NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:07 – ????????????: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM HASBUNALLAHU WANI,IMAL WAKEEL, , , ,

Yana tsaye daga kofan falon da waya a hannun shi yanayi ya tsura muna ido da mamaki yake kallon rawan da mukeyi din duk mun shagala mun buge da rawa bamun ya dawo ciki ba a lokacin.
Merry sai tafa muna take da hannayen ta duka biyu a hankali ya tako zuwa wurin remote din ya dauka ya kashe kidan.
Gaba daya muka mike muna mamakin abinda ya tsayar da kidan kuma juyowan nan da zamuyi mukai arba dashi ya daure fuska tamau kamar bai taba dariya ba a rayuwan shi.
Merry ta tako zuwa gare shi tana fadin why dear zaka kashe muna redio muna enjoyed din kan mu zuwan yaran nan gidan nan yasani yau na shiga nishadin da tun zuwa mm a kasan nan ban taba shigar shi ba tana magana tana kokarin kwanci saman kafadan shi.
Dan ture merry yayi ya yana fadin why merry why kin san hakan mu ba al,adan mu bane zaki saka yaran nan rawa kija muna hatering gun iyayyena.
Rawan kawai na nishadi da suke tayani yi diya bafa gun fati naje dasu ba da kake wanan maganan haka ya kara daga mata hannun yatare da fadin please, .
Daga haka ya shige ciki ya barmu zaune tsuru tsuru muna boye fuska ni dai kasa wani mosti nayi tunda na samu na saka hijjab dina a jikina na dunkule bayan Aisha.
Ina ganin merry ta bishi nace ku tashi mu fice don Allah kun jawa mutane abin kunya Aisha duk jece kika jawo min haka wallahi na fada a dan hasale.
Merry ta fito da dan murmushi a fuskanta tana fadin mu saki jikin mu nan fa gidan dan uwan mu ne taga mun tsorace dashi ta kai zaune tana fadin shi haka yake baison abin jin dadi a rayuwan shi sai idan shi yaso.
Can sai gashi ya fito bai ko kalli inda muke ba har yakai kofa ya dan juyo yana fadin ku fito in sauke ku gida idan kun tashi.
D way yadda yai maganan umurni yake bamu kowan mu ta mike da sauri muna shirin tafiya merry mamaki ya kamata ta take fadin don may zaka kore min abokan nishadina kuma kai ba zama zakayi a gidan ba.
Bai kulata ba sai ficewa yayi daga gidan mukan har mun daga kowa na kokatin daukan jakkan shi nidai hannun fauziya na riko muka fito tana biye damu da tikeken cikin ta a baya tana fada dashi.
Yana cikin motar dake rufe lif a lokacin muka karaso wurin motar muka tsaya ya sauke glass din motar yana fadin kanwata zagayo ki shigo nan gaba wurina da cewan fauziya don ita yake kallo yana magana.
Ban san lokacin da bakina yace zamu iya karasawa gida ai ba nisa don islamiyan mu ma yana gaba da nan.
Shoutup ban tambaye ki ra,ayin ku ba yace da sauri na rufe bakina muka fada bayan motar da tsoro da mamakin shi ashe yana iyawa matar shi haka yadda nake ganin su a soye kullun.
Maimakon ya mike damu hanyar gida sai ya dauki hanyar da zai fitar damu daga unguwar gaba daya.
Kallon kallo muka fara yi kasa kasa na radawa Aisha da ido ina kuma zai tafi damu haka ?
Sai muryan shi mukaji yana fadin sayar daku zanyi kin san ni dan yankan kaine ai ko baki sani ba yace ba tare daya juyo ya kalle mu ba.
Sai ya ja tsuki yaci gaba da tukin motar shi shiru na wani dan lokaci yace idan ni ba kafiri bane aike da kika buge da rawa yanzu kin dauki hanyar zama kafiran sallon kuje gida ku fada kunyi rawa a gidana ace zata koya maku kafirci.
Duk wanda naji wanan maganan a bakin shi sai na bata maku rai dukan ku baku san halina ba ko ?
Kina wani boyewa a cikin wanan abin kullun ashe shedaniya ce ke ko bai fada ba nasan dani yake fada nidake cikin hijab din ya kama ina rawan shakiyanci.
Ya furzo da iska daga bakin shi ta yadda muke iya jin sa bai kara magana ba sai daya tsaya a bakin wani katafaren shago da akaiwa manyan haruffa rubutu.
Ina dan kallo wurin naji yacewa fauziya barin maku tsaraba kuje dashi gida ko yana kallonta tare da fadin wa yan nan yan shagalan sun kwaso ki sun barki zaune.
Ya fita ya zagayo ya budewa yarinyar nata bangaren ya rike mata hannun suka fara tafiya a nan ya barmu zaune tsuru tsuru a cikin motar.
Murja ta fara magana tace ashe gaskiyar fatima da ki kace bahagon mutum ne sosai gashi ko ya nuna muna yau din.
Ni wallahi da nasan yana nan da banyi rawa ba har ya zargemu wai muna karya da uztazanci a fili.
Shiru nayi ban iya furta komai ba sai lokacin da naji Aisha ta fadi hakan na dago kai daga kallon wajen da nakeyi nace bafa daku yake ba dani agolan gidan su yake kukan ai kannen sa ne bai maku fada .
Ba yazo ya samay ku da farko kuna rawan ba baiyi fadan ba sai Aisha tace ke kila fa don yaga yadda mumun ku da hjy su suke yasa yayi gudun fitina.
Muna nan ciki zaune sai ga wani yazo da uniform din wurin yana fadin wai ance ku fito ku shiga daga ciki yana fadi ya juya abin shi.
Bin mutumin nayi da kallo sai kuma na juyo nace ku shiga ni ba inda zanje Allah.
Kallona sukayi kawai kafin suce mukan zamu shiga mu dibi rabon mu suna fita zuciyana ta bani in bisu muga gudun shi.
Da sauri na samay su har sun tura kofan sun shiga nima nabisu yana rike da hannun fauziya yace kowa ta dauki duk abinda take so.
Tsayawa mukayi muna shawara a tsakanin mu kunga mu dauki biscuit da sweet kawai koda bibiyu ne kada yaga haukan mu ko muyi kauyanci nace enyyeh kawai.
Ban tsaya ko inaba danaga sun nufi sashen kayan zaki nikan na nufi sashen wasu kaya dana hango.
Dogayen riguna mai tsaron wurin yana ganina ya taso yana fadin hjy a tayaki dubawa ne nace eh kawai nan ya shiga zakalo dogayen riguna masu tsadan gaske har guda biyar.
Nace sun isa na nufi gurin turamay nace ya zaba min ya dauko masu tsada gaske ni dai ban hana ba guda hudu na zaba nace ya saka a basket din ya bini da kallon mamaki na fuske sosai.
Sai na koma wurin turare da man shafi ina dubawa nan ma mai tsaro yace bari na zaba maki daidai da jikin ki ya zabar min turare masu tsadan gaske da kamshi na juya kowa sai kallona yake yana mamaki.
Daga haka na nufi gurin mai lissafi nan na samay su harshi suna jirana Aisha da murja suna ganina ido waje sun bude baki suna kallona da mamaki na iso inda suke tsaye.
Kallon kayan Aisha tayi tace A ruwa nace A wuta dan Allah niki kyale ni kin ji tace cewa fa yayi abinda muke so nace ai shine na dauko wanda nake so din tunda raina yana so.
Yana jin mu baiko kalli inda muke ba sai mai lissafin yace oya hajiya ina naki na tura mai basket din na ja baya sai da acounter din ya dago kai ya kalle ni ya girgiza kai yana dariya.
Ni dai na fuske ya buga tare da dago kai ya kalleshi yace 2,2500 a cikin rashin damuwa da komai ya mika mai dan kati naga sun cire ana saka kayan a leda.
Nace kai an saye duka ne ya dago kai yace har an biya ai hajiya sai kuma tsoro ya kamani dan ni ba haka na shirya a raina ba.
Naso yace don may na dauko wanan kayan kamar mara hankali ince bakai kace in dauki abinda nake so ba sai kuma aka samu akasin hakan ni yanzu may zance a gida idan mun koma.
Amma wallahi A ruwa ke yar iskace wai yaya akayi kikai wanan tunanen haka , ?
Nace ganin iyaka najeyi na fada a ciki akaga nawa ni mai zance akan kayan nan gida yanzu ya juyo a fusace yana fadin ba zaku shiga mota ba kun tsaya kuna gulma a nan.
Da sauri muka shige motar yadda mukazi haka muka koma ya sauke mu a kofan gida bai shiga ba yaja motar shi ya wuce.
Cirko cirko mukayiba kofan gidan ance ko lahira mai kaya shike wahala yanzu a nan sai aka barni da tarin ledoji a gaba ganin sun fara shiga sai dariya suke min yasa nabi baya su da sauri da tarin ledojina a hannu.
Muka shiga part din Amma sai dariyan keta suke min na zauna ina kumbura baki .
Amma da ta fito wanka tana saka riga a jikin ta ta kalle mu tace lafiya kuke wanan dariya haka ?
Nuna mata ni sukayi tare da kayan dana tara a gabana tace wanan kayan na may ye kuma ?
Aisha tace bari ke dai Amma ta fada maki da bakin ta yau tarko ne yakama mai shi a wurin nan.
A ruwa bata labari da bakin ki taji na kalle ta da harara bace A wuta dai wallahi Aisha ku daina kirana da A ruwa din nan na juya gurin Amma nace.
Amma ai duk keda manjo ne kuke kirana da wanan sunan har suka samu.
Baki son sunan ne yar nan ai wanda aka haifa ana ruwa akecewa A ruwa ko damana shi kuma namji ace mai Ana ruwa.
Ni har suna nawa za a saka min a barni da fatima na zai fi mun dadi wallahi amma wai wani a ruwa can babu dadin ji haka ?
Na karasa ina bata rai ledan na taka da kafana na tuna dashi a gurin itama Amma ledan ta kalla tana fadin wanan kayan fa na maynene a ciki ?
Sai suka kama dariya babu kakautawa har hakan yasa mama hadiye data dawo daga gurin aiki ta fito daga dakin ta tana fadin gaku kamar mahaukata mana ?
Nace a marairaice mama wani sukewa dariya don kawai wanan mijin kafirar da mukaje gidan ta ya kaimu shago yace kowa ya dauki abinda yake so nikan na kwaso wa yan na rigunan na daukowa Amma da manjo da mamu da Addah zannuwa shine suke min dariya.
Murja tace mama ba hakana bane taso yace ta mayar tai mai halinta sai gashi ya biya kudin babu tambaya.
Maimakon inga mama tayi fadi wani magana sai itama ta kwashe da dariya a gurin na kalli kayan cikin marairaice murya nace mama yaya zanyi da wanan kayan haka yanzu shiyasa ma nayo nan gurin Amma in samu mafita da kayan.
Mama ta dan tsagaita dariya tace aisai ki saka abinki wanda kika daukowa su hajiya kuma ki basu abinsu.
Da sauri Aisha tace wallahi sai dai mu raba Amma tace ta hanaku daukowa ne shifa ya bada bakin duk abinda mutum ke so ya dauka ku ina abinda kuka dauko a shagon ?
Sai lokacin suka dan shiga natsuwa suna fadin wallahi Amma a ruwan nan shegen wayau ne da ita mu san bamuyi tunanen haka.
Da mun sani ai muma jidan kayan zamuyi kamar haka mu biscuit kawai da sweet muka dauko daya daya .
Allah ko ya shirye ku da bakin kwadai yau kunga illar kwadai gare ku, sakarkarun banza kawai .
Jin haka murja ta kara fadin to mu munsan da hakane in bada mukaga ya biya wanda ta dauka ba mama hadiye tace ai kune abin dariya ba ita ba.
Yar albarka shiyasa nake sonki kamar yadda kike sona watau ko a ina kike ina ranki ke nan yar nan da har kika kasa mantawa dani.
Nan tayi ta samin albarka tana yabawa sai hankalina ya dan kwanta don nasan ko ba komai zata tare min fadan da nake tsoro na mamu.
Cewan da Amma tayi cikin maganan ta ashe Sani nada gaskiya wanan hadin da alama zatai kyau kyakayawan jumma,a tun daga alhamis ake ganewa.
Na shagwabe fuska ina fadin Amma yanzu ke zakiwa mamu magana ko tace maganan may zanyi abin yiwa kai idan yayi maki dawainiya ai kansa yaiwa ba wani ba.
Jin shiru da mamu tayi ashe ban sani ba fauziya har ta fice zuwa part din mu mamu suna tambaya akace da ita ina nan shine ta biyu ni don bata gane zancen da fauziya ke mata ba na gulman an saya muna kaya masu yawa wai nace ban so.
Hankali tashe mamu tayi sallama a falon tana fadin yanzu fauziya take fada min wai kun dawo kina nan kinawa gwaggo rikici.
Ke ba wani rikici da tayi tsaraban fitan su ne wai take tayar da hankali a kai kada kice tayi rashin hankali.
Kallon kayan da mama hadiye ke budewa a gaban ta tayi da ido tana fadin kayan may ye hakan ?
Nayi tsuru tsuru da ido sai mama tace Umar ne da zasu dawo gida ya biya dasu shago yace kowa ya zabi abinda yake so su wa yan nan sakarkarun wai sai biscuit suka dauko.
Ita ko diyana sarkin wayau kinga sai ta zabo wanan kayan haka shine fa take nan wai tsoro fadan ki takeyi.
Inda nake ta kalla take fuskan ta ya sauya tana fadin sayadi wanan rashin hankalin fa haka ?
Kin fi yan uwan ki ne da suka tsaya iya matsayin su sai kece zarara kika kwaso wanan kaya haka kamar hauka.
Muryan mama hadiye ke fadin ke tayani ganin abin mamaki wai fa super ne atamfar nan ?
Sai mamu tace wanan hauka daga ina hakan nan Aisha tace wallahi mama A ruwa bata san zai saya ba kai tsaye kin santa do tsokana don yace kowa ya dauki abinda yake so shine ta dauko su haka .
Idan yayi magana ta rama haushin fadan da yai muna a mota tayi wani rashin hankalin ne kuma ko ?
Bayan wanan shima umar zai biyewa karamar yarinya haka ai wanan abin magana ne gidan nan idan hjy ta sani sai ta gaskanta abinda take fada a kan mu.
Ikon Allah yanzu don umar yaiwa wanan yarinyar hidima haka shine abin tsayawa bata baki don zamani ya canza ko aimu da garemu wanan abin alfahari ne gare mu.
Don an baka toshi gwaggo wanan fa ba toshi bane rashin hankaline irin nata kawai sai amma tace yanzun dai na fahince ki sosai watau dai kin raba daya biyu a tsakanin yaran nan dai.
Jikin mamu ne yayi sanyi tace ba haka bane gwaggo wallahi abin ne naga kamar yayi yawa duk irin nasihan da naiwa yarinyar nan sai da ta zubar da kimanta a idon su.
Abu haka kamar wata zararariya har ina yar nan tasan ta zabo kaya haka masu kyau da tsadada sauri nace bafa ni na zabo ba yan wurin nace su tayani zaba.
Tace ina kinji rashin hankalin gwaggo tana kallon Amma data kawar da kanta daga kallon mamu din tana jawo ledan goron ta.
Ta juyo tana fadin ki fita daga idona maimuna tunda ke baki san abin arziki ba dai kayane kuma nace yar nan sai ta saka su a gidan nan kowa ya gani.
Mai mutuwa yaje ya mutu da bakin ciki ganin ran Amma ya baci sai mamu tace ban hanata sakawa ba ai amma ta bar wanan halin don watarana.
Kuma ta raba da yan uwan ta suma su samu da sauri Amma tace la,la,la haramiya wallahi ba wanda zata ba su a yanzu gaba daya ita zatai amfani da abinta tunda tana so waya hanasu su zaba cuncan ai dama ya basu Allah ya cisheta daga gare shi.
Dole mamu taja bakin ta tayi shiru tunda ta fahinci Amma ta daure min gindin abin dole ta kyale badon taso ba.
Mamu ta juya zata bar shiyan tana fadin ki kwaso kulolin abinci idan zaki dawo Amma tace yaki nan maimuna.
Sai mamu ta dawo dan shiru Amma tayi tana kallon ta kamar yadda kowa na fali yai shiru yana sauraren ta tace kada inji kada in gani kin yiwa yarinyar nan magana a bayana don zan saba maki sosai.
Ki godewa Allah kin samu yarinya mai tunane da har samun ta bai wuce muba tun yanzu don turamay nan da kike gani ra dauko da gaiya da sunana dana kakarta da yar uban ta saike ta dauko su tun can.
Wanan abun datayi ashe ba zai zama abin alfahari gare ki ba su wa yan nan sakarkarun ai kinga kayab shirmay da suka kwaso a can .
Sai magana na biyu wanan magana a barshi a nan inda akayi shi a tsakanin mu duk wanda ya fitar da zancen nan waje ban yafe mai ba bandai ki shi mijin naki ba zaki iya fada mai don ko baki fada ba ninan zan fada mai komai.
Don haka shine maganata dana kiraki sai mamu ta sauke ajiyan zuciya jin an hanata ta yi min fada da tasha alwashin yau sai naji a jikina sosai a gurin ta .
Mamu tace gwaggo ni ba nice uwarta ba ga anty hadiye nan ita ya kamata ta dauki na uwar bani ba.
Aiko da sauri Amma tace haram ai na fada maki ko kyale ba za a tabawa yarinyar nan ba yadda ta tsaro abinta haka za a yi.
Su gobe du kara idan haka uwar su tayi masu tarbiya da abin kwadai maza kwashe kayan nan ki tafi dasu kibi uwarki idan kuma kika bata shi ban sani ba ban yafe maku ba.
Kai hajiya ai abin bai kaican ba may ye na abin Allah ya isa a cikin maganan mama hadiye ta fada adan hasale tana barin falon.
Ni dai na kwashi kayan nabi mamu dasu a baya tare da dauko kulolin abincin Amma din na mara mata baya da kaya nikiniki a hannu na.
Sai dai muna fita mukai arba da hjy maryam da yaran ta a barandan part din ta zaune wai suna shan iska duk da wutan nepar da akedashi.
Dagani har mamu babu wanda ya kalli inda suke yayin da gaba dayan su suka tsuro muna idanuwan su a kan mu.
Ikilima ce tace A ruwa ina kuka je yau baki shiga islamiya ba nace inda kika aike ni sai uwar daga inda take tace magani ki ke nan da tambaya ina ruwan ki da ita aikin samu amsan bakar magana yanzu.
Mu dai muka shige muka kyale su a nan ina ta dari dari da mamu kada tayi min fada don naga ranta ya baci..
Sai dai muna shiga ganin manjo zaune a falon yasani matawa da fadan mamu na zube kayan ledan a gaban ta na kai kayan dana kwaso na abinci kitchen na dawo ina cire hijjab dina.
Yar nan ina kika shige haka duk yinin yau baku yini damu ba kafin in bada amsa Addah tace an fada maki sunje gaida matar yayan su na nan gidan ne ita da yan uwanta tace to to ai na manta wallahi.
Muna nan zaune da manjo muna hira da yake ina fashin sallah yasa na ban rama sallolina ba da akayi muna waje.
Kiran sallah ne ya tayar damu a gurin sai da muka fito bayan kawu ya shigo ya gaidasu manjo ya fitane na dauko ledan ina fito da turamay zannuwan daga cikin leda.
Wanda duk na dauko da sunan kowa na mika mai don na barwa Amma nata tunda zan dauko kayan a part din ta.
Turmin suke bi da kallon mamaki har na gama mika masu wanan fa na maynene Addah take tambaya ?
Nace wanda mukaje gidan sa ne ya saya muna su ni dama da sunan ku na zabo do yace kowa ya zabi abinda yake so.
Nan dai na sake na basu labarin komai da ya faru lokacin fitan namu manjo ta kalle ni tace A ruwa duk wanan kayan haka mai yawa ya saya maki a lokaci guda haka ?
Ko dai da wata a kasa ne yana toshi ba sani ba nace kai kaji manjo kuma sufa masu kudine ana fadin kudin kayan ya mika kati aka zare kudin.
Manjo yau naga gida wallahi wai fa duk nasa ne bana kawu ba wanan ma ai ina yafi kawuna kudi nake gani.
Ikon Allah kuma kawun ki ne ya haife shi nace shine babba dan sa ina gani ni dai ban sani ba son yawa ke gare su kuma fa uwar su daya dukan su.
Shigowan mamu yasa naja baki na ba tsuke don kada tace min na cika zuba kallon kaya tayi tana zama sai Addah tace gamunan muna sauraron ikon Allah wai fatima ce tayi muna tsarabab kaya haka.
Anty Addah wanan yarinyar ni ban san irin ta ba yau ai gwaggoce ta kwace ta a hannuna don tace kada in fara in mata fada zata saba mun in banda hauka irin na yar nan daga ance ku zabi abinda kowa ke so sai kiyi diban hauka haka.
Kurciyace wataran zataji kunyar yin hakan shine wanda kuka gani jiya da kuka iso suna magana da uwarsu a waje babban dan maugidan nan ne a kasan waje yake zaune da italin shi ta fada a takaice.
Amma tana fada muna yanzu wai gidansa abin tsoro ne kamar gidan dan yankan kai.
Da sauri mamu ta kallo inda nake zaune tana hararana tace wanan yar da sheri take wallahi umar din ne dan yankar kai ?
Bakinki kanin kafan ki duk na sake jin wanan magana zan saba maki sosai wallahi nan dau ta shiga fada masu irin aikin da yakeyi a can nima na bade kunne na ina sauraren sirin da ban sani ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button