NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

Ayi manege yau ban samu natsuwan typing ba yan uwa sai kun jini kuma zuwa gobe insha Allahu.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:09 – ????????????: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHEEM YA FATTAHU YA SALAM, , ,

Sun isa lafiya inda ya samu abokan arzikin shi suna kewan shi sunyi missing din shi sosai musanman a gurin aikin shi mutane da yawa sunyi missing din shi gurin.
Tunda suka kaishi gida suka dire ya shige sallah ya gabatar da ake binshi yana gamawa yadan ci abinci don shigan dare sukayi .
Ya kwanta bai fito daga dakin ba saida hayaniyan su merry da akazo yiwa adduan kore mata evils sprit din da ta kwaso a Nigeria ita da baby ta da maigidan.
Pastor mahaifinta ya dauko masu dungurun gun don yin addua gare su don ma a ciki dare suka sauka da abin yafi nan don da church za a kaita ai mata wanan adduan.
Saukowa yayi yana saye da wando three quarter a jikin shi sai riga fara daya saka a jikin shidon shan iska.
Tunda yake saukowa yake kallon merry da take tsugun ne ta rufe ido hannaye ta na sama alaman roko take yi kenan.
Pastor da mahaifin merry sukai mai alama da yazo gurin adduan shi ma ya kalle su da mamaki ya kara tsare gida a fuskan shi don haka yake masu idan zasu tursasa shi yin wani abu na addinin su .
Pastor din yace ya kamata kaima kazo a kore maka evils din da suka biyo ku a tafiyan ku yace cikin kada kai banda matsala ni yana tafiya yake fadin hakan ys nufi hanyan fita daga wajen gidan wurin wani dan shan iska na gidan ya tsaya yana karewa dogayen gine gine garin kallo daga inda yake ya sauke ajiyan zuciya a hankali.
Dafa dan karfen dake gaban shi yayi yana lumshe idon shi a hankali babu abinda ke zuciyar shi sai tunanen abubuwan da suka faru zuwan shi nigeria suke dawo mai a rai.
Ya sauke ajiyan zuciya yana kara lumshe ido tare da dan damke karfe da karfi yana hadiyan zuciya.
Daidai lokacin mahafin merry ya fito yana bin kusurwan gidan yana wasu sambatu irin nasu na kiristoci da sukeyi wai ana koran shedanu a gidan .
Bai kula shi ba don idan da sabo ya saba amma shi ko a jikin shi duk wana abubuwan da sukayi yakan nuna takar bai san dunayi ba.
Inda har yakan basu mamaki irin taurin kan shi akan riko da addinin shi don basu san zai iya riko haka da addinin shi ba sai zuwan nan da sukayi nigeria ne merry ta tabbatar da idan tushen rikon addinin shi duk yan gidan su tana ganin kamar malamai ne don irin shigar su da suke .
Ita babu abinda ke bata mamaki kamar yadda har da kananun yara suke saka zunbulelen hijab da nikaf a fuskan shi tunda wanan yar ta step mum din don tun a waya ta labarta wa iyayyen ta wanan akidan na yan gidan.
Muryan maman merry ne ta zo inda yake tana fadin my inlaw ya hanya ya mutanen ka can ya dan lumshe ido cikin rasgin son nagana yace suna lafiya ta sake fadin .
Munzo kana kwance tu safe don yiwa merry addua ta samu kariya daga evils ayes ta haihu lafiya ita da baby ta su samu kariya.
Yana da kyau ya bata amsa da fadan hakan yana juyawa don barin gurin matar tana kokarin ganin ta jawo shi a jiki kamar yadda suke da dan cikin su.
Wanda daga hakan zasu yi amfani da daman wurin samun jawo ra,ayin shi gare shi na addinin su sai dai kuma yaron tauri ne dashi da rashin sabo sam baida yarda da kowa ko sakin jiki wanan halin yana matukar damun su a rai.
Tsoron su shine kada watarana yaja ra,ayin yarsu tace zata juye ta koma tasa a kidar wanda wanan babban kalubali ne gare su don su din suna da wani mataki a cikin church din su na shugabanci.
Haka zai zama abin kunya sosai a wurin su shine dalilin su na kin yin fushi da halayan yaron garesu na rashin yarda da amincewa dasu da baiyi ko wani lokaci.

NIGERIA
Tafiyan ya umar da sati aiyukan yan uwan uwanshi ya fito yana daya daga cikin wanda sukai hanya aka samu aikin don mahaifin su yayi iya kokarin shi a samun aikin abu ya faskara .
Gashi bai son zancen komawan su waje yanzu koshi umar din akwai dalilan da yasa ya barshi ya koma din don ya koma ya karasa.
Habbib yafi kowa korafin wanan tsayar dasu da akayi din wanda ba haka yaso ba yaso ya koma kamar yanda yayan nasu ya koma can.
Kawune ya fadawa sauran mutanen gidan inda suka dinga layi zuwa yin murna wa hjy jummai yar mulkin tana amsawa da kyat don bata so haka ba ita a nata ganin ai sirin su ne hakan ba dole sai kowa yasan da maganan ba a saka masu baki.
Itako abinda bata so ke nan kowa ya kama fada ana nanata magana ta dauki hakan da yawan saka ido ga mutum.
Wata rana kuma sai gashi umar ya bugo waya yana sheda masu haihuwan merry din wace ta haifi diya mace wai har anyi sati uku a lokacin da ya bugo wayan yace ya radawa diya sunan mahaifiyar su Aminatu.
Gida sunyi mamaki kwarai da jin hakan kowa na tofa albarkacin bakin sa ga irin halin umar din wanda shi bai damu ya fadawa yan uwa wani abin shi ba idan ba yaso hakan ba sai dai daga baya suji.
Hjy su tayi fada sosai kan rashin fada mata da baiyi ba da wuri lokacin da aka haihu din yace mama ni dai a nawa bangaren nayi wa yarinya huduba da sauran abin da ya dace ayiwa yaro idan an haife shi.
Amma ta bangaren merry ita har yanzu basuyi nasu bukin sunan ba tukun tace yau ga hauka ?
Kace sati uku da haihuwa zakace basuyi bukin suna ba har yanzu yace eh mama ga nasu al,adan ai yarinya zata iya kaiwa har wajen shekara ba ai bukin suna ba sai idan an shirya akeyi.
Tsuki hjy taja tare da fadin wanan bakin kwashe kwashen naka babawa mukan bai karamu da komai ba sai dadin ta kaici ni a ina na taba jin wanan shirmay haka ?.
Yace haka sukeyi ga al,adan yahudawa da suke koyo yasa na barta da akidar su hakana idan sun tashi sai suyi sai hjy tace sai dai kuyi ku tafi church ke nan har kai ana faman raye raye ko a can ?
Shi dai yai dariya kawai ba tare da ya furta komai ba sai ta kara fadin to kaga kamar yadda nace ma idan ta haihu zamuyi namu hidima a nan ya zama dole yanzu ka aiko da wasu kudi ayi don wancen da ka bayar nayi amfani dasu bayan wucewar ku.
Yace ai da kawai ku bari tunda ba mai jegon ma nan itama batai komai ba aiko kamar jiran take ta fadi hakan ta haushi da sababi sai daya koma bata hakkuri da baki tare da alkawarin zai aiko mata da kudin kamar yadda ta bukata.
Sai take fadin saura naji wanan zancen bakin mahaifin ku don yanzu na kula ko wanka kayi baka bushewa sai ka fada mashi ya sani.
Dariya yayi yana fadin kai haba mama ni di kuma kike wa wanan shedan haka ya dai samu har uwan ta sauka daga fushin data dauka dashi da farko.
Daga shi sai Aliyu suka iya bi da ita a cikin yayan ta idan ka ganshi miskili zaka dauka ta ko ina baida dadin sha,ani.
Sai dai abin ba haka ba don fanin mahaifiyar shi yana kokarin kare mata hakkinta sosai yana gudun bacin ran mahaifan sa fiye da komai a duniya.
Ba laifi hjy ta dan shirya dan kwarya kwaryan walima a gidan wai matar danta ta haihu yan uwa da kawayen ta aka taru a gidan tun safe ana shagalin suna.
Bata gaiyaci kowa na fannin kawu ba har matanshi sai dai hakan bai hana hjy maryam shiga cikin tsabgan ba don ganin kwam.
Mamu kan ficewa tayi abinta unguwa bata tsaya ganin takaici ba gidan sai data daidaici lokacin dawowan mu school yayi ta dawo gidan saboda yara.
Ni kan ban san da zancen ba mun dai dawo na samu gidan dankare da manyar motoci tun daga wajen gidan dole haka muka raba muka shiga ganin part din mu a rufe yasa naja kanne ba muka nufi gurin Amma.
Tafe nake amma tunane ya addabeni a rai na may ke faruwa a part din hjy yau naga ana ta shagali haka ?
Da sallama muka shiga na zube saman kujera ina cire safan kafana dana kanne na Amma ta fito daga daki jin motsin mu.
Tana fadin har kun dawo ashe agogon falon ta na daga kai na duba nace Amma yanzu kusan hudu fa don munyi jiran mamu bata zo daukan mu dole motar haya muka biyo.
Tace nima bansan ina taje ba tun dazun nasan dai fitan ta bai rasa nasaba da wanan taro da taga anyi yau gidan nan.
Da sauri nace wai Amma taron may akeyi ne haka a gidan nan yau naga motoci har wajen gida ga mata zaune gungu gungu a wajen gidan.
Sai da ta tabe baki kafin tace wai yau suna ake muna a gidan haka tana fadi tana juyawa da kai da gani abin bai gamshe ta ba.
Da sauri nace suna Amma wa ya haihu kuma tace wai matar dan uwan ku kafiran nan mana matar saudaki.
Kallon mamaki nayi mata ina fadin tau a gidan nan ake bukin ko suna kasan nan ne ?
Tace ina fa daukarwa kaine kawai irin na jummai data iya abin kwarai batayi sai abin banza.
Kai Amma ba danta take tayawa murnan samun karuwa ba taja wani irun tsuki tare da fadin Allah kadai yasan irin riban data samu aurin wanan bukin.
An fada maki jummai tana abu don Allah ne ita barta nan inda kika ganta da halin ta sai kurum kawai.
Abinci na tashi na dibanwa kanne ba tare da basu ruwa sun zauna suna ci ne mamu ta dawo part din Amma ta nufo don ta diba idan mun dawo.
Bayan ta ganmu ne sun gaisa da Amma sai Amma take tambayan ta ina ta fito sai data kai zaune take fadin ina gidan kawu cewa mahaifin ta don haka take ce mai kamar yadda yayan Amma ke kiranshi.
Gwaggo yau gidan bai zaunuwa ne yasa na dan fita zuwa gaida shi dama na kwana biyu banje can din ba.
Sai dai idan kina da jiyar fita dama kan wanan shirmay da ake zaisa ki bar gida nan don kawai guje masu.
Nikan mikewa nayi na shige dakin Amma don akwai kayana a nan wanka nayi na dauki bakar riga na saka tare da dauko wani dan gyale daura a kaina na fito na samu har mamu ta tafi part din ta.
Wani flat takalmana dake nan kofan Amma na saka ina fadin Amma zanje inwa su fauziya wanka in dawo tace kada ki dade ki dawo nace tau Amma.
Kidane yau yake tashi a gidan ga mata nan gungu gungu zaune saman fararen kujeru da akayo hayan su sai dai duk cikin taro banga yan bangaren kawu ba.
Wasu yan mata ne naga sun zubo mi ido har na kawo kusa dasu naji daya na fadin ai wanan ce yarinyar dama ?
Ashe ma ba wata babba ce haka dama gaskiya dai wanan sai dai in an kwan biyu kan auren su ni dai yi nayi kamar banji su ba sai daya tace uwar ta fa ta cusawa daddy su ra,ayin ta amma wanan ina zai kaita shida yake dan gayu yadda ya waye din nan.
Allah ya sauwake ai hanyar jirgi saban data mota sai suka kwashe da dariya dayan ta kare da fadin a to kwarya tabi kwarya dan uwanta badai a cikin dangin mu ba don su mama sunce ba zai taba yuyuwa ba wanan zancen.
Dan murmushi na sake a fuskana nace a raina kuna da gaskiyan ku komai akai muna baku da laifi don dole yanzu na zama mujiya a idon jama,a ke nan .
Ban kula da wata mace dake zuwa ba sai ji nayi na buge da mutum na dawo daga tunanen da nakeyi da sauri ina bata hakkuri.
Don maganganu yan matan yasa hankalina dagawa har na shiga tunane ban san matar tana tafe ba lokacin.
Matar na fadin ba komai sai jin muryan hjy maryam mukayi daga bayan mu tana fadin ke A ruwa kanki daya kuwa zaki bangaji babban mace kamar wanan.
Ban san tana tafe bane maman ikilima kuma na bata hakkuri ai, ta watsa min harara tare da fadin dallah rufewa mutane baki marasa tarbiya kawai har da baki ma sai kin nuna masu halin ki sun sani.
Cike da mamakin kalamin ta na waro ido ina kallonta matar ta sake fadin haba hankalinta ne baiya a hanyan ai bata san ina tafe bane itama asali nima waya nake ban san da zuw ba goan ta ba.
Wanan ma aiko ta sani hakan zatayi don rashin kunya da take takama dashi da jiji da kai kin dai ga inda abin arziki yake don haka a daina kwadayin shiga manya mutane don ba kamun kai.
Sai duk wa yanda ke wajen suka sako muna idanuwan su suna sauraren ta kamar daga sama mukaji muryan hjy tana fadin maryam may kuma ke faruwa ne nan ?
Yanzu Asma,u ta samay ni ciki take fada min magana mara dadi wai matar DG wanan yarinyar ta bangaza don kawai tana takama da rashin kunya har na waje su sani.
A tausashe nace maman ikilima ba bangazan ta nayi ba karo mukayi da ita kuma na bata hakkuri .
Acikin tsawa suna hada baki in masu shiru da rashin kunya suna magana ina fadi don banda kunya ta tara taron arziki don bakin ciki zan wargaza mata taro.
Watace da ganin ta malama ce suna zaune a gefe ta daga nikaf din kanta sama tace haba ku dinga kyakyawan bincike kafin ku yada magana mu nan muna kallon abinda ya faru asalima ai matar dg itace ta buge yarinyar ba yarinyar ta zo ta bugeta ba.
Amma duk da haka hjy lami bata iya tausasa harshe ga manya ita ta bada hakkuri zata tsaya muna haka a kai kimkam.
Matar dai ta sake fadin yo ai wanan yarinyar nada kirki tunda tana bugeta ita tashiga bata hakkuri dazun akwai wata yar bakar yarinya data fito wancan part din kunsan mata kadani tayi a gidan nan cewa part din hjy maryam take nunawa.
Hjy jummai tace yaran banza ne kawai an tara muna su a gida babu tarbiya suna abun da sukaga dama wa mutane.
Kin fito kamar wata bakuwar buzuwa dake kina baza ido don gulma wa gaiyace ku gaiyan tsiya.
Na daga ido na kalli hjy dake ta muzantani a gaban bakin ta uffan ban furta mata ba har sai da matar mai kama da malama tace min ke wuce ki tafi inda zaki.
Jummai idan ta samu fada bata jin assh na juya nacewa matar nagode hjy tace kinji kilibibin ko ?
Wa yar da kike gani ta koyi kilibibi har ta gaji a gidan nan haka kawai zaki zo min cikin tarona kamar bakuwar shedan.
Dariya yan matan nan suka kwashe dashi har suna tabawa tare da fadin wuuuu.
Mama hadiye dake tsaye tace amma dai kunji kunya wallahi don kunyiwa a ruwa haka a cikin taro shi zai zama may ?
Tunda duniya ta wanke ta ga gaskiya ana fada kin fito da abinda ke cikin ki a fili a bainan jamma, a hakan ne zai hanata shiga gidan danki don kin muzantata ko may ?
Hjy ko tace bakikai labari ta hau mama hadiye da fada sai kallon ya dawo gare su nikan har na shige part din mamu ina jiyo hayaniyar su wajen.
A take zazzabi ya sauka min na karasa falon mamu da kyar na haye kujera na kwanta ina tunanen wanan wani irin kiyayya ne hakan tsakanin mu da matan nan.
Ina nan zube saman kujeran idanuwana a lumshe naji mamu tafito daga daki tana ganina sai tayi turus a wurin tana kallo na.
May ke faruwa ne waje sayadi naji kamar muryan maman ku hadiye da hjyn su salma ?
Nace sune mamu fadan dani ake mama ta shiga wai na bangaji wata mata alhali matar ta fada masu ban bangajeta ba itace ta bugeni bata gani ba.
Sayadi mai ya kaiki guri su don Allah mamu ta fada a cikin wani murya na bacin rai nace wallahi mamu banje gurin su ba na fito inzo inyiwa su fauziya wankane muka hade da matar a hanya na karasa idona yana kawo hawaye.
Sayadi banson abin fitina sam wallahi shiyasa kikaga na bar masu gidan tun safe ashe ban tsira ba daga sherin su.
Mamu ta ban tausayi yadda tayi maganan ya nuna ta gaji da wanan rayuwan na gidan su itama tana dai hakkuri ne kawai.
Kwana biyu bayan taro ranan asabar da dare ina falon mamu zaune da littafi ina karatu don jerabawan da zamu fara.
Kawu ya shigo part din namu yana sallama a ladace na zamo saman kujeran ina gaida shi ya amsa ya samu wuri ya zauna.
Mamu dake zaune kasa ta gaida shi da dawowa ya amsa ya dago kai ya dan kalle ni kamar mai nazarina yace.
Fatima kin ramay haka da yawa ko har yanzu zazzabin ne a jikin ki kuma ko damuwa dai kika sawa kanki haka ?
A ladabce nace a, a kawu naji sauki jerabawa dai zamu fara nake karatu.
Murmushi yayi yace shine kike matsawa kanki haka akan jerabawa ai nasa an saka sunayen ku cikin masu fita bana .
Na dago na dan kalle shi sai kuma na sada kaina kasa a hankali murna zanyi ko bakin cikin hakan ?
Mamu ne tace zata iya kuwa naga karatun nasu yanzu sai a hankali yace sai da nasa akai min bincike a kanta sosai zata iya insha Allahu.
Ya juya gurin mamu yace ina ganin idan akai haka zata tafi da kwalinta can kinga da taje sai kawai ta fada jami,a baki daya dama kin san tace likita zata zama ko kin fasa ne fatima yana kallon fuskana.
Ban san lokacin danace ban fasa ba kawu ina nan da kudirina har yanzu sai kuma naji kunya ya kamani daga baya na noke kai.
Ai fa ka tabo mata inda ke mata kaikayi yau da zancen zama likita sai dai itama gata da tsoron allura nagani sosai amma tana sha,awan tayiwa mutane ita.
Mikewa nayi zan fice kawu yace dawo ki zauna abinki nace zan je in kwanta ne kawu na fice tare dayiwa mamu saida safe.
Cike da farin ciki na shiga gurin Amma da dan guduna na rugumay ta na kama hannunta ina fadin Amma kawu yace bana zan fita school sai in shiga jami,a.
Tayi murmyshi tace aure yazo ke nan kusa tunda har zai katse maki karatun ki yanzu.
Da sauri na girgiza kai nace a, a Amma yace karatuna zan dora sai kuma nayi shiru tuna yadda yai maganan.
Dan jimm nayi sai na mike tsaye tace aure sha kan yaro sai gida umaru sanda babuga yarinya a can zaki digree ke nan ko ?
Fuskana bata na koma saman kujera na zauna na shiga tunane can kuma na mike na shiga ciki don in kwanta ita kuma amma tafi kwanciya a falo tana nafilfilin ta ba dare wanda yanzu zama da ita yasa ina koyo.
Can kusan barci ya fara daukana cikin tunane na naji muryan kawu gurin Amma suna hira tana fadin tana ciki nasan ta kwantane.
Yanzu tazo min da murna zaka katse mata karatu don nace aure yazo tayi fushi ta shige dakin.
Ai hakan yayi daidai don a wuce wurin kowa ya shiga hankalin shi zaifi fitina jummai yayi yawa haka kawai ki tozarta yarinya a bainan jamma,a don wata manufa taki kawai na banza.
Hajiya kin hana in mata magana ne danayi mata tsiya wanan karon haba a bainan jamma,a haka ki muzanta yarinya kankanuwa kamar fatima ?
Zubur nayi na mike daga inda nake kwance ina sauraren su naji Amma tace yanzu ai tsuntsun dayaja ruwa shi ruwa ka doka don dai ta kara kawo nesa kusa ne ai.
Toshe bakina nayi don kukan da yazo min a lokacin har kawu ya fita ina jin su suna magana ne duk a kaina da matsalan gidan shi.
Ranan dai barci rabi da rabi nayi shi da asuba koda na idar da sallah na jima ina rokon Allah yasa a fasa wanan auren ga baki daya.
Ya kuma kareni daga ko wani sheri duniya da lahira ga baki daya na dade a dakin kwance don naji ban bukatan fitowa saboda gani nake Amma tana cikin masu zuga kawu akan yin auren namu.
Har kusan goma ina kwance kuma ba barci nakeyi ba Amma ta shigo tana fadin yau ko barcin lafiya kike yar nan ?
A sanyaye na dago kaina na kalle ta da idanuwana da sukai luf luf dasu nace ba barci nakeyi ba ai.
Kallona tayi fuskanta ba yabo ba fallasa ta zauna bakin gadon da kyar tace banyi tsamanin kina da taurin kai irin hakaba yar nan ?
Ina maganan nan kunyi shi da kawu ki kin amince yanzu kuma zaki shiga wanan halin haka ki dami zuciyar ki.
Maimakon in bata amsa sai na barke da kuka ina fadin Amma kin dai ji abinda hjyn su take min wullakanci har a bainar jama, a.
Mikewa tayi ta fita daga dakin zuwa falon ta ba adadeba kamar daga sama naga mamu a kaina lokacin na kifa ciki ina kuka ban san shigowan ta ba dakin.
Jin kamshin turaren ta yasa na dago kai na na kallo bayana ta tsaye ta kura min ido tana min kallo tuhuma.
Tace sayadi nace na,am murya a dakushe .
Bata kara cewa komai ba sai tayi shiru kamar mai tunanen wani abu sau can tace ashe ba an gama maganan nan dake ba wai ?
Wani irin tsoro ne ya lullubeni na mike zaune tukun na dukar da kaina kasa ga barin kallon ta.
Karo na biyu ta koma kirana tace kina jina ai ina magana yau dai ayita ta kare kada ki boye mi komai na yarda in kashe nawa auren da in jefaki cikin damuwa ke.
Wani irin kaduwa naji dajin furcin ta da sauri nace mamu ni may nace yanzu kuma kan maganan ?
Tace gashi tun jiya kin tada hankalin ki dana tsohuwar nan dake kokari dake har ta fara yanke shawaran fadawa kawun ki a raba wanan auren da yake son hadawa tunda hankalin ki bai kwanta ba.
Nace a marairaice wallahi mamu ni bancewa Amma komai bai tunda dai nayi sallah ne na koma barci kawai.
Murmushi tayi tace ba gaskiya bane ko kina tunanen gwaggo zatai maki karya akan abinda bakiyi bane.
Da sauri na girgiza kaina nace na bari mamu ni ba kuka nake ba gani dai nayi kamar ba za a barni naci gaba da karatuna bane shine damuwa na ayanzu.
Wa yace ba zakici gaba da karatun ki ba indin abinda kikaji ya fadi ne jiya ai hakan yana nufin taimakon ki yayi da hakan.
Nan dai ta nuna min bacin ranta tare kuma da dan min nasiha na share hawayena karshe nayi wanka na fice zuwa part din mu don har lokacin ina fushi da Amma.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button