dama.
Kafin maria tazo faisal da bai san kaiba yaci gaba da fadin tare suka so muje don kada kai fada yasa ban fita dasu ba sai na barsu nace su bari naje na sayo masu ai.
Don mun dade falon mama tare dasu suna min hira yau ya juyo ya dubi yaron yace falon wa kace yace falon mu muka zauna dasu da maman su.
Mama fa ya tambayi yaron mama kyalesu tayi ita da Nafisa suka shige daki nima banso hakan da mama tayiwa anty Fatiman ba wallahi na bita daki nace sun barsu zaune su kaidai ta koreni.
Muje muyi sallah yace wa yaron yayin da cikin rashi yake maimaita innalliallahi a zuciyar shi.
Amsan ball din maria tayi tana godiya tare sukai sallah a masallacin unguwan inda yaiwa yaron fada yabar kaiwa dare a waje hakana kafin yace driver shi ya kaishi gida bayan yaba yaron kudi da murna yana godiya ya tafi.
Inda na idar da sallah na zauna ina tunane idan har hjy ta fara cin galaba akan danta zata iya fada mai magana ya yarda dashi a yanzu ashe kuwa aiki babba ya ganni a gabana.
Shine ya turo kofan ya shigo udon shi ya sauka kan sultana dake kasa yashe tana barci a gurin tayi kukan in dauketa naki na tayar da sallah lokacin sai tayi barci.
Daukan yarinyar yayi tsab zuwa kan gadona ya ajeta ya dawo saman kujeran dake gefena ya zauna.
Ya dan dauki lokaci kamar ba zaiyi magana ba can ya dago tare da ajiyan zuciya yace cikin natsuwa zarah na fada maki tun bamuzo kasan nan ba .
Na rokeki cewa ki mutunta min kowa nawa da yake nawa kamar yadda nima zan mutunta kowa naki kamar yadda ni kike mutuntani da aurena.
Sai lokacin na dago kai nace wana taba yiwa rashin mutunci a gidan mu kaf ko bayanzu ba sai wanda yaso raina min wayau ko shi sai yara yan uwana zakace na taba wani tashin hankali dasu.
Ya murmusa yace amma dai kin san tun farko inda maganan nan ya fito har zaki tsaya gabana kina kokarin karyata min mahaifiyar data haifeni a gaban idona.
Nace yanzu kuma ai ya saura gare ka don ban zama ko yaushe dan magana kadan ya hadamu ka daga hannu ka mareni ko a gaban waye .
Ni nagaji wallahi na gaji ba zan iya irin wanan zaman ba wallahi da kaje an fada ma magana baka tsayawa kayi bincike sai kawai ka daga hannu ka mareni .
Idan ke kin gaji ni ba zan taba gajiya dake ba raini ne kawai ga kowa ba zan iya dauka ba don gaba ki sani ban raina maki naki mahaifan ba bako zan yarda ki raina min nawa ba.
Raini kuma na nawa ne ba aiwa mahaifiyata ba ina ji ina gani tunda muka zo sau nawa ka shiga ka gaida ita.
Kumani data haifa kana kokarin hanani zumunci da nawa iyayyen .
Yayi murmushi ya mike tare da fadin komai zaki iya fadi yanzu ai saidai dadin abin ita maman taki tasan ban taba rainata ko mata wani abin bacin raiba.
Don haka kema nake rokon ki akan ki kara yin taka tsantsan da duk wani abinda zai jawo mama tace maki kinyi mata laifi ko wani abu da har za a iya tunzurani a kanki
Don nasha fada maki cewa kimin adalci don ni din na mijine namiji kuma yana nufin zan iya juyawa daga matsayina in koma wani matsayi a gareki don haka nake kara fada maki ki bini a sannu.
Ya mike ya fita tare da kallin yaran dake ta barcin su saman gadona hankalin su kwance ya fice daga dakin zuciyar shi tana mashi kuna.
Yana fita nakai kallona ga yaran dake kwance suna barci tausayin su ya kamani a lokaci guda ban san lokacin da wasu hawaye masu dumi suka kara sauko min a idanuwana ba.
Ina kuka ina tunanen sakani gaban da hjy tasha alwashin yi taga bayan aurena da danta yanzu in haka ya tabbata yaya makomar diyana zai koma don nasan karshe dai karbe yaran za,ayi daga hannuna abawa hjy don babu mai rikesu sai ita.
Haka muka zauna kusan kwanaki kowa sai harkan gaban shi yake a cikin mu iyakarshi in ya shigo ko kafin ya fita yaba yaran shi kulawa kamar yadda ya saba basu koda ina zaune bai kulawa da ni kamar yadda nima na dauko share shi din.
Ranan da safe ya shigo dakina ina kwace muna waya da Aisha ina ganin shi na cewa Aisha zan kirata anjima na dan juya wurin shi a gyatsire na gaida shi da kwana ya amsa ba yabo ba fallasa tare da fadin zanje lagos yau ina ganin zan kwana biyu a can .
Don haka ki kula da gida da yaran nan yasa hannu cikin aljihun riganshi ta ciki ya ciro kudi yana miko min tare da fadin wanan ki rike a hannun ki ko wani abin zai iya tasowa bana gida.
Da ka barshi tunda komai muna dashi yace na sani ki dai rike wanan din a wurin ki nace na mika hannu na karba tare da fadin Allah ya tsare.
Har yakai kofa nace yaushe zani bauchine ganin su yanzu muna batun share wata daya da wani abu a kasan nan fa.
Idan na shirya zan fada maki in lokaci yayi ya fada yana fita daga dakin ganin bai gari yasa na kira murja mu zauna tare da ita don bata son zuwa idan yana nan bansan may yasa haka ba.
Da rana muna zaune sai ga salma tazo muka gaisa take tambayan yayan nata nace yai tafiya a ranan.
Sai naga bataji dadin hakan ba bata dai fada min komai ba nan muka zauna da ita mukai hira taci abincin rana tare damu.
Saida tayi sallah tace zata tafi nace ta bari in kira driver gidan ya mayar da ita gida na tashi na shiga daki dubu hamsin na kidaya daga cikin kudin daya barmuna na hada mata da yan abubuwa na saka a leda .
Lokacin dana rakota namika mata kudin da kayan saida naji tayi wani irin ajiyan zuciya tana fadin Fatima nagode yau kin rufa min asiri wallahi don ba karamin dadin wanan kyautar naki naji ba.
Saboda may anty salma na tambaye ta tace kinsan halin mazan nan yanzu buki ake dashi can garin su dama na kannesa shine nake son dama indan rike wani abu kada in tafi hakana hannu sake.
Yanzu kinga zan dan samu na rikewa saura har in samu indanyi dinki a ciki.
Wani irin abu naji ya dira min a zuciyana nace anty salma kina nufin shi yaya Ahmed ba zai maki wa yan nan abubuwan ba ta danyi murmushi tana fadin fatima ke dai Allah ya sauwaka yanzu ko namiji yana maka idan baka dashi ga hannu ai ragagene.
Karatun nan fatima yaya ya tsaya muna saida mukayi shi muka gama aiki dai ne yanzu ya zama fitina kuma don shi na gidana ya rantse ba zai barni inyi aikin gwaunati ba.
Jin hakan shima mijin ikilima yace itama ba zatayi ba nace anty salma haka yaya Ahmed ya koma kuma.
Tace bari kawai Fatima ina da maganganu da yawa danaso mu zauna muyi dake saidai ko wani zuwa nayi bamu samun lokaci.
Kada ki damu anty salma zanzo har gidan in samay ki mu tatauna sai dai yanzu barin zo na koma ciki na kara fitowa da wani ledan turama a hannu na kawo mata tana batun yin godiya nayi saurin bude mata motar ta shiga ina fadin ta bari sai munyi waya da ita.
Nan ta tafi ta barmu cikin tashin hankali ta barni da tunane kala kala a raina ranan