NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:21 – ????????????: ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA MUSULMAI , , , ,

Saida ta dan kura min ido na wani lokaci nima kallin ta nayi ido cikin ido kamar yadda take kallon nawa ba tare da yau naji wani shayinta ba ko kadan atare dani.
Karfin adduan mudulunci ke nan da hausawa ke fadin addua makami mumuni na gwada a gare ta.
Fatema nazo wurin kine da magana don nasan zaki fahinceni fiye da maigidana ta fadi tana kalona ido cikin ido.
Nan nace Allah yasa abinda zai yuyune kikazo dashi ta kara kallona karo na barkatai tace ko zaki tuna wancan karon kin tafi ba tare da sanun mu a gidan nan.
Kan wani dalili da nake zaton ko kin sanshi ko baki sanda zancen ba wanda ba wani abu bane sai zance yata guda daya tilo da nake da ita.
Kallon ta nake a cikin mamaki don ban san may take son fada min ba lokacin sai zuba take.
Nasan da biyu kika zo kasan nan kada ki dauka ban san may ya kawo ki kasan nan ba Fatema ?
Da sauri ba dago ina kallon ta cikin mamakin jin tasan zancen auren mu da yaya ashe dama nunawa ne batayi ba.
Nayi kasa da kaina cikin kunya jin tasan mijin ta na aure na bata nuna min komai ba.
Saida naji tace don kawai ku dauke wa yata hankali ga addinin mu aka turoki kasan nan ki zauna damu.
Saidai baku san cewa mu din dagani har yata ba a London muke zaune ba don haka nazo da murya mai kaushi don baki warning kan yata.
Wanan can karon kin fada mata abinda bata taba sani ba zancen ku yan uwantane kuma tana da grany da aunts da sauran su a Nigeeia.
Wanda da kyat na samu ta bar zancen nan a ranta don haka nake son inyi warning din ki wanan zuwan kada ki fara ki shiga harkan yata har ki fada mata wani zance gamay daku can .
A jiyan zuciya na sauke da gama adduan bakina na kalleta jin inda ta dosa na dakatar da zancen ta da fadin .
Nace wait merry zancen fadin wai ya takice ko wani abu duk bai taso ba don zaki iya fadin haka a yanzu saidai nasan nan gaba fadan hakan zai maki ciwo.
Don ko wani dan Adam yana daraja danginshi ne a duniya yana basu girma da sanin kimar su kada ki zalunci yarki don wani manufa naki merry bance ko anty ba wanan karon.
Kallona take da mamaki nace yes idan Amina bata nemay muba a yanzu nan gaba zata iya neman mu dole ne wanan sai ya faru.
A yanzu zanyi kamar yadda kike so merry don ni ba wanan ne ya kawoni gidan nan ba nazo nan bisa tursasawan dan uwanane kawai.
Yar kice Amina saidai ki sani nan gaba ba da yarki kawai yaya zaiyi alfahari ba don zai iya haihuwan wasu da wata mace yan uwa da dangi kaf su sosu a bar taki a gefe yadda kike so.
Shin idan anyiwa yarki hakan zakiji dadi a rayuwan ki kuwa naji daga yau na daina kulaki har yarki.
Saidai ki sani gida daine gidan dan uwanane ina da right din shigowa kamar yadda kema yan uwan ki suke zuwa duk lokacin da suka ga dama.
Maimakon inga bacin rai ga merry dake min wani irin kallon mamakin yadda na tsaya ina fada mata magana haka sai naga murmushi a fuskanta.
Tace kinyi kokari wurin fada min wanan magana saidai zan so ku san cewa dani da yata yanzu keda iko da komai a gidan nan na Omar.
Don nice matar gidan queen kuma diyar mu ce kowa a kasan nan ya san da hakan so banga wani dalili da Omar daku yan uwanshi kuke kokarin sakamu gaba hakan nan ba ?
Dan murmushin karfin hali na sake don maganan ta ya razana nani sosai jin abinda tace dani yanzu saidai ban nuna mata razana na ba kadan lokaci.
Komai zaki iya fada a nan merry saidai kada ki manta kin aure hausa man wanda keda addini daban da al,addu daban da naki ki rubuta ki aje komai zai yi faruwa daga baya wanan haka yake.
Wani kallo tayi min tare da tafa hannayen ta tace yarinya kinyi kokari kin nuna min aikin ki yana tafiya daidai a yadda wanda ya turo ki ya koya maki karfin halin jajircewa don yanzu idanun ki sun nuna a bude suke sosai.
Dama nasan da zaman ki a cikin dangin Omar kina daya daga cikin masu kyamata na tun farko saidai darajan mahaifiyar ki da kimar ta ba zai bari in dauki wani mugun mataki a kanki ba don ni mutum ne da bana mance halarci a rayuwata.
Nace realy ta gyada kai alaman kwarai kuwa don steps mother tayi min abinda ba zan taba mantawa ba a rayuwata danaje gidan ku.
Kin san da hakan kike kirarin cewa wani aiki aka turoni yi a kanki da yarki in ma wanan kike tunane ki cire a ranki don ba wanda zai tsaya yana wahal da kanshi kan mijin ki ko yar ku don ba shi kadai iyayyen mu suka haifa ba.
Kin san mu musulmai wanan ne fa,idan yin aure gare mu fiye da mata daya da kuma yara da yawa don idan wata ko wani ya kika ba zaka rasa wanda zai soka ba.
Don haka cewa Umar nakine keda yar ki ina son ki gane cewa kin makaro ga hakan don dai shi din musulmi ne mai alfahari da addinin shi.
Kofan a bankado da karfi ya Umar din ne a tsaye yana muna kallon tuhuma dukkan mu gaba daya wurin.
Merry may hakan ke nufi ne ya tambaya lokacin da yake karasowa tsakiyan dakin da tarin tambaya da fargaban abinda muke tsutaunawa a tsakanin mu.
Don yanayin kowan mu ya nuna ba maganan arziki mukeyi tsakanin muba a lokacin yadda yanayin fuskan kowan mu yake hade.
Sake tambayan ta yayi may ya kawo ki wurin ta yanzu bayan ki san ba lafiya ke gare ta ba kece kika matsa tazo nan ko zata samu karfin jikin ta.
Wani kallo ta watso min don amsan da bata samu bani ba ya shigo yana cin zuciyar ta.
Banga alaman mara lafiya da kake fadi ba a nan don wanan yariyar alama ya nuna min garau take ba abindake damun ta.
Yayi mata wani kallo shekeke yace zaki iya fadan hakan don ciwo ba a jikin ki yake ke da yarki ba ko ?
Tayi mai wani kallon wullakacin ba tare da yin magana ba ta fice daga dakin tana fita ya juyo yana min kallon tuhuma ?
Na kawar da kaina daga kallon shi da sauri yace may kika fada mata yanzu na juyo ina kallon shi nace amsan abinda ta fada min kawai.
Kamar zai sake magana sai kuma naga yaja ya fita dakin da sauri ya banko min kofana kafada na daga irin mai nuna ko a jikina.
Dakin barcin su ya nufa a nan ya samu merry tana zariyo a tsakar dakin tana ganin shi ya shigo ta tare shi da fadin sister din ka ta fada min magana masu zafi Omar.
Yace kamar yadda kema kika je kika fada mata ko wanan ne dalilin da yasa kika yaydareni akan a kawo ta nan zaki kula da ita ?
Kashedi nayi mata a kan diyata dani sai na fahinci yanzu yarinyar ta wuce yadda nake tsamanin ta.
Don ta fada min abubuwan da tun farko hankalina ya kawo a kanka rashin wayau ya hanani gane hakan da wuri.
May ta fada maki ya tsure ta da ido yana tambayan ta kasa bashi amsa tayi sai hannayen ta data dunkule tana dukan juna dasu da gani dai tana cikin wani irin yanayi lokacin na bacin rai.
Ya gaji da tsayi don jin bai samu amsan tambaya shi ba gun ko wacen mu ya nufi gadon kwanan su zai zauna tace.
Omar muna nan akan alkawarin mu dakai ko ka canza ra,ayin ka garemu yanzu yayi murmushi may kama da yake yana kallon ta yakai zaune yana fadin wani alkawari nayi maki ada da kike tunanen zan canza yanzu.
Dole in tambaye ka don abubuwan da nake gani dama wanda yar uwanka ta fadamin yanzu sun sa na shiga halin tunane ?
May ta fada maki gamay dani wanda har yasa kike ganina mai karya alkawari gareki ?
Kallon shi tayi tai murmushi ta karaso bakin gadon ta zauna ita ma shiru sukayi na dan lokaci yayin da shi yaya yake jiran amsa a gareta na abindana fada mata din.
Don a tunanen shi na fada mata abindake tsakanin mu dashi na aure hankalin shi inyai dubu ya tashi maimakon ta bashi amsa sai ma yaji ta buge ga waya da abokanta na nan da zasu zo su fita.
Ganin ta kyale shi ga dare yayi lokacin ya kasa zaune ya kasa tsaye a dakin kamar ya sani ya fito a daidai lokacin da nima na fito rataye da jakkan dana zo dashi da zuman barin gidan.
Ke yace a cikin wani irin tsawa daya daka min yana fadin ina zaki yanzu ciki wannan daren haka ?
Kina da hankali kuwa waima ko ke kinsan darajan kanki kuwa zarah da bin dare a kasan nan bai zama maki komai ba?
Hawaye suka soma zuba min a idanuwana shifa ya daukoni ina gidana zaune cikin rufin asirina zuwa gidan matan shi.
Tazo tana fada min maganan banza akan abinda baishafe niba yanzu kuma har yana kirana da ban san darajan kaina ba.
Ganin irin hawayen da nake daga inda naja na tsaya yanayin fuskan shi ya dan sauya kadan ya tako zuwa gareni yana fadin .
Kiyi hakkuri ke kika daukan min alkawarin zaki taimaka min kan yata sanin haka da merry tayi zuwan ki na iya jan ra,ayin yarta zuwa gare ki yasa tayi wanan zaman dake.
Kada kice zaki fushi ki kara barin gidan nan don shine burinta taga kowa nawa bai mamay mu ba da zakibi daren nan yanzu baki tsoron wani abu yaje can ya samay ki a hanya kasan nan fa ba kamar tamu bane Nigeria.
Yaya haka ya isheni na fadi a cikin kuka tun yanzu matar ka bata san alakan dake tsakanin mu ba tana nuna min hakan ina ga ranan da tasan cewa ni matar kace ta sunna ?
Idan ta sani saimay zara iyaka dai rabuwa zamuyi idan bata iya zama dani dake don ke ba saki a tsakanin mu har abada.
Ka daina fadin haka yaya kada ma kasa zama da kaida nakeyi na har abadane tsakanin mu ko ka manta da abinda ke jiran mu a gidane bayan wanan ?
May ke jiran mu a gida zarah nace cikin kallon shi da mamaki yaya har ka manta da hjyn ku tana kalubulantar auren mu ne.
Dan murmushi yayi yana fadin wanan ba matsalan ki bane tsakanina da mahaifiyatace zarah don haka bai shafeki ba yana matsowa inda nake yake magana.
Yace ki duba yadda kike shirin fita a gidan nan wai mako kinsan darajan auren dake a kanki kuwa zarah ?
Kina da darajan da babu wani mahalukin da zai ganki a haka bai kara kallon ki ba kallon kaina nayi don sai a lokacin naga yadda nake shirin fita daga gidan dagani sai dan riga irin tasu dake saye a jikina lokacin.
Kunya da nauyin hakan ya kamani koshi da yake kare mun kallo haka a lokacin jin motsin merry data fito ta tsaya tana kallon mu bai hana shi riko hannuna ba ya rungumay ni a jikin shi yana dan bubuga min baya alaman rarashi.
Jin nayi shiru yasa ya ja hannuna zuwa dakina sai da ya kara ban magana ya fita daga dakin sai bayan fitan shi daga dakin na sauke ajiyan mikewa nayi zuwa kofa na rufe da key na dawo saman gado har lokacub ba komai a cikina da naci tun karyawan safe daya tursasani nayi a gaban shi.
Wani tunane yazo min nayi zubur na mike zauna daga kwanciyan ruf da ciki danayi da farko.
Na fahinci akwai rikici a tsakanin yaya da matar shi a wanan yan watannin da suka shude duk dai a kan rikicin yarsu ce hakan ke faruwa tsakanin su.
Daman kine wanan sayadi damaki ne hakan a ruwa muryan mamu da Amma ne ya ziyarci zuciyana lokaci guda.
Ba sai mun koya maki yadda zaki samu kan mijin ki ba kije ilimin ki da kika samu ya fitar dake a matsayin ki na diya mace.
Abinda zan kara maki shine juriya da hakkuri da al,amarin rayuwa sayadi sai ladabi da biyayya da zaki kara dashi mamu ke fadin haka lokacinda Addah ta kaini gurinta muyi ban kwana.
A ruwa ke mace ce don haka ba sai na koyar dake komai saidai zan kara da hakkuri da kwantar da kai ta haka ake cin ma manufa a saukake A ruwa.
Nasan zaki iya kawun ki baima saudauki zaben banza ba don kece kika dace da daidai da rayuwan shi ki kula da addinin ki a duk inda kika riski kanki addua ko takobin mumune Aruwa a kula da yawaita yin addua ko yaushe.
Amma ce take fada min hakan wani dare saura kwanaki bukin mu na dawo daga misau ina korafi gareta na banyin aure mai mata kafira.
Yo itama kafira ina tasan kissa irin namu na nan a ruwa ko zama gidan nan kadai ya isheki koyon duniya abinida iyayyenku keyi a gidan nan.
To ta ina zan fara wai idan ma har na saki jiku dashi na dan lokacine wanan kulawan dayake bani don kawai sun samu matsala da matar shine har nake samun sakin fuska gurin shi kwana biyun nan.
Ranan da suka daidaita fa tsakanin su suka koma shiri da ita idan na sake jiki har sabo ya shiga tsakanin kwana biyu kaina abin zai koma tunda ba sona yake ba yadda yake fadi kuma ya nuna.
Ke nan nice da mahaifiya ta za a cuta a karshe tunda nice zan yi hasaran kimata da martabata na mace .
Ni da wanan zaman ai garama ina gidan mu gaban iyayyena yafi min zama mai kamar ukuba dashi.
Kaina gyada ina fadi a fili anya nayiwa kawu adalci idan naki dan shi da yake sa ran gyarauwan komai a dalilina.
Ya zama dole dai in bi shawaran mutane in fara wani abu nima a bangarena kodon wanan bakar arniyar mai zagin iyayyen mu a gaba don na kula taki jinin kawuna don dashi take adawan ta.
Ranan dai barci rabi da rabi nayi shi gidan wasu na fatan suje kasan waje suji dadin rayuwan su ni kuma da na samu zuwa ga irin ukuban zuciyar da nake ciki tun zuwana.
Washe gari kodana tashi na gama yanke shawara a raina wanka nayi tsab na shirya cikin green din kaya duk da ba kala na bane kayan dai sun karbi jikina sosai nayi rolling din kaina na tsaya gaban mirrow ina karewa kaina kallo.
Ban fito ba saida na kara shafe jikina da oud dina masu kamshi sosai tun tun karowana falon kamshi turaren jikina ya daki hancin su.
Dago kai sukayi suna kallona direct wurin table din abincin na nufa kai tsaye fuskana a washe kamar ba wani abindaya faru daren jiya din.
Shina fara gaidawa kafin in juyo ina kokarin zuwa wurin yar su nace anty merry good morning ina zaton ba zata amsa min ba sai naji ta amsa min gyatsire da morning dear taci gaba da cin abincin ta.
Dan rugumar yarinyar nayi nakai mata kiss a goshin ta tare da fadan morning my dear ta tabure fuska can ta dago tana fadin .
Ina kikaje bana ganin ki ina tambayan Mumm tace kin koma garin ku da zama dan kallon uwar yayi ya kawar da kai nace da yarinyar ina zama yanzu ai gani na dawo gare ku kuma.
Tace idan zaki garin ku zakije dani ta fada a marairaice nace why not idan kina son zuwa.
Ina kallon yadda merry fuska ba annuru ko kadan yarinyar zata kara magana ta dakatar da ita ta hanyar fadin will you kep quaint dear ?
Da sauri ta mike ta fada jikin uban tana fadin daddy mumm tana min shauting ba dalili.
Dan rugumay yarinyar yayi yana shafa bayanta a hankali ta lafe saman jikin shi abincin da baici gaba da ciba ke nan ya barshi.
Ni dai na gama na mike na koma saman kujaran falon na zauna ina karatu a cikin wayana sam na manta da wani zancen new year sai lokacin da naga merry ta fito cikin shiga ta alfarma tana fadin zasu church wurin addua,a ita da yarta yarinyar tana bata fuska rai bace.
Daga sama uban ke jefo masu baki akan idan yarinyar bata zuwa ta barta a gida ta gallamai wani harara ta fisgi hannun yar nata.
Kamar zata wuce bata sallamay ni ba komai ta gani tace sister inlaw zamu tafi sai sun dawo nayi mata tare da fadin queen tayi min addu,a idan sunje kila kalami na yaiwa merry dadine tace zasuyi suka fice.
Da farko ganin da nakewa yaya haka sai nake daukan shi miskili mai ji dakai kamar yafi kowa marason magana ko wani lokaci a cikin daure fuskan shi yake.
Sai dan zama na dasu London din nan nake fahintar koshi waye sannu a hankali don na fahinci baison ganin mutum a cikin damuwa ko kadan bai kula da mutane amma idon shi na akan duk wani na tare dashi.
Gashi dai yan kwanakin nan yana nuna min kulawan shi amma ni sai kama jikina nake dashi ban sake mai don kada in wuce iyakata a ranshi.
Ina kwance a dakin nayi karatun Allah nayi na boko na gaji nayi barci sai da azahar na mike don inyi sallah bayan na idar na zauna bakin gado ina game a wayana don haka hankalina ya dauke banji shigowan shi dakin ba.
Muryan shi naji a kaina yana fadin waike baki gajiya da game a wayane haka ko rashin nayine wanan duk.
Ki tashi mu fita zuwa cikin gari tunda ke zama wuri daya yana damun ki nasan nan din ma a takure kike yanzu.
Dago kainayi jin yakai aya nace barni na koma da sunana na fatimana gida kada matar ka ta kara zargina kan wani abin tunda bata san koni din wacecen kaba har yanzu.
Maimako maganata ya bata mai rai sai naga ya dan kara matsowa har inda nake yana fadin kina tunanen ina tsoron fada matane ko may ?
Sai da yayi min wani lalatacen kallo kafin yace ni ba irin mazan nan bane masu tsoron matan su har in tunanen ki yana baki don kada ran merry ya baci ne nake maki hakan.
Ciki ciki nace ga abu a baiyane kuwa zaka wani noke yanzu don kaga bata gidan ai kayi dadin, , ,
Tsawa ya daka min tare da fadin ke kada ki bata min rai don kinga ina kokarin tsare hakkin ki dake kaina.
Na dan fadi a fili ina gusawa daga inda nake zaune nace aini bance sai an sauke min wani hakki ba can a barni inyi rayuwata ni kadai mana agani.
Zarah ashe rashin kunyan da ake fada naki har ya kawo kaina har kin kai ki kali idona kina fada min magana kai tsaye.
Kina nufin dan ance kina matata zaki fada min magana irin haka ki kama kanki yarinyar hakan ba yana nufin wai harki rainani bane don kina kurin ina mijin ki.
Duk da jan idon da yake min da nuna min bacin ranshi a fili hakan baisa na rufe bakina ba lokacin sai cewa nayi aini ba matarka bace zaman kanwar kace nakeyi ko dako gida muka koma .
Juyawa yayi zai fita daga dakin bayan hararan daya watsamin din sai kuma ya sake juyowa ya kalleni cikin na tsuwa yana fadin.
Da na dauka kina da wayau da zaki gane abinda nake nufi da yin haka gareki na dauka ko ban fada bake hakan ba zai damay ki ba.
Sai gashi ashe har yanzu wayau naki baikai ki gano hakan ba ba laifi nasan kina mutuntani a wani bangare sai dai kada zancen ki da merry yasa kice zaki rainani yanzu.
Na dukar da kaina kasa cikin karamar murya nace ni zancen merry bai shafe ba gareni ta fada min na fada mata don ba zata zagan min iyayyena ko yan uwa in kyaleta ba ko addinina.
Yace koma dai may ye ki sani aurena dake ba,ayishi akan so ko wani kauna ba anyi shi ne kawai bisa kaddaran rabon sai anyi don haka yadda kike jin ko maynene a ranki hakan kowama ke jinsa.
Don haka ki ban lokaci har in gama tsare tsarena kafin in waiwayo ki mu san mafita yana fadan haka ya juya ya fita baiko sake kallona ba.
Yana fita na fashe da wani irin kuka mai cin rai tare da kunan zuciya lokaci guda ke nan nazama matar kushe wace aka auro ta a bisa wani kaddaran.
Zuciya mai nashe nashe har ta fara naso min irin rashin mutuncin da zan kula mai idan mun koma gida yayin da wani bangare na zuciyana ke fada min in fito fili in fada matarshi gaskiyan koni wacece a wurin shi.
Tunda ya fita ba wanda ya kara leko dakin gama tun zuwana banga Greco a gidan ba ba hurmina bane don haka ban tambaya ba.
Ina idar da sallah magariba cikin ikon Allah sai ga wayana yayi kara na dago daga inda nake ina duba mai kiran wayan nawa.
Mamu nagani rubuce na dauka da sauri da sallama a cikin dakusashen muryata dana ci kuka dashi yau.
Shiru tayi ba tare da ta amsa min sallaman ba sai na fara sheshekan kuka muryan ta naji tana fadin sayadi kina son in daina kiran layin ki ke nan ko ?
Na daina mamu nace da sauri don jin abinda ta fada nasan kuma zata iya din ba iya fadi a baki tayi ba.
Ko mainene hakkuri da mika kai ga Allah shine maganin sa ai sayadi ba wai kukane mafita ba gare ki harki jawa kanki wani ciwo can.
Sayadi ina son ki sani daka cuci abokin zama gara ka barshi shi ya cuce ka kina dai gani na a nan bana yarda in wullakanta aurena sayadi.
Idan namiji ya cuceka ke mace ki daure ki zuba mai idanu saboda watarana ko ance yai hakan gareka ba zaiyi ba ai, kuka na somayi sosai don zanyi magana ta hanani.
Amma duk da hankan sai dana samu na furta abindake cin raina nace mamu yau yaya fa cewa yayi auren mu nidashi ba aurene naso da kauna ba.
Aurene da akayi shi bisa wani kaddara wanda sai dai mu barwa Allah lamarin sa abin mamaki amsar da mamu tabani a likacin shi yaba mamaki matuka don cewa mamu tayi ai ya fadi gaskiya sayadi.
Ehma ko ba auren kaddara din kukayi ba keda shi fada min dole sai kowan ku ya yaki zuciyar shi dama ai a zauna lafiya muddin kina son kici riban auren ki.
Ko ni da kawun ki an fada maki munyi wani soyayyane kafin auren mu da fada min da saka rana duk baifi kwana biyu ba tsakani.
Yanzu fa sayadi wa zai gane hakan akayi sai wanda yasan tushen labarin zai sani.
Shi hakkuri ai baibar komai ba da wansn wautan taki da kikeyi garama da Allah yasa ba a gida daya ya barki da kishiyar taki ba don da zuwa yanzu ta gane halikin na rashin hakkuri ta dan kara min nasiha akan in daure in kara hakkuri dai ta kashe wayata ta barni da tarin bakin cikina.
Ke nan kowa laifina yake gani akan auren nan shi basu ganin nasa ko kadan har zai fada min hakan mamu tace wai banda hakkuri ko din
mahaifina baya rayene yasa kowa baisona a duniyan nan.
Barci na samu ya daukeni a hakan bayan naci kukana na gaji can cikin dare ina barci na dinga jin kamar hayaniya a gidan tun ban falko ba hardai na bude idona tar jin hayaniyar yayi yawa yasa na sauko daga saman gadon ina saurare.
Muryan yaya nake ji sama sama hakan yasani komawa na kwanta don bai wuce wani abin ne tsakanin shi shida matarshi kuma.
Hayaniyan sai dada karuwa yake inda nake jin muryan wasu mutane na daban yana tashi.
Kamar in fita gashi barci yaki daukana kuma naga idan na fita na kula dasu kenan don ance tankawama yabawane.
Nan kuma wata zuciya ta tuna min da gargadin mamu na kada in sake in bari a gane ina kishi ko wani abu tambayan kaina nayi ni yanzu yayi to fita kawai zakiyi zuciyata ta bani amsa.
Gabanane ya fadin ganin harda yan sanda a gidan a hankali na taka zuwa inda dandazon taron yake ina sauraren bayanin dan sandan.
Daga inda nake na fahinci merry ce sukayi accident da suka fita ashe bayan zuwan su church da aka taso suka wuce yawon su na bukin new year.
A can ne suka hadu da wanan kadaran don tana a cikin maye wai ashe tun fitan shi daga dakina ake wanan rikicin ban sani ba yanzu ma yansanda sunzo tafiya da itane bayan ta gudu daga asibiti inda aka kwantar dasu din.
Ga bayanin dansanda dayayi karshe na gane har yarsu queen tana asibiti kwance wanan lokacin.
Ga uwar ta gudu ta dawo gida tabar yar can asibiti shine mijin ya kira yan sanda suzo hargida don ba zai yarda yarshi ta salwanta ba yace.
Kai wai wanan wani irin aure mutanen nan keyi na tambayi zuciyana hakan ina karewa yadda merry din ke fama.
Daga inda yake ya watso min wani irin kallo mai kama da harara har na dauke kaina daga kallon shi sai can na tuna a yanayin dana fito falon sake dan kallo shi nayi har lokacin yana watsa min harara hakan yasa na juya da sauri zuwa dakina na sako hijjab dina.
Sai dan ban sake fitowa ba ban kuma san yadda suka karkare ba a can don ban kara jin duriyan su ba kuma a gidan.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button