NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:23 – ????????????: Shiru dakin yayi ana sauraron abinda hjy sabuwa da ta fado dakin babu ko sallama take fadin magana iya son ranta.
Babu wanda yai mata magana daga cikin wa yanda ta sama a dakin ita da kanta taji nauyi da kunyan kanta lokaci guda sai kuma ta fara dan kame kamen zancen.
Ina gida yanzu wanan yar ta kirani take sheda min wai umar ya ci mata mutunci tunda safen nan akan matar shi.
Shine ya mike tsam daga inda yake zaune ya nufi hanyar fita daga dakin ba tare da yama tsaya sun gaisa da ita ba.
Fita zakayi ne mama Asabe take tambayan shi bai juyo ba yake bata amsa da fadin ina da abin yi ne yanzu.
Amma kasan wurin ka nazo aiko don kaji abinda ya kawo ni gidan nan yanzu ai.
Juyowa yayi da mamaki a fuskanshi yake fadin wai dani kike magana hjy ?
Itama kallon mamaki take mai don babu alaman wasa ko girmamawa a gareta ko kadan a fuskan shi.
Eh matar kace takai karan ka gareni nazo jin dalilin faruwan hakan don zancen mata ba a san namiji da daukan bangare daya ba.
Har kana fadin wani zance dani kaina na kasa fahintar may hakan ke nufi a zuciyana.
Matata fa kika ce hjy ki dai ce yarki dake zama a gidan nan ko zaifi sauki matata kan ai ga daya nan a gaban ki yanzu kina ganin ta.
Ke zahra ko kece kika kai kara a wurin tane don ban fahinci zancen nata ba har yanzu gaskiya.
Eh lalai kana da gaskiyan ka don ba laifin ka bane idan kayi hakan a yanzu saboda alama ya nuna baka cikin hayacin ka gaskiya.
Zaki iya fadin hakan tunda yarki na son ta lalata min gida da fitina don kawai taga tana cin albarkacin wani a wurina.
Saidai ina son ki fada mata cewa zaman ta a gidan nan yana gab da karewa idan bata fita harkan iyalina ba.
Don ba zan lamunci a wullakanta min matana da yayana ba ko kadan a zauna lafiya ko yanzu taci albarkacin mahaifiyata ce da take zama gidan nan donta.
Koda yake ku din baku sanda hakan ba tunda ko ita sin bataci ragowa a wurin ku ba sai kokarin nakasa muna ita da kukeyi ba dan Allah ya gyara zancen ba.
Jummai kina jin abinda danki ke fada mi a gaban ki baki yi yunkurin hana shi fada min wanan maganganun da yake fada min ba.
Ashe taimako yana iya komawa tsiya kefa da kanki kika bukaci hada wanan alakan don a ceto maki danki daga hannun wanan matar tasa da kika tsana.
Sai haihuwan da take zubawa a gidan don ta mallake dukiyan shi ita da uwarta da wasu can daban da baki son hakan ya faru dashi.
Ashe kin san bakifi karfin daki bama tukun balle matar tashi da alama ya nuna duk ta gama dake da diyan nakima.
Ai ashe don ni kika dauko yarki kika kawo ta gidan nan ban sani ba don ni bansan ma da wata aba bacan dana nazo wai matar mijina don banga alaman hakan ba a gidan.
Ke fitsarara kada ki soma kawo min rashin kunyar ki da ake fadan kina dashi nan don gida kika sama na rashin mutunci.
Sabuwa dama kece daidai dani ba yarki ba don haka yanzu ki kauda yarki kizo ki share daki mu zauna dake sai mu kara ina ganin haka zai fi don kece daidai dani wurin daukan fansa ba lusarar yar nan da kika aje muna a gida ba kamar ba mace ba don ko gaba na mata bata dashi.
Kutumar uban nan har iskancin naki yakai ki kalli tsaba idona ki fada min haka kwarai kuwa tunda ke baki ji kunyar fada mi magana irin haka a gabana ba.
Aiko ta kara tasowa tana kokarin kaiwa gareni da sauri yaya yace hjy muddin hannun ki ya kai a jikin matana wallahi sai na daure ki a garin nan karyan masifa kikeyi ana kyaleki ne dama.
Muryan hjyn su yayane data fashe da wani irin kuka lokaci guda a dakin ya mayar da hankalun kowa a wurinta .
A daidai lokacin samira ta fado dakin tana fadin wallahi babu mai wullakanta min uwa ya zauna lafiya a cikin ku.
Don uwa bata fi uwa ba ehhe ki daina kukan munafunci ki tsaya a gyara zance zaki sakawa mutane kukan munafunci don zancen ya tsaya a, , , ,
Saukan mari da tajine a fuskanta har biyu lokaci guda ya hana ta karasa maganan da take son fada.
Yaya ne da take tsamanin ya bar dakin yaga shigan ta ya dawo a daidai lokacin da take wanan magana ga mahaifiyar su.
Hanyar fita ya nuna mata ita da uwar yace ku fice min daga gida yanzu nan ba sai an jima ba har hjy sabuwa zatai magana ya kara daka mata tsawa saida ta firgice don tsoro.
Mai hakkuri ance ranshi bai iya baci ba don yau kan ko mahaifiyar shi ta sheda hakan don bai ragawa hjy sabuwa ba ko kadan ranan tsaye yayi yana umartan yan aikin shi da su tabbatar basu kara shigo mai gida ba.
Sai kuma ga hjy sabuwa ta zube a kasa tana rokon shi ya rufa mata asiri ya dubi zumuncin su ya bar samira a dakin ta.
Zumunci zumunci fa kika ce hjy ko kin manta ke da bakin ki kika fada babu wani zumunci a tsakanin ku sai na zaman unguwa daya dasu mama.
Yanzu hat zaki kira min wani kalman zumunta a tsakanin mu dama talala na sake maku don inga iya gudun ku saboda albarkacin mahaifiyata da kukaci na bar yarki a gidana tana zama.
Yanzu ko kun kaini bango ta yadda ban kaunar kara ganin kowan ku a gidan nan .
Dama ance yar mace bata taba zama mace ta gari do gashi kin nuna min baki san darajan iyayyen wasu ba balle naki .
Kun duke ta kuna ganin kamar kun daki banza ba wani matakin da za, a iya dauka a kanku do kawai an maku dubaiyan da baku san ana maku ba sai gashi kuma har zaku maimaita hakan a gaba gun matana a yanzu.
Kin dauka idan idon mama ya rufe da abinda kuke dura mata nawa dana yan uwana zai rufene hjy.
Da har zaki dauko yar ki mai ciwo ki kawo min har gidana wai da sunan aure watau duk mu taru mu halaka bayan ta gama halakanta da taimakon ki.
Baki hjy ta bude tare da fadin sheri kuma zakai muna umar don kaga muna rokonka ko may ?
Habbib dake tsaye tare da iyalinshi dana Aliyu yace eh ai dole ki roke shi kan cuta azzaluman mata mun dade da sanin komai kyale ki mukayi muga iya gudun ki gidan nan ai.
Ko kin dauka idanuwan mu muma a rufe yake kamar yadda kuka rufewa mama gaskiyan abinda ke damun yarki taki aurowa a lagos din.
Shine do cuta zaki kwaso sheri ki haro dan uwan mu dashi har gida wai da sunan kin taimaki mahaifiyat mu da yarki.
Hjy dake wani kukan takaici da bakin ciki a zaune ta wani dafe kirji da karfi tana fadin na shiga uku dama yar nan bata da lafiya ashe sabuwa kika rufe min.
Abin nasu kamar hadin baki don sai jin muryan yan uwan haihuwan hjyn su yaya mukayi suna fadin dama ai saida muka fada maki bakiji ba hjy a lokacin .
Yanzu ba don Allah ya gyara ba da kin cuci zurian ki da kanki anty wanan maganan nake fada maki a kullun kuke gabin zafina a cikin mu.
Akan wani ra,ayi naki can na banza zaki cutar da rayuwan yaran nan ki halaka mashi zuria irin wanan ranan ake gudu dama ranan nadama ga bawa.
Godiya mu ga Allah a kullun da yake kawo muna dauki akan komai kafin wani abin ki yakai ga samun mu.
Yanzu gashi kin biyewa hjy sabuwa har auren ki na shekara da shekaru yakai ga samun tangarda wanan son zuciya dame yai kama haka don Allah ?
Gida duk ya kidime da yayan mutane shikan yaya yana gama magana da hjy sabuwa tun lokacin ya juya ya shiga part din shi ya rufo.
Haka nima naja kafa zuwa part din mu yarana na samu zaune a falon maria ta hadesu a guri daya suna kallo.
Zama nayi a cikin su a daidai lokacin da su Aisha da Rukkaiya suka karaso ina masu sannu da zuwa.
A cikin alaman mamaki suka karba min tare da fadin wanan abin mamakin dame yai kama hakane wai ?
Rukkaiya tace mu dai gamu muda ba,a so din dai mune na kwarai a yanzu ai don da bakin suke magana akan irin taimakon da kike mata a yanzu .
Koma dai meye ai naka sai naka ba don Allah ya gyara yaya yana da natsuwa ba da yanzu ya dade da kwasan wanan cutar ko tunda auren nasu ai yakai wata biyu ko uku yanzu tana gidan nan zaune.
Wana ma wani iri rashin zuciyane ace mutum ya nace kan abu idan ba yasan cutar da yake son yi ba a gurin.
Ni wanan zancen ma gaba daya duk ya kashe min jiki wallahi wai mutane mai yasa basu da imani ne yanzu Aisha ke fadi.
Sai yanzu nai magana tun zaman su wurin ina fadin rayuwa haka take zuwa da kalubali mai tarin yawa ga bawa sai idan Allah kareshi a cikin ikon shi sai ya kawo mashi komai da sauki .
Abinda hjy take nuna min da farko ne nake jin zafin hakan amma yanzu na daina rikon abin a raina ko kadan don dai jini ya riga da ya gauraye da ruwa.
Don ko yanzu na bar gidan nan sunana ba zai taba kankaruwa a cikin zurian dakin hjy ba dole sai ance nice uwar yaran nan jikokin ta.
Kwarai kuwa Rukaiya tace dole ne kan a fadi hakan dan ma hjy ta godewa Allah rabon yaran nan bai kasheta ba yara kusan nawa ta nuna bata kaunar auren iyayyen su da diyanta.
Allah ya riga daya tsago sai zurian dakin ta sun fito daga jikin mu ai dan ni kiri kiri hjy ta kira sunan uwana ta hada dana ubana ta zagesu tas a gabana wallahi.
Wanan idan ba kakai zuciya nesa ba kina ganin mai zai faru a wurin saukin abin ma yaran nata basu dauki wanan halin nata ba a ran su da ai zumunci ta dade da lalacewa ko a family mu.
Gulman me kuke yi haka kuka kashe murya haka don da gani zaman gulma kuke a nan muryan yaya habbib ne yake fada muna haka .
Juyowa mukayi muna kallon shi da dan murmushi a fuskan ko wacen mu sai matar shi ke fadin kai yaya mu hiran abinda ya faru mukeyi ba gulma ba.
Kun gaisa da hjy ne da kuka zo nan kuka zauna ya fada yana tsare mu da idanuwa ma,ana umurni yake basu a lokacin.
Dakin ne baida dadin shiga yanzu yaya ana cikin wanan tashin hankalin haka yasa bamu shiga ba sai dan zuwa anjima idan an rage yawa.
Yadda ya juya yasa ta fadin Aisha tashi mu dubata kada muma namu ya same mu yanzu a gurin shi.
Ni dai ina jin su suna mikewa na mike nabi bayan su zuwa dakin da hjyn ke ciki duk da muna jin hayaniyar yan uwanta a dakin.
Mun samu har su salma sun shigo don labarin abinda ya faru da safen ya isa kunnen yan uwa sai zuwa gidan suke don jin ba,asin zancen.
Sallaman mu ya dawo da hankalin su kofan dakin muka shigo mu uku muna gaida su mama Asabe take fadin au a tare kuke da maigidan ashe ?
Tare muke mama Rukaiya ta fada tana neman wurin da zata tsuguna a dakin don ba wani fili a dakin don tarkacen hjy dake dakin yanzu.
Sun gaida hjy tana amsa masi cikin yanayin rashin dadin zuciyan da take a lokacin take tambaya da ina yaran suka barsu ne ?
Aisha tace suna gida wurin mama muka barsu da zamu zo mun biya can suka ce zasu tsaya a nan da cewa gidan kawu ke nan.
A dan dakile ta amsa don jin abinda Aisha ta fada din da alaman hakan bai mata dadi ba kasan ranta.
Fatima sannu da kokari fa muna ta jin kokarin da kikeyi da jikin hjy wurin asabe Allah ya saka da alheri ya baku masu rama maku hakan.
Dakin ne ya amsa da amin ina fadin hjy dazun ko kin sha wanan maganin dana hada sai mama asabene tace .
Ina fa yan nan ta dauko ke nan zata sha wanan bala,in yazo muna tunda safen nan ai sabuwa batayi ba wallahi.
Don Allah Asabe ku daina ganin laifin su nifa har gobe inda gaskiya yake nake fada sam sabuwa wuri ta samu a nan .
Allah dai ya kare komai bai kai ga faruwa ba a tsakanin su amma mama komai gaskiya ai hjy sabuwa tafi mama laifin don ta boye mata gaskiyan halin da yarta ke ciki don cuta da zalunci kawai salma ke fada.
Magani na hada na kara bawa mama Asabe don taba hjy din a wanan lokacin na fita zuwa dakin yaya don na samu yaya habbib shi kadai a zaune falon shi bai fito ba.
Dakin na tura na shiga da sallama na hango shi kwance yana rigingine fuskan shi yana kallon saman dakin.
Dan juyowa yayi ya kalli kofan kafin ya kawar da kai ya koma a yadda yake da farko na karaso ina fadin yaya ka kwanta kabar yaya habbib a falon shi kadai zaune.
Yana gidan nan ne har yanzu ya tambaya har lokacin kamar bason mu hada idanuwa dashi ne.
Zama nayi a gefen shi ina fadin lafiya na gabka haka yaya ina tambaya tare da kallon shi a yadda yake din kwance.
Yace da kyat No ba komai sai yai shiru nima dai shirun nayi na dan lokacin kafin yace Zahra na amsa da na,am ina kallin shi.
Kada ki dauki wanan abin daya faru da zafi kice zaki rike shi a ranki don Allah .
Da sauri nace haba yaya a kan me zan dauki wanan zancen da zafi bayan Allah ya karemu daga sherin hjy da yarta.
Hannu ya daga min yana mikewa daga kwancen yake fadin nasan kalaman hjy sabuwa da mama ta fada a kanki suna da zafi sosai.
Don haka nake rokon ki kan kiyi hakkuri da duk abinda hjy tayi maki kada kice zaki dauki wanan abinda zafi a ranki.
Yanzu bada bane yaya hjy nasan uwatake a gareni kuma sarakuwata don haka don mahaifiya taiwa yarta abu saita dauki zafi da ita.
Ajiyan zuciya naji ya sauke mai dan sauti yana fadin idan kin min hakan kin kyauta min matuka kuma ina alfahari dake akoda yaushe don nasan daddy bai min zaben tumun dare ba.
Ko nace ina dan kallon shi ina murshi yace kinfi kowa sanin wanan hadin namu ai daga Allah yake kawun ki idda sunna yayi kawai .
Au goron da zaka ba kawu a yanzu ke nan yace gaskiya na fada yana kokari tashi tsaye ta hanyar dafani ya mike tsaye.
A tare muka fito dakin har lokacin yaya habbib yana gurin zaune wanan katon tare da yaran yake fira jin fitowan mu yasa ya dago kai yana kallon mu.
17/11/2021, 07:26 – ????????????: Sun dade tare a falon bansan may suke zance a kai ba don ina daki tare dasu Aisha muna hira inda suke ban hiran abubuwan da hjy take yi masu na rashin dacewa gare su.
Ban furta komai ba sai kara kwantar masu da hankali a kanta kamar yadda nima mamu take yawan yi min nasiha da kada na nuna abun yana damuna don dan ta bazai ji dadin hakan ba idan na nuna.
Rukkaiya kan cewa take ita kan gaskiya ba zata iya shanye wani abu a ranta ba don da gangan ake maka cin fuska don kawai danta yana auren ka sai ka zama abin ki ga mutum ?
Sai bayan la,asar yaya habbib ya bugo waya yana fadawa matar shi ga driver nan a waje yana jiran su don yaran sun fara damuwa lokacin.
Sai da suka shirya sun dadauki abinda suke so a dakin nawa ban hanasu don sun nuna ra,ayi akan abina nasan Allah zai musaya min da wanda ya fishi idan na basu da zuciya daya.
Muka fito zuwa dakin hjy don su sallameta a zaune take lokacin tana shan ferfesun kaysn cikin rago.
Nafisa tana tsaye a kanta da ruwa rike a hannun ta tana bata jin sallaman mu shigowa yasa suka mayar da hankalin su gare mu.
Mun mata yaya jiki yayinda take dan dago kai tans fadin ashe kuna gidan nan har yanzu eh yanzu zamu koma don yaran nacan su damu mu dawo.
Ke nan ba za,a kawo su su ganin basu ko don kuna gudana da yayan ko hjy ta fada tana kai cibin da take shan ruwan miyan a bakin ta.
Can muka fara zuwa gaida daddy shine suka lekawa mama don sun saba da ita yasa muka barsu can tare da ita don lokacin an bugo waya ana wanan fitinan da safe.
Na fahinci may Rukkaiya take nufi yasa nayi saurin fadin hjy Nafisa ashe kin shigo ban sani ba ?
Tace ummm ke dai fatima na shigo dazun bayan azahar da nake jin abinda wayan nan marasa mutuncin sukayi yau .
Don ni ina kuryan Amma ina barci banji me ke faruwa ba sai dana tashi Amma ke labarta min hakan.
Wallahi naso na shigo a lokacin da yau sun kara raina kansu wallahi don wana karon ba zan kyalesu ba Allah.
Umm tashi mu tafi Rukkaiya tace tana hararan gefen da Nafisa din take .
Jin hakan nace Nafisa ke nan wa yan nan ai sai irin su yan duniya don babu mutunci a tare dasu ko kadan.
Na fahinci babu shiri a tsakanun su da samira do haka nake kokarin a rabu lafiya a dakin don yanzu sam bansan me yasa bana son tashin hankali ba ni.
Ganin sun fara fita daga dakin yasa nace barin dawo Nafisa in baki labari ta amsa da ai ina nan don kilama a gidan nan zan kwana yau.
Nace kice dai yau mune da bakuwa a gidan nan ashe mara masu Aisha baya nayi ina fadin sai yaushe kuma zan ganku ?
Muna nan ai tunda an kawo mu jiya ne don haka sai kin gaji da ganin mu har bakin mota na raka su suka tafi ni kuma na koma ciki.
Dakin nayi niyar shiga zancen dana sama sunayi ya hanani shiga dakin Nafisa ce ke fadin ai nasha fada maki wallahi fatima tafi su kirki dan dama Aisha don ita bata fitowa fili ta tsulawa mutum tsiya kai tsaye.
Uhumm ni kaina canzawan yarinyar nan yana ban mamaki don da farko na dauka makircin sune take min don mijin nata ya gani.
Amma yanzu na fara sarewa da al,amarinta don yadda akai wanan maganan sabuwa ta tona min asirin duk abinda mukayi tare da ita amma bata canza min fuska ba saima goyon bayana da tayi a gurin.
Jin hakan yasa na fasa shiga dakin naja kafana nabar kofan dakin zuwa part din mu zuciyana cike da tunanen maganan nasu.
Lalai mamu tayi gaskiya da take fadin duk abinda zataiwa hjy bazata taba son mu a ranta ba don kiyayyan mu ya riga da ya shiga ranta ko mai kankare shi sai Allah.
Tunanen ba zai kare ba na tashi zuwa gun maria don ganin halin da suke ciki don yinin ranan na barta da yaran tana dawainiya dasu.
Na sameta tana goye da babana da yai barci a bayanta sai sultana da take shiryawa don fauziya tana bayi tanawa yaran wanka lokacin saboda yamma dayayi.
Har zuwa lokacin da yaya ya dawo gida baya cikin walwala tare dashi na fahunci hakan ne ta hanyan rashin cin abincin dare da baiyi ba sai ruwan shayin daya sha ya kwanta a lokacin.
Ban matsa da tambayan shi haka nazo na kwanta na tashi don da safe ma muryan shine a inda yake karatun kur,ani ya tayar dani .
Kallon shi nake da mamaki da bai tayar dani inyi sallah ba a ranan haka kuma banji lokacin da akai sallah asuba ba a ranan .
Ki tashi kiyi sallah lokaci yana kurewa sanyin ruwan sama ya hanaki tashi kiyi sallah akan lokaci.
Ban iya magana ba lokacin don raina da nake jin babu dadi saboda rasa sallah asuba danayi a ranan.
Ban tsaya dakin ba fita nayi zuwa dakina na shiga bandaki kodana idar da sallah ban daga ba wurin ina zaune sai faman tunanen rayuwa nake a raina.
Merry ce ta fado min a rai tausayin ta ya kamani don raba da da mahaifi sai Allah nasan kuma wucen merry ta bar queen a kasan nan bawai ta bar zancen bane.
Saidai matakin da zata dauka ne ban san yadda zasu kaya karshe ita da mijin nata ba a karshe.
Mikewa nayi don jin ruwa ya kara saukowa a lokacin hakan yasani fita daga dakin zuwa wurin maria don in duba halin da suke ciki.
A daki na same su bata yarda tabar yaran sun fito koda falo ba don ruwan da ake shekawa a safiyan .
Tana ganina ta fara gaidani kamar yadda nake kiranta da maman kid’s haka na ambata mata ina zama nake tambayan ta ya suka kwana tace lafiya sai dai Abbanane jikin shi da dare ya danyi zafi kadan.
Tabashi magani da safen nan taji zazzabin ya sauka nace a jikin shi nace ai da bakuyi mai wanka ba yanzu.
Ina daki har ta shirya yaran suka fito cin abincin sai lokacin na tuna ban leka hjy ba ranan .
Koda naje na same shi dakin suna hira nayi sallama na shigo Nafisa tana kwance saman dogon kujera har lokacin tana barci bata tashi ba.
Mama Asabe ne ke fadi ai nace hjy yau bamu ganki ba tun dazun dan murmushi na sake a fuskana ina fadin Abbana ne baida lafiya yau na dan tsaya dubashi.
May ya samu yaron kuma ta sake tambayana, hjy kuma tana fadin waye ake kira haka cikin yaran ?
Bani kadai ba har yaya saida ya dan kalli mahaifiyar tashi don jin tambayan da tayi a lokacin.
Kafin wani cikin mu ya bada amsa sai mama Asabe tace karamin wanda ake goyo shine da wanan sunan.
Ikon Allah sunan shi wa ke nan ake kiran sa da Abba shiru nayi ina mamakin ta a raine sai shine ya bata amsa da Abubakar yake ai.
Sunan mahaifinta ke nan ka sakawa yaron ashe ai na fada maki tun lokacin da aka haifeshi Abubakar na saka mai.
Amma ai baka fada min sunan mahaifinta bane ka saka mai ko zaiyi magana mama Asabe ta amsa da fadin ko ba sunan shi bane tunda haka sunan yake sai ta kirashi da Abbanta don sunan mahaifintane haka ?
Umhumm kawai hjy tace tana kawar da kai gefe daya ganin haka yasa na mike don barin dakin sai mama Asabe ke fadin.
Allah dai ya bashi lafiya da dukkan musulmi baki daya muka amsa da amin ina barin dakin.
Wanka na shiga na fito na tsaya shiryawa hakan ne ya dan daukeni lokaci har yakai ga shigowa dakin ban gama shiriba.
Fuskana babu walwala ina mai jin zafin maganan hjy datayi kan yarona ko adduan samun lafiya bai samu ba a gurin ta.
Yana shigowa ya kalleni ganin yanayi na yake fadin ni zan fita akwai inda zamu tafi da Nasir yau.
Kayi break ne na tambaya daga inda nake zaune a gaban mirrow na yace yanzu dai zan fita nayi ina son zanje gida yau in gaida kawu na fada.
Ki bari sai idan na samu lokaci mu shiga tare don ina son zuwa mu zauna dashi nima amma kasan mamu bataji dadi ba tun shekaran jiya ban lekasu ba .
Kina magana kamar wace ke cikin bacin rai mana ta fada a daidai lokacin daya kai kofan dakin .
A kan me raina zai baci zancen mama kikewa wanab daure fuskan kaima a kanshi zaka hanani zuwa gida na tambaya.
Kafin ya bada amsa nace akan me zan daure fuska tunda bani tayiwa maganan haka ba kuma ai da zaka saka sunan bakai shawara dani ba da sai ince a saka na kawuna.
To ni na saka na surikina amma ai ba aso ka saka din ba ya dan kalleni ya girgiza kai yana fadin Allah dai ya raya min yarana yasaka masu albarka.
Ya juya ya fita bin bayan shi nayi da kallo tare da jin wani takaici a raina naso yau in je gida in duba su mu dan kebe da mamu kan abubuwan da suka faru.
Ban fito ba don na karbi dana muka kwance tare a dakin haka yasa ban fito ba sai wajajen sha biyun rana ko shi sultana ce ta shigo da kuka dakin na falka.
Muka fito tare zuwa falon lokacin ne maria ke fada min kamar taga merry ta shigo gidan nan don taga wasu mata sun fito part din ta dazun.
A raina nace nasan za a rina shigowan Atika ya dauke min hankali ban kara bi ta kan zancen merry din ba koda gaske ne ita din ce.
Don Atika dana gani saboda koda mukazo kasan tun lokacin mun samu tana bauchi sunyi bukin kanen mijin ta su biyu a can.
Mun jima da Atika a dakin muna hira kafin mu fito zuwa cin abinci a falo sai lokacin na tabbatar da zuwan merry din da muke kwankwanton zuwan ta garin.
Da fara, a a fuskana na yi mata sannu da zuwa ta amsa min da kyat ganin haka yasa na share ta don ni ba lokacin ta nake dashi ba yanzu.
Ban kuma koma dakin su hjy ba don saboda cin fuskan da tayi min saboda kawai sunan mahaifina dataji yaron dashi.
Bayan mun gama cin abinci na kai Atika dakin don ta gaida ita da jiki suna zaune sunyi shiru a dakin da gani kowan su yayi zurfi a tunanen wani zance ne muka shigo dakin.
Sai mama Asabe ke fadin kai bukar ya jikin naje dubashi akace kuna barci tare dashi a dakin.
Na dan juya ina kallon ta tare da fadin yaji sauki ai mama nagode komay hjy ta gani can tace an fada ma maza na rakin ciwo ne halan mai rakin ciwo.
Dan murmushi nayi kawai ina fadin wanan kawatace tun na yarinta yanzu suna garin nan ne da mijin ta zaune.
Ohh itama yar bauchin kuce ashe Nafisa da tunda muka shigo sai a lokacin tayi magana take fadan haka.
Na dan juya inda take ina fadin kin tashi ke nan don iyakata da ita dan guntun murmushi kawai tunda na fahinci tsanata a garesu har zuciyan su yake.
Ashe merry ta dawo ne Nafisa ta fada yanzu na tashi na ganta nima na bata amsa a takaice muka daga muka bar dakin.
Karfe biyar bayan Atika ta tafi ne sai gashi ya dawo wanan karon su ukunsu suka shigo gidan inda suka yada zango a dakin da mahaifiyar su take.
Sun dan jima a dakin shi ya fara fitowa ya same ni a daki tare da fauziya muna ba Abba magani don jikin shi da ya kara zafi lokacin..
Har yanzu jikin nasa da zafi ke nan ya fada lokacin daya shigo yana karasowa inda muke .
Na dan dago kai ina fadin yanzu ya kara zafi kuma shine nake bashi magani .
Dukawa yayi ya karbi yaron a hannu na yana fadin bari ayi sallah mu kaishi asibiti a dubashi bandai yi magana ba har ya gama da yaron zai fita nake fadin ashe merry tana tafe ne ?
Merry ya juyo da mamaki yana tambaya fuskan shi dauke da mamakin jin haka.
Tazo ne ya tambaya yana kallon fuskana da mamaki sai kuma ya juya yana fadin humm ya fita.
Nikan sai ban san dalilin jin zuwanta bai kwantar min da hankalina ba don haka nake faman kafa kafa da yarana a gidan na saka ido ga duk wani motsi nasu.
Zuwan ta da kamar sati biyu a gidan kowa na zaman sa ba ruwan wani a tsakanin mu don baka sanin ma tana gidan sai idan ta fito za a ganta.
Gashi ta rame ta kara duhu sosai da gani bata cikin yanayin dadin rai yanzu.
Kai ranan dai yawan mafalkin da nakeyi marasa dadi yasa na yanke hukunci fadawa mamu cikin daren nake waya da mamu ina fada mata nifa hankalina bai kwanta da zuwan merry din nan ba, .
Don haka kawai nake jin faduwan gaba tunda na ganta garin nan ga yawan mafarki da nakeyi mara dadi.
Mamu ta tambayeni da ita kike yawan mafalkin kodawa nace hankalina daine bai kwanta ba mamu.
Nasan halin bakaken fatan America wurin daukan famsa sai nake ganin kamar shi tazo yi a kan yarana da sauri mamu tace
Don me zaki fadi haka sayadi ina ruwanki da maganan su da zata dauki fansa gun yaran ki kuma.
Mamu nidai hankalina bai kwanta ba da wanan matar tunda har naji gabana yana faduwa haka tunzun ta gaskiya a cikin daren nan zan kawo su yanzu daya shiga sallah.
Ki bari zanzo da kaina tare da Nura mu dauko su a daidai lokacin ta yadda ba wanda zai gane hakan zan ma kawun ki bayanin komai yanzu.
Inji mai zai fada kada in kwaso yaran bada sanin shi ba.
Haka kuwa ya faru don ba wanda yasan fitan su gidan har da maria suka fice gidan koda ya dawo yana tambaya cewa nayi kawu ya aiko aka kwashe su dazun bayan fitan shi.
Don me aka dauke su da yamman nan nace ban sani ba ya dai aiko yana son yaran su zo mai ne kawai yace.
To amma kuma idan daddy zai kwashi yaran zai kira ko ya fada amma haka ka, , , sai kuma yai shiru ya juya ya fice daga dakin.
Nikan ganin merry tana gari yasa nake rufe kofana da wuri na shige abina daki in kwanta.
Da kyat na samu Abbana yayi barci ranan sai fitina yake min bayan na samu yayi barci, bayan dan fitinan daya taba shiga barcin can cikin barcina nake jin hayani ana dukan kofana da karfi kafin in bude idona da kyau ina saurare kofan aka kara duka da karfi sosai na mike zaune ina kokatin kunna autan dakin don inga haske.
17/11/2021, 07:26 – ????????????: Jin bugun kofan yayi yawa yasa na fara addua, can naji murya da alama ba hausawa ke magana ba a yadda nake jin muryoyin su a lokacin.
Suna fadi a cikin turancin lagos dana kwarai meke na break d fucking door now.
Wanda aka ba umurnin karya kofan ya fara kokarin dukan kofan da karfi yana son balla kofan kota karfin tsiya.
Ina tsaye kuryan daki ina jero duk addu,an daya zo min a bakina a lokacin can naji dayan yayi wani kara yana fadin shit he don’t shoot me wooo.
Jin hakan yasa na kara matse yarona gam a bayana ina jero adduan ina ji ina gani ga kofan ya kusa budewa don ba karamin duka sukewa kofan ba lokacin.
Wani karan na kara ji mai karfi wanda ya tayar min da hankali sosai don ina jin sautin tankar na yaya umar a lokaci.
Ina saman bakina ga hawaye yana zubo min wanda bansan inda suke fitowa ba a lokacin.
Shiru naji a lokaci guda a daidai lokacin da Abbana yaji matsan da nayi mai yaiwa hadi da karan dukan kofan ya tayar dashi a lokaci guda.
Ya fara kuka babu kakautawa a lokaci daya ina kokatin rufe mai baki yanayi kamar zai shude a lokaci daya.
Kukan nasa yai min yawa yasa na sauke shi ina kokarin bashi nono ko zaiyi shiru .
Sai dai ina zuciya irin ta yara yazo mai a lokacin sai kuwa yake don ya tsorace ga baki daya.
Shawara nayi na shage ban daki dashi in lalashe shi a hankali na tura kofan ban dakin na rufo na fara lalashin yaron da kyat na samu ya kama nonon sai faman ajiyan zuciya da yake saukewa lokaci guda .
Ina cikin bathroom din cike da tsoro don ba komai nake jawa ba sai wullakancin da sukewa mata a yadda nake jin labari shi nafi kawowa a raina.
Can gabanin asuba naji ana sake dukan kofan dakin tare da kiran sunana inda na tabbatar da muryan yaya habbib ne dana su kawu.
Sai wasu muryoyi danake ji na daban suna fadin a karya kofan mana aga halin da take ciki idan basu harbe ta ba.
Tunda ga shedan harbi a kofan kuna gani sai naji an kara kiran sunana da karfi haka yasa na taso a inda nake da sauri zuwa wurin kofan na fara budewa.
Da kawu balarabe na fara arba haka ya kwantar min da hankali na nufesu ina kuka sosai naji muryan mama hadiye na fadin a kama yaron kada ya fadi kawu kuma yana fadin bakidai ji ciwo ba ko Fatima ?
Kai kawai na iya girgiza masu ina kwantawa a jikin mama hadiyen cikin tashin hankali.
Can kuma na dago da sauri ina fadin yaya fa mama ina yaya yake don ban ganshi a cikin su ba yasa nake tambayan shi.
Ya na nan naji kawu balarabe ya bada amsa yana kawar da kai da sauri tare da fadin hadiye ku zauna da ita a nan zamu koma asibitin yanzu.
Mama wake asibiti don Allah ku fada min ina yaya yake ko shine ke asibitin ne mama ina tambayan ta wasu hawaye na kara zubo min lokacin.
Kwantar da hankalin ki ki kama yaron nan dake kuka yanzu idan gari ya kara wayewa zai dawo ai.
To nace ina kaiwa zaune har lokacin ina raba ido ga mutanen dake tsaye a kaina fuskokinsu babu dadi a yanayin su suna tsaye kowa ya kura min idanu suna kallona.
Dan dukawa nayi ina kallon yatlron dake shan nono don ajiyan zuciyan danaji yayi da karfi lokaci guda saboda kukan daya sha din.
Wani sautin kuka naji an sake wanda yasa na mike tsaye zubur da yaron dake makale da nono a bakin shi yana sha kamar ba gobe.
Sai lokacin nasan da hjy maryam a wurin don jin muryanta da nayi tana fadin don Allah ku bata hakkuri karta koma daga muna hankalin Fatiman kuma.
Lokacin har nakai tsayeni na nufi hanyar dakin hjy inda nake jiyo koke koke a dakin hjy ce ke fadin na shiga uku na lalace sun kashe min jigon dakin nawa yau.
Wa aka kashe na jiyo ina tambayan mama hadiye danaji ta dafani da sauri mama tace ba a kashe kowa ba fatima rudun hjy ne kawai.
Yanzu me aka dauki ran mutum ne sai akashe mutum akashe banza don kawai imani ya kawo a zukatan jama,a.
Allah ya jikan ka umar Allah yabi maka hakkin ka ga duk wanda ke da hannu a cikin aikin nan.
Idona naji ya fara rufewa a lokaci guda daga haka ban kara sanin inda nake ba sai falkawa nayi nagani daure da ruwa karin ruwa a hannu na ana kara min.
Bude idona da sukai min nauyi nayi har wani yaji suke min saboda halin masifan da muke fuskanta a ranan.
Kallon dakin nayi na fahinci a asibiti nake kwance har lokacin ban san karin ruwa ake min ba saida na daga hannu na a lokacin naji karin ruwan da ake min din.
Zubur nayi kokarin mikewa zaune don tuna abinda ya faru damu da zancen hjy danaji har nakai ga sumewa sai yanzu na farfado daga suman danayi din.
Muryan su Amma naji suna fadin subbahanallahi hadiye ku kamata don Allah kada ta fama ciwon ta.
Sauke idona nayi kan Amma dake magana ina fadin don Allah Amma ku bari in tashi ina son ganin yaya umar yanzu don Allah Amma ki taimakeni in ganshi kofa sau gudane zan natsu wallahi.
Umar yana nan A ruwa saidai shima a kwance yake yana jin jikin shi don sun mashi rauni a lokacin da suka shigo gidan.
Innalillahi wa ina alaihim raji,un Amma sun jinwa yaya ciwo wa yan nan mutanen wasu irin mutane ne su marasa imani.
May mukai masu suka zo muna a wanan dare haka harda bindiga suna harbi kamar munyi masu wani laifi a rayuwan mu.
Shigowan yaya habbib tare da wani likita yasa na mayar da kallona garesu ina fadin din Allah yaya habbib ka kaini wurin yaya ina son ganin yaya insan halin da yake ciki don Allah.
Za a kaiki zahra ki kwanta ki huta shima din yana dakin hutu a yanzu haka ba a son a dame shi.
Tau tau yaya don Allah a kula dashi da kyau tunda kana wurin nan kada wani abu ya same shi.
Za a kula dashi insha Allahu ai ya samu sauki sosai yanzu barci kawai yakeyi daya samu.
Idona na mayar na lumshe hakan bai hana hawaye biyo gefen idanuwana ba a hankali suke gangarowa daga cikin idanuwana.
Barci ne ya kara daukeni a hakan sai lokacin yaya habbib suka fice daga dakin shida likitan da suka shigo a tare.
Yana ganin nayi barci yasa shi fita dakin ranshi babu dadi a lokacin muryan mama hadiye ne yaji a bayan shi ya dakatar dashi daga tafiyan da yakeyi.
Ya juyo yana fadin mama ana kan bincikin har yanzu ba a gane komai ba don kin san suma a bangaren su ai ba karamin shiri sukayi ba kafin su diro masu din gidan.
Allah dai ya tona asirin kowaye ke da alhakin wanan abin da gagawa mama hadiye tace tana hawaye.
Yanzu yaya ake ciki zancen shi umar din kai ya girgiza yana fadin har yanzu dai bai farfado ba sai dai yana numfashi kamar yadda yakeyi tun dazun.
Nan dai zuwa safe idan munga halin da yake ciki zamu nemi transafer zuwa Abuja mu gwada can mu gani.
Allah dai ya tada kafa ya bashi lafiya ita Fatima din sai zuwa yaushe za a sallameta ne don naga kamar dan damuwa ne kawai ke damun ta da firgici.
Eh to yanzu dai likita ke fada min cewa sai nan zuwa safe itama idan anga yadda jikin nata ya kasance.
To Allah ya kaimu mama tace tana juyawa zuwa dakin da nake kwance a ciki ta samu amma ta shiga yin alwala don yin sallah la,asar da yayi.
Tana fitowa itama mama din ta shiga don dauro alwalan tayi sallah fitowan ta yayi daidai da zuwan mamu da hjy maryam tare da kawu.
Abincin dake hannun Nura ya aje yana kallona suma din hankalin su a kaina yake mama ta fito take masu sannu da zuwa.
Suka karba tare da tambayan ta yaya mai jikin tace da sauki don ta farfado dazun sai dai damuwanta shine a kaita tana mijin ta don Allah.
Innalillahi suka furta Hjy maryam tace wanan daukan alhakin dame yai kama don Allah mutum a gidansa yanzu bai tsira ba wanda ke kan tafiyan ma haka ba a barshi ba.
Imani da tausayi ya fice a zukatan mutane sai son kai da son duniya shine abinyi a yanzu ido rufe.
Umar dai ba wani mai rigima bane balle ace wani abu ya hadashi da wani akai mai haka.
Yanzu ai ba sai kayiwa mutum komai ba zaiyi kokarin rabaka da duniya kawai lokacin muke da Allah ya fada shine ya fara gabato muna ubangiji yasa mufi karfin zuciyan mu dai suka karba da amin.
Dakin yai shiru sai kukan Abbana dake tashi kawai wanda su mamu suka shigo dashi don yadan sha nono idan na falka.
Don tunda na fadi aka daukoni sai aka mikawa mamu shi a can ya wuni gidan mu wurin su mama din duk da kowa ranan ranshi babu dadi kowa babba da yaro daya shafe mu yana cikin tashin hankaline.
Asibitin kuma yana cike da yan uwa da abokan arziki har ma da wa yanda ba,a sani ba a lokacin.
Kawune ya kawar da shiru ta hanyar tambaya wai shi fa tun safe da abin nan ya faru baiga wanan yarinyar ba da akace itama tana kasan kuma ai dole tana cikin gidan ai da abin ya faru ko ?
Wa ke nan Alh hjy maryam ta tambaya tana kallon kawu din yace dayan matar tashi mana ai naji ana fadan tana kasan nan ko ?
Laila kuwa merry din tun ganin safe da nayi mata a gidan ban kara ganin ta ba mama hadiye ta fada.
A jiyan zuciya mamu tayi tana fadin yarinyar nan sayadi kamar mai duba a jiyan fa ta kirani muna waya da yamma take fada min.
Cewa ita dai gabanta sai faduwa yakeyi tun zuwan merry din kasan nan danayi mata fada kan hakan .
Sai cewa tayi ita tasan ko waye merry din don halin black American da nakeji merry din tana dashi sak.
Don haka ita dai bata yarda yaran nan su zauna a gidan ba dole Allah zata kawo min su su kwana biyu a waje na.
Nace ta bari sai Alh ya dawo zan fada mai zuwa dare kuma ta sake kira tana fadin taji shiru shine ta bugo min don gaba daya ta kasa natsuwa da hakan .
Nace ban fada ma Alh ba do bai dade da dawowa gida ba a lokacin shine fa tace gasu nan yanzu zata saka akawo su idan daga baya zanwa Alh bayanin zuwan nasu.
To zuwan nasu ne yasa na manta in fada ma Alh don yaran sun shagalar dani wallahi sai gashi kuma mun tashi da wanan maganan yau na tashin hankali haka.
Lalai akwai ayan tambaya a nan don wanan magana yayi kama da batar ita merry din su hjy ya kamata a tambaya ina ita merry take aji ko a gidan ta kwana itama jiyan da abin ya faru.
Gidan ta kwana yaya don na ganta da mukazo da idona sai hjy maryam tace tabbas tana gidan don itace ma ta ke kururuwan da Alh balarabe yace a daina kuka haka.
To ina wanan yarinyar ta shiga yanzu ko dai tana gidan ne don taga kowa hankalin shi yana ga wa yan nan kamar an fita batunta an ware ta daban.
Bani tunanen haka Alh inji hjy maryam yanzu dai habbib ya kamata ka sanarwa komai don a bincika inda take din ko ya sani shi.
Ina zai sani tunda shine tsaye a kan komai tunda aka wuto da umar asibitin nan yake nan ban sa ya koma gida ba har yanzu ma mama hadiye ta fada.
Kawu yace to amma dai kun san wanan maganan ba abin kyalewa bane don dole ne mu san halin da yar mutane take ciki kasa ta salwanta kuma.
Ko tana daki don bakin ciki ta kulle kanta don shi kafiri bai san yarda da kaddara ba idan tazo mashi.
Waya kawu ya dauko daga aljihun shi yana neman layin habbib din ya fara kira sai kiran ya shiga.
A daidai lokacin ne kukan da Abbana keyi ya falkar dani daga barcin na bude idona sai akan su kawu din da matan shi dake tsaye a kaina lokacin.
Kallon yaron dake miko min hannu zuwa wurina don ya karbi abincin shi sam yaki sakewa a gidan mamu dukda mariya da fauziya dake gidan tare da yan uwan shi a lokacin.
Kawu yace min sannu Fatima ya karfin jikin kuma da sauki kawu na bashi amsa sai hawaye.
A daidai lokacin ya dauki wayan suka fara magana da yaya habbib a waya kan zancen merry din da ba,a gani ba a lokacin.
Ya juyo yana gab da fita dakin yana fadin ku mikashi mana ta bashi nono tunda ta tashi tun safe yake wanan kukan saboda firgitan da yayi.
Yana fadin haka ya juya ya fita daga dakin ita kuma mamu ta miko min Abba din dake kuka ta hanyat shi fidar dashi saman gadon da nake kwamce din.
Ita ta gyara muna kwanciya da yaron duk su mama d hjy suna kallon mu gwani ban tausayi damu lokacin.
Kawu sunyi magana da yaya habbib yace shima ta fado mai a tai da bai ganta ba asibitin tun dazu.
Dkn Allah ayi kokarin nemo inda take kada yar mutane ta salwanta kuma muna cikin garin nan.
To daddy ya amsa yana dauko wayan shi kake a cikin aljihun yana neman wani ashe hjy yake kira don ya tambayeta ina merry din take ne .
Hjy jiki na rawa ta dauki wayan tana zaton za ace wani abu game da yaya umar don haka tayi saurin daga wayan don gani layin habbib din ke kiranta dan jin halin da umar din ya ke ciki a lokacin.
Saidai sabanin jin bayanin komai daga gareshi da tayi yake tambayan ta ko merry na gidan do bata asibiti tunda suka zo nan.
Ina zan sani tunda ba nan take shigowa ba balle mu sani don Allah idan nafisa na kusa ta duba muna ita a bangaren ta ko tana gidan.
Nafisa ta kalla kafin tace ni ba wanan ba yanzu wani hali dan uwan naka yake cikine wai kun barmu nan a duhu haka babu labari.
Yace mama sai dai addua ga yaya gaskiya don yanzu shi yafi bukata a gare mu tunda har harbi biyu sukai mai da kafa da kirji kinga dole ya shiga wani hali a yanzu.
Shiru tayi ba tare da ta kara furta komai ba sai can ta kalli Nafisa tana fadin wai ki duba mashi wanan yar waje din ko tana gidan nan.
Nafisa tana kunkumi ta mike zuwa part din don dubawa sai dai tana zuwa ta tura kofan ta sameshi a bude babu kowa a ciki ta dan duba har bathroom nan ma bata a ciki ta fito ta bude wardrove din dakin dakin sai dan daidaikun kayan merry din ta gani a ciki.
Alaman dai babu mutum a cikin dakin na dan wani lokaci ke nan ta fito ta fadawa hjy abinda ta gani a dakin.
Hjy dasu mama sukace ta duba waje ta tambayi masu gadi ko sunga fitan ta .
Masu gadin sun tabbatar mata ba, a dade da kai maigidan asibiti ba ta fito wata bakar motace tazo ta dauke ta da yar jakkar kayan ta.
Komawa tayi ta fada masu habbib hjy ta kira take fada mai komai kawu dake gefen shi yace shike ban zancen yarinyar nan ya tabbata kan matar nan da alama fansan yarta tazo dauka gareshi dama.
17/11/2021, 07:26 – ????????????: Bai bata lokaci ba wurin kiran dansandan dake kula da case din yana bashi bayani kan zargin merry da kuma batan da tayi.
Dansandan yace gasu tafi don du kara daukan bayani kowa dake gidan lokacin da abin ya faru.
Cikin yan mintina suka shigo asibitin a nan suka samu yaya habbib don jin karin bayanin kiran da yai masu din.
Kara maimaita masu bayanin dayayi mai a waya yayi suna rubutawa a takarda kafin su ce suna son duk wanda ke gidan a wanan daren zasu gana dasu daya bayan daya.
Wake cikin asibitin nan a cikin su eh akwai matar maigidan wace ke kwance a yanzu da take jin jiki sai kuma dayan maigadin da aka harba dayan kuma ya mutu tun a lokacin da abin ya faru dashi.
Ok ko zamu iya ganin wani daga cikin su a yanzu dansanda yace yana tambayan likitan sai a lokacin likitan ya dan gyara tsayuwa yana fadin.
Da zaku barsu har zuwa gobe don lokacin hankalin su yadan fara kwantawa suna cikin dan hayacin su zaifi sai ku dauki duk bayanin da kuke so a garesu.
Ba matsala dansandan yace ko akwai wasu da zamu iya gani bayan wa yan nan din yaya umar yace eh akwai wani mai kula da duk wani al,amarin gidan tare da matar shi da suke a gidan lokacin da abin ya faru.
Ok yana ina yanzu ya habbib yace zamu iya samun shi a gidan yanzu don ko yaushe shi yana gidan bai faye fita ba.
Zamu iya zuwa yanzu mu ganshi idan ba damuwa ya fada yana kallon habbib din yace No problem zamu iya zuwa mu ganshi ai da haka suka bar asibitin a tare.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button