NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:02 – ????????????: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM YA ALLAHU YA KAIYUMMU, , , ,

Ranan lahadi da yammaci kawu suna zaune da mamu a falon shi tana hada mashi abincin sa da idan yadawo yake ci sai kuma dare idan zai kwanta yasha yayan itacen da akullun baya katsewa gun matan shi don sun san shine abincin shi.
Umar da merry ne suka shigo gidan tun a waje ya san daddy su na gida don motan daddy daya gani a waje.
Don haka kai tsaye part din daddy ya nufa da matar nasa dake cikin atamafa buje da riga sai dai kanta babu dan kwali ko hula balle hijjab sai dan kwalin kayan ta dan dora a saman kafadan ta daga gefe.
Daga kofan falon ya tsaya yana sallama aka amsa mashi kawu da ya sheda muryan dn nasa tunkan su shigo ya kalli kofan yana kokarin kawar da kanshi gefe daya.
Yana gaba tana bin shi a baya suks shigo falon mamu dake gefe zaune tana ganin tare da merry suke ta dan sake murmushi a fuskanta tana tashi a inda take zaune kusa da kawu din tana fadin.
A cikin murna yau inlaw dina ce haka ban sheda ta ba kin fito yar African ki tsab wallahi suka dara gaba dayan su banda kawu daya kara tsuke fuskanshi a lokacin.
Ta kamo hannun ta tana dan rada mata tayi yadda taga mijin ta yayiwa mahaifin nasa ta amsa da thank you ma.
Cike da fargaban abinda zai biyo bayan shigowan nasu umar yake, don bai san irin karban da daddy zai masu ba a lokacin .
Sai dai samun mamu dayayi a gurin yasa ya danji sanyi a rashi don yasan komai zai faru kasancewar mamu gurin abin zai zo mai da sauki.
Ya karaso har inda kawu yake zaune ya zube bisa gwiwoyin shi tare da dukar da kanshi yace daddy barka da wuni an dawo lafiya ya kasuwa ?
Merry da takai kasa da kyat don bujen jikin ta da nauyin ciki tace good afternoon dad.
Umar da kirjin sai bugawa yake a lokacin don sauraron amsa kawu din zuwa gare su.
Kawu ya dan dago kai yana kallon umar din yace cikin dakiya Alhamdullahi umaru kasuwa ma masha Allahu.
Mamu dake gefe ke fadin marry ta zauna da kyau don taji dadin zama mana sai tace a a hakan ma yayi tana son daddy bless on her.
Lokacin kawu ya dago ya dan kalle ta yace thank you iam fine fuskan ahi ba yabo ba fallasa gare ta.
Dan shiru ya biyo baya falon kafin ya juya wurin mamu ya ce a shiga da ita wai kunu take son sha yanzu.
Mamu dai tace to bari aje a dama mata yanzu Allah sarki abu ga mai ciki ita yanzu kunun kawai ya biyo mata a rai ?
Dan juyawa yayi gurin ta ya danyi magana da ita ta mike ta bi bayan mamu zuwa part din suka barshi nan tare da mahaifin nasu a falon.
Shiru ne ya dan kara wanzuwa a falon sai karan na,uran dake aiki a falon lokacin umar ya rasa ta inda zai fara bayani wa mahaifin nasa don yana tsoron ya sake wani laifi a gurin shi.
Kawu ya kula umar magana yake son yi dashi lokacin sai dai da alama yana jin nautin fadin maganan da yazo mai dashi ne.
Kawu ya dan kai kishin gide yana fadin umar may ke tafe da kaine don da alama wani magana ya kawo ku gare ni yanzu.
Umar din yayi murmushin karfin hali yana gyara nade kafan shi yace eh daddy sai dai ba wani magana bane ina dai son in kara baka hakkuri bisa ga laifin dana aikata maka don Allah ka yafe min.
Kai kawu ya girgiza yace yaro ke nan umar idan banyi hakkuri ba kashe ka zanyi aini na hakkuri muddin dai kabi sharadin dana kindaya maka akai ba tare da kuntatawa marainiyar Allah da na zaba maka ba ni ya wuce a gareni ai.
Umar ya dan sosa keyan shi yace in sha Allahu daddy zaka samay ni da maka biyayya kamar yadda Allah yace a cikin natsuwa yai maganan shi.
Kawu yace daya fima alheri umar yanzu ina dadin wani koda dan uwana yau yazo gidan nan ace wai wanan arniyar ce uwar yayan ka.
Ka kwatanta a kanka yanzu zakaji dadin hakan a rayuwan ka wace irin uwa ka nemawa zurin,an ka da zasuzo duniya nan gaba ?
Umar yaya kake son mu,amulan mu da iyalin ka ya kasance a gidan nan nan gaba ?
Umar a cikin yayana kaf kai nake sa ran rike min zuriata koda bayana ne don hankalina gare ka yafi karkata da hakan sai dai kash ashe ban yi tunane mai zurfi ba da nake wanan shawaran a raina.
Maganar kawu ya saka hankalin umar a wani hali sosai a lokacin don shi sam baiyi tunanen wanan ba a gaba shidai ya biya bukatan kanshi kawai don jin dadin sa.
Sai yanzu da mahaifin nasa ke fadakar dashi yake tuna hakan hankalin shi idan yayi dubu ya tashi da zancen kawuna da yake mai yanzu.
Saboda hakan na yanke shawara akan ku akan abinda ku kuka kasa hangowa nan gaba uwar ku kuma tana goya maku baya kan shirmay da kuke yi din.
Lalai kawu yayi ya tuno mashi abinda shi ya kasa tunowa gaba ake duba ba kusa ba don maganan kawu gaskiyane umar yace a ranshi.
Kawu ya kare da fadin saboda haka ko bayana idan kuka saba alkawarina ban yafe maku ba umar.
Da sauri yace in Allah ya yarda daddy zaka samay ni mai biyayya a gare ka don Allah daddy ka yafe min nayi kuskuren da ba zan sake irin sa ba a rayuwana.
Dan shiru ya kara biyo a falon sai kawu yace akwai wani abin ne bayan wanan don ni kaji magana ta na dade da yafe maka don duk mairai bai wuce kaddaran shi sai dai taka kaddaran tazo muna a kyamace don haka nake maka fatan shirguwan wanan yarinyar nan gaba.
Yace insha Allahu daddy ina kokari a kai yace kamatsa da hakan don yana da kyau gaba akewa gudu ai.
Nagane nufin ka yanzu daddy a gare mu in sha Allahu haka ba zai sake faruwa ba gareni.
Ya gyara zama tare da fadin daddy dama tun dana dawo bamu samu zama da kai munyi magana sosai ba don ina son fadama irin ci gaban dana samu a gun aikina a can.
Ina jinka kawu yace tare da fadin uwarku tana kokarin nisanta ku dani kan wani dalili nata na banza ta yaya zan iya sanin halin da kuke ciki a yanzu.
Yace No daddy ba hakana bane zama ne ban samu yi ba amma ta yaya mama zatace ta nisanta mu da kai.
A can bayan kare karatu mataki na biyu na samu aiki da wani company daga nan na wuce karo ilimi ina aikin kuma da na kamala sai gwaunatin kasan ta dauke ni aiki a ma,aikatansu nacan.
Ganin irin riban da hakan ke dashi yasa na yarda zanyi aiki dasu na dan wani lokaci idan adadin danake ganin
Kawu ya girgiza kai cike da gamsuwa da bayanin dan nashi yace yaro ke nan sai dai ina son ka sani rayuwan mu yau ba a hannun mu yake ba umaru.
Don ko yayane kasanka tafi bukatanka a yanzu don haka ban lamunce ma zaman ka acan ba dindindin kaji na fada maka.
Ya amsa da insha Allahu daddy don nima ba zanso yarana su taso da wani akidan da baishafi al,adana ba a yanzu.
Kayi tunane mai kyau Allah yayi maka albarka yasa a gama da duniya lafiya yace Amin daddy na gode.
Kawu yace zanso ka bani dama in gana da ita matar taka idan ba damuwa don ta fahinci irin gidan da ta shigo.
Cikin dauriya da faduwan gaba yace ba matsala ai daddy sai dai kuma ka gafarce ni don nayi wani karanbanin ba ban shawarce kuba daddy don nasai gida tun ina can a nan unguwar aka rusheshi akai min tsarin da nake so gare shi.
Kawu ya jima shiru ba tare da yai magana ba yana tunanen halin rayuwan dan nasa na zurfin ciki.
Yaya har akai ya sai gida akai masa gina duk basu da labarin hakan sai yanzu yake fada mai ga wanan bakin aure da yayi ace duk yara matan musulmai dake cikin kasan nan da garin kano basuyi mai ba ya jajibo masu kafira a matsayin suruka don yawan zurinfin cikin su bai sanar dasu ba sai da abu yayi nisa haka harda rabo.
Sai dai babu yadda zai da dan nasa tunda ya fahinci halin sane hakan ba wai yin kasa bane illar nisan ta su da kowa da mahaifiyar su tayi tun farko duk yajawo hakan.
Allah ya kyauta yasa albarka ka more kai da iyalin ka lafiya da yawancin rai.
Wani irin dadi ya ziyarci zuciyar umar da wanan adduan da mahaifin shi ke masa a yammacin nnan haka ya bashi daman ci gaba da fadin akwai wasu dana saya a lagos da Abuja sai kanfanin da muke son hadawa ni da wani abokin aikina bayerabe a can kudu.
Umar duk wanan lissafin da kake min a ina ka samu kudin yin su cikin wanan dan shekarun da kayi kana aikin ka ?
Dan murmushi umar yayi tare da fadin daddy ka yarda dani ba abinda kake nufi din nan bane don idan ka duba can kasan ba irin nan bane da ake tauye ma,aikaci shiyasa mutanen mu yanzu basu son yin aiki a kasan nan.
Don albashin can ya nunka na nan nikin baninkin idan kuma kayi duba gani international referner ne na hadin kasa da kasan turai zaka fahinci ta yadda kudi suke zo min a yanzu.
Shiru kawu yayi na dan wani lokaci yana nazarin maganan dan nasa kafin yace Allah ya kyauta a dai riki gaskiya ga duk abinda akasa a gaba.
Ya dora da fadin a dinga kyautatawa yan uwa da mabukata dake a kwai kasa damu don muna da yan uwa a birni da kauye wa yanda ke bukatan kulawan mu.
In Allah ya yarda daddy za a kula zan yi kokarin zagawa a cikin dangi mu kai ziyara kawu yace Allah ya bada iko ya amsa cikin jin dadi da Amin.
Kawu yace kaje kazo min da matar taka kafin lokacin sallah ya gaba to in fita ya amsa da to daddy yana yunkurawa ya tashi.
Ba karamin dadi umar yaji ba na fahintar juna da sukayi da mahaufin wanda ya samay shi a cikin saukin kai a yadda bai zata ba.
A falon mamu ya samay mu zaune ana dariyan merry dake shan kunu tana santin shi don hadin da mamu tayiwa garin kunnun tsamiyan kafin ta dama dama yana aje a ckin fridge din ta don ba kullun ake damawa ba.
Muna ganin shigowan shi kowan mu ya natsu muna gaida shi da shigowa gidan ya dan kalli mamu yana fadin daddy yana son su gana da ita.
Tace masha Allahu hakkuri bai bar komai ba umar dama nasan in anbi Alh zai sauko a sannu a cikin muryan shi kamar mai rowa yace hakan ne nagode maimuna.
Wani kallo na watsa mai da mamakin yadda yake kiran sunan mahaifiyata haka gatsau sai naji ya kara zube min a idona.
Ita ko mamu hakan ko a jikin ta bata damu da yadda nasha toka ba na bata raina sosai sai ji nayi tace sayadi dauko mata dan karamin hijab din nan naki na zaman gida ta saka kada taje masa haka nasan shike kara hadasu da yaya.
Ba tare dana kallo inda suke ba nace yayifa dauda mamu tace daya ne halan dan Allah shiga ki dauko mata kinji ta fada a cikin zafin rai.
Haka yasa na mike na shiga na dauko mata bakin dan just to cover na fito dashi na mika mata tabi da kallo tana dan dariya tare da tambayan yaya zata saka ?
Ya juyo inda nake zaune yana fadin taimaka mata ta saka mu tafi dole na taso na gyara mata ta dinga wani rawa ba kunya a gaba shi tana wani juyawa shiko gogan yana lushe ido yana binta da kallo cikin sha,awa.
Ya rike mata hannu suka jera a tare suka fita daga falon suna dan magana yana kallonta yana murmushi.
Suna shiga falon ta kara gaida daddy a cikin gurbatacen hausan data koya a lokacin kawu dai ya karba mata.
Bayan sun natsu kawu yace may sunan ta yana kallin dan nasa yake tambaya yace merry da sauri.
Kawu ce merry take to mu nan zamu kirata da maryam ya fada mata cikin harshen turanci ta danyi dariya tace that’s my name.
Kawu yace maryam ina fatan kin san wanda kika aura ma,ana addinin sa da yaren sa da al,adun mu ?
Da sauri ta amsa da yes uncle yace good sai dan zan kara fada maki idan ma shi bai fada maki da kyau ba ki sani mu ga addinin mu mata basu shiga irin wanda kika shigo gidan nan dashi.
Kai ta sunkuyar kasa don nauyin maganan kawu din gare ta don ko shi umar din yayi mata korafin hakan.
Sai na biyu kin dai san umar musulmine tun kan ki aure shi kika yarda kika aure shi a hakan ta gyada kanta alaman ta sani.
Kawu yace good masha Allah yace adfinin mu bai hana mu aure ku ba matukar ba zaku sauya mijin da kuka aura i zuwa naku addinin ba.
Sai dai mu Allah ya haramta ma yayan mu ta auren yan naku addinin ga baki daya addinin bai yarda da hakan ba.
Da sauri ta dago kai tana kallon Umar din da kanshi yake sade yana sauraren maganan mahaifin nasa.
Kawu yace don haka ne nake horon ki da ki bar min yarona yayi nasa addinin tunda mu bamu kyamaci addinin ki ba.
Sai dai idan kikai kokarin yin hakan ki sani ni mahaifin shi ne zan iya raba auren ku a duk lokacin da na fahinci haka a gare ki.
Tace cikin sauri i will never try that uncle and beside Omar is riligious somebody he will never accept that.
Kawu yace again kin ga family din mu babba ne ga al,adan mu shi babba a gida kamar uba yake a gun kowa na wanan family din kada naji wani yaje gurin shi an samu matsala dake.
Ita kan may yai zafi haka wanan tsohon yake ta kidanya mata sharuda haka dama haka auren musulmi yake ko nasu al,adan ne haka merry ki rayawa a ranta.
Ita dai burin ta shine suyi accepting din ta as a daughter inlaw din su idan ma sun barta a hakan ya wadatar da ita may ya shafe ta da wani al,adun su kuma su da suke can uwan duniya mai nisa in ba ma shi da ya matsa zaizo gida ba yaushe zasu gansu ma.
Kawu yace kin san addinin mu ya bamu daman auren mace da daya don duk lokacin da umar yaso kara aure a cikin kabilan shi yana da daman yin hakan.
Da sauri ta daga ta kalli tsohon inda yake zaune ta sake juyowa ta kalli umar din kafin ta sada kai ganin umar ya girgiza mata kai alaman ta yarda kawai.
Kawu yace sai na karshe dole ne dana ya ding zuwa nan dubamu duk bayan wasu watanni akala sau uku a cikin shekara ko biyu idan kuma zamuyi sallah ya kasance yana gida tare damu a matsayin na babban da a gidan nan .
Idan wanan yayi maki a tsarina baki da matsala komai damu muna maku fatan alheri da samun zuri,a masu albarka.
A sanyayr merry ta dago kai tana fadin taji tagode kwarai yace ba matsala cikin daga masu hannu yana kokarin mikewa tsaye don zuwa maslaci don sallatan magariba.
A daidai lokacin kuma hjy jummai tana shiyan ta tana bala,i jin cewa su umar na gidan tun dazun shiyan hjy maimuna ta dinga surfa ji dali da sauran yaranta.
Tana fadin ita bata yarda da wanan tsarin ba watau maimuna mamircin data kulla ke nan na janye mata suruka a wurinta don ta jata a jiki saboda taga wurin ci ko ?
Tana cikin wanan masifan ne Umar din ya shigo da merry don su gaisa fuskanta babu annuri take karba masu gaisuwan su.
Tare da tambayan shi ance tun dazun kake gidan nan kana wurin maimun da wanan yarinyar makitcin da maimuna zatayi min ke nan tanan take ganin zata bullo min taci galaba na.
Ido merry ta tsura mata duk da bata jin abinda ake fadi tana iya gano fada matar keyi da Umar din sai dai bata sa ko a kan may bane ?
Umar daya tsaya sauraren maganan mahaifiyat tashi jin tayi shiru yace haba mama tace haba din may babawo yanzu har kai kokarin hada wani alaka kakeyi da matar nan.
Nifa daga ita har kakar taku da kake wani soye mata ban yarda dasu ba dukkan su makasa nane idan sun samu wuri don haka ban yarda da hakan idan kunzo gidan nan ku shigo nan kai tsaye daga yau.
Yace mama ba haka na bane tun dazun a gurin Alh muke muna magana dashi fa har yaushe muka zauna a gurin maimuna din.
Tace Alh may kuma ya kiraku yake fada maku shi bai son a zauna lafiya ina ganin sai na fito masa ta hanyar bayan gida a zauna lafiya don kawai an cusa mai ra,ayi a kanku na kiyayya shine har yanzu abu yakici yaki karewa a tsakanin ku.
Innalillahi mama nine fa nakai merry din su gaisa saboda ta damay ni tana son su gaisa da shi na kaita yau dana yana gida sai muka tsaya ya danyi muna nasiha.
Daga nan nake fada mai irin plan din dana shiryo a can kafin in dawo and kuma daddy yayi muna magana ta fahinta sosai wallahi.
Sai lokaci ta dan sauko tana fadin oho ai dai na dauka wani abi ne kuma yake sharada maku don shi bai gajiya da tsincen mata.
Haba mama tun dazun kina ta fada haka a gaban surukan ki mun fada maki ba komai bane kinki ki gane ai shi brother yana da wayau shi .
Salma wallahi ki fita a idona tun ban saba maki rai ba yanzun nan a gutin nan abinda nasani zaki tsaya kina mussamin akan shi.
Hannu ya dagawa salma din tare da fadin is ok mama don Allah ba haka zancen yake ba zan tafi sallah idan na dawo zamu wuce a nan zan barta.
Ya juya yana fadawa merry shi zai tafi masallaci ta zauna a part din mum din shi har ya dawo mikewa merry tayi tana fadin No ba zan tsaya a nan ba nafi jin dadin wacan part din don muna hira dasu a can sosai.
Dan tsayawa yayi yana rarashin ta fafir merry tace ba zata tsaya a nan ba don ta karanci hjy dan zuwan ta matar bata da marmari sam tana da dan fada da jin kai.
Daidai lokacin har ta fara tafiya ta nufi hanyar fita daga falon sai hjy tace ba masalaci kace zaka ba ita kuma ina zata ?
Yace a cin cool voice tace gun maimuna zata tafi tafi sabawa da ita can ai kaga matsalan tun ba,aje ko ina ba abinda nake fadi ke nan ya fara fitowa.
Mata da kinibibin tsiya harda wanan da zuwan ta ta sace mata zuciyar ta wai a haka ake son i hada zuria da ita ina wallahi ba zai yuyu ba sam.
Merry ka har ta kai kofan mamu can taga fitowan shi hannu kawai suka dagawa junan su ya fice daga gidan zuwa wurin sallah.
Haka yaje sallah ya dawo ya samay su a falo da mamu suna dan hira hefi jefi ba wani hira bane sai labarin irin al,adan hausawa da sukeyi.
Haka ya shigo ya samay tayi da daya a falon ta sake jiki ga plete din ferfusun kayan ciki a gaban ta tana sha a hankali.
Yaji dadin hakan da mamu ke nunawa matar tasa wanda har kasan zuciyar shi ya yaba da hakan sosai don baiga wani kissa da mahaifiyar shi ke fadin mamu tanayi ba shi kam.
Don mamu sai kokarin farantawa merry take don kawai ta ingata darajan shi a gare ta wanda ko na munafunci tayi mai dai ya gode da hakan.
Yace maimuna zamu tafi dare ya soma da sauri mamu tace dashi km kaci abinci ne Umar da fa abunci nan na zuba maka kai da matarka.
Yace banda lokacin cin abincin nan yanzu maimuna ta taso mu tafi kawai in kaita ta huta akwai maganin da zata sha karfe tara.
And ina son mu shiga mu duba Amma kuma lokaci ya kure sai dai idan mun sake dawowa kuma.
Mamu tace sai ku tafi da abincin don daku na girka dama ta mike tana kokarin zuwa kitchen don dauko basket ta saka masu a ciki.
Ina daki ina jin duk yadda sukayi a tsakanin su don tunda na shiga sallah da gangan naki fitowa falon do takaicin mijin da mata saboda tabaran su a gaban kowa babu kunya a tare dasu ko kadan.
Mamu ta fito tana kwala min kira na fito na kai masu abincin bakin motar su yace No ki barta zan dauka dare yayi yanzu ba kowa a wajen gidan nan.
Sun fito bayan sun mata sallama ne suka hade da hjy maryam data dawo daga unguwa tace a, a umar ashe ku shigo gidan namu ?
Yace eh yanzu muke shirin komawa bata damu da kallon ta da yakeyi ba gulma ya cita tana karewa merry kallon kurlla tsab tana kada kai ya wuce merry da bata san tana yi ba tabi bayan shi zuwa inda ya aje motar shi a waje.
Da gulma a bakin ta fam ta nufi part din ta cike da tsegumin merry wa yayan ta lokacin nan suka zauna suna dariyan shakiyanci wa halitan merry din suna dariya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button