NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
16/11/2021, 22:37 – ????????????: ALLAH SARKI YAU YAZO YA TAFI KE NAN UBANGIJI YASA MUN AIKATA ALHERI A CIKIN WANAN RANAN ALLAH YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YA GAFARTA MUNA KURA KUREN MU GA BAKI DAYA AMIN.

Mai karatu zaki dauka zancen yaran hjy Jummai zai kwantar mata da hankali ne don da farko har ta dauki maganan yaran da muhinmanci a ranta.
Ta sakar da maganan duk da ranta yana matukar sosowa da zancen don ya tsaya mata a rai tana ganin hakan komawa baya ne a gurin ta.
Shigowan hjy maryam part din yasa maganan yarta Salma yazo mata a rai dama tayi tsamanin hakan da farko kallon ta tayi ta watsar sai da hjy maryam din da yake makirace ta in ma bakinta tace.
Giwan gida kada ki dauki wanan maganan da zafi haka don ni tun ranan da aka kitsa hakan na sanda zancen sai dai banyi magana bane sai na gano abinda ake kitsawa din.
Don ina ranan da kika fito gaida tsohuwar nan kina fada kan suna labewa da Alh suna hira a can ba ranan girkin ta ba.
Tun wanan ranan aka kulla hakan a gidan sun riga da sun kulla abinsu dama aiwatar wa ne da tsohuwar taga baiyi ba yasa ta fadi a fili.
Dama ni a tayadda na samay su ranan nasan akwai wani babban al,amarin da zai faru a gidan nan don samun su nayi suna raha suna zaune kamar wasu kawayen junna.
Zancen tafiyana kuma da nayi wa Alh sai cewa yayi sai dai idan da maimuna zanyi tafiyan don itama tana da abinyi a bauchin.
Nuna masa rashin yardana da hakan da banyi ba shine mfarin rashin zuwana har yau da banyi ba tunds naki yarda inyi tafiya da yar gwal din gidan shi.
Jin hakan ya sasauta zuciyar hjy jummai tace ke kuwa gaki wace bata san abinda takeyi ba mana ba dole ki tafiya da ita ba tunda kowa na tsoronta kamar yadda ya take juya shi.
Ita wanan da taki zaman aure ta kaso tazo ta zaunawa mutand gida har da yara biyu dama abinda suke so ke nan su samu dukiya suyi yadda suke so dashi ta samu yanzu ji abinda ta fada a wurin.
Ni wallahi na dai bari an kai min nawa ne don kada ace mutum ya karya dokan maigida a sashi ga baki.
Ji munafuka bayan ta gama dariyan mugunta a daki yazo tazo nan tana dadin baki don kishiyar tata ta kara tunzura.
Nan ko mai zafin kishi ta hau ta fara fada tare da fadin dama nasan da manufa akai mi hakan don kawai aga bayana a gidan nan .
Anzo a taru a wawashe dukiyar banza a watse daga baya a koma ana fadin bai da komai yanzun don haka suke so wallahi zanyi maganin kowa a gidan nan har hadiyen dake zaman kama mata su ga yan uwa ko ?
Ni da naga tasbaha a gurin zumunta banji tsoro ba shida kafin ka gama da dan uwa daya ya biyo hannun ka.
Sun dauki lokaci suna zancr daya a dakin tana kara iza ta akan itama zata dauki mataki kan abinda ake masu a gidan cewar hjy maryam din.

Ya kasance yau ranan girkin hjy jummai ce a ranan ta kudirci yin magana da maigidan ba wani abin kirki tayi ba don kamar kullun yan aikin gidan tasa suka shirya mai abinci kamar na kullun.

Sai da ta gama abinda take ta tun kari part din maigidan da harta samu yana shirin kwanciya a lokacin ta shigo da sallaman ta dakin.
Ya dago tare da amsa mata sallaman a takaice don yasan har yanzun fushi take da shi kan abinda ya faru dan kwana biyu a gidan don babu walwala a tare da ita tun lokacin.
Don hakane shima bai yarda ya bata kafan da zafa kawo mai zancen ba don Ahmed ya fada mai duk yadda ya faru a gidan ranan.
Muryan tane bayan ta samu wuri ta zauna tace Alh magana nazo muyi ni dakai ba tare da ya daina abinda yakeyi din ba yace umhumm ina sauraren ki ai.
Gaskiya Alh bangane abinda kake nufi damu a gidan nan ba kokarin zama shima yake tare da fadin kamar ya dake da wa kuma ?
Tace dani da kowa na gidan nan da wanan maganar ta shafa kana tsamanin ban san abinda kukeyi ba a gidan ko ake shiryawa don dai kawai aga an kuntata ma rayuwan mu.
Wai kina fadin ana kuntata maki dake dawa kifito fili ki yi maganan da zakiyi kin tsaya kwana kwana.
Hakan ma zakace tunda ka na kokarin fifita wata akan mu yau ka fada min da abinda maimuna tafi mu dashi a gidan nan da tun shigowan ta kake kokarin muzanta muna haka akanta
Kai Alh ya girgiza lokacin da tayi wanan maganan tare da fadin nikan Jummai da zaki bi shawarata da sai ince kifita harkan yarinyar maimuna tun tana ganin ki da daraja a gidan nan.
Wallahi Alh yau dai ayita ta kare don sai ka fada muna abinda ta fimu dashi don ban gane may kake nufi ba da bin ra,ayinta
Mtss yaja tsakin takaici yace ke a tunanen ki haka ake daukan girma idan Allah yaba mutum don zaki zubawa da kanki da kima a idon kowa ne.
Kefa babbace ba sai na tsaya maki bayanin daukan girna a cikin lumana akeyin sa .
Indan fa kin matsa a kanta komai na iya faruwa na iya faruwa tazo bata girmamaki a cikin gidan nan wanda ni kaina ba zanso hakan ya faru ba a gidan nan kodon yarana dake kallon ku.
Don kina dai gani tun bata iya baki amsa har gashi yanzu ta fara budan baki tana magana a gaban kowa ba komai bane fa halin yau da gobe ne ya fara isarta.
Ita may yasa kuun bata kawo zancen kunyi mata abu koda kuwa din kunyi sai dai kune a kullun tayi maku wani abin mussanman ma ke jummai why ba zaki tayani gyara gidan nan ba kamar yadda naso sai kokarin bata min gida.
Da kike maganan ina kuntata maku ai ita maryam nan tazo tayi min godiya kan abinda hjy ta bada umurni ayi nakumayi sai ke ne da baki gudun halakana zaki zo ki sakani a gaba kina wanan babatu haka ina ilimin ki da hankalin ki yaje ne wai.
Abin nan fa sauke nauyi ne a gare mu duka akayi idan kin gane ko da basu magana amma kema kin san ana cuta masu dai a gidan nan ta wani famni ko ?
Ya kamata ki dinga nazari idan kinga na aiwatar da abu ba wai ki dauka nayi hakan don ra,ayin wata bace a gidan .
Tunda ya fara magana har ya ambaci sunan hajiya maryam jikin ta yayi sanyi akan maganan nasa da yaga yanayin nadama a gurin ta yaci gaba da fadin.
Ni da zaki bi ta nawa ki kwantar da hankalin ki don bada ke ya kamata kullun a rika ji bakin a gidan nan da maimuna ba tunda dai kece babba.
Shi kuma auren maimuna da nayi ba haramun bane yinsa sai karin zumunci idan kin matsa na saki maimuna ma wata zan kawo gidan nan tunda yanzu na gane auren mace fiye da biyu kuma.
Wani kallo ta watsa mai daya fadi hakan tare da fadin watau ma ba zancen zama da mace daya kakeyi ba ke nan ?
Kwarai kuwa ban maki wanan alkawarin ai tun farko kinga idan kun fitar da maimuna wace zan kwaso kila tafi maimuna fitsara da kuke fadin tana maku ko yaushe tazo ta gyara min zaman ku a gidan nan tunda ita maimunan tana bin ku a hankali bai maku dadi ba.
Mu maza ba ai muna haka ku bar mu da abinda muka gani muna so on haka gara maimun kin santa tun farko kin san halinta .
Gaba daya jikin ta yai sanyi da jin maganan ta hankalinta yafi tashi dajin yace ko maimuna ta fita wata zai kwaso masu take natsuwa ya kamata har take fadin.
Ai sai mu zauna muci kan mu nidai dama raini ne ban son a gidan nan don haka sai a kiyayye don gaba.
Yace ba wanda zai rainaki a kidan nan muddin ina raye don haka ki barni nasan abinda nakeyi ranan hjy jummai da tunanen maganan shi ta kwana a ranta.

BAUCHIN YAKUBU, , , , , ,

A cikin garin misau gidan malam sale ba wani babban gida bane na azo a gani gidane irin ginan kwatas din nan da ake sayarwa na gwauni aima ma,aikata gwajon shi su saye.
Gidane na mata biyu sai falo a tsakiya da ban daki sai kitchen wanda kowa yake sharing a gidan
Yaran malam sale tsohon malamin asibiti ne a primary health care aiki ya kawo shi misau daga azare har ya zauna misau din saboda dadewan shi garin da kuma auren yar garin misau din da yayi.
Yaransa goma wanda mata biyun suka haifa mai sai dai yanzu wasun su sun girma do haka ba zaman gida sukeyi sosai ba.
Gidan malam sale gidane da mata ke iko a cikin shi hakan ya jawo lalacewan tarbiyar yaran gidan kamar yadda wasu dake gane masu suke hango hakan a gare su.
Don uwar yaro zata iya saka shi yin abu yaro ya kafe akan ba zaiyi wanan abin ba ko a hana shi yace sai yayi .
Hakan ya samo asali kan rashin zaman gidan da malam sale din bai faye yi ba din da zaran ya dawo daga gurin aiki zai wuce chemest di shi da yake dan sayar da magani a kasan uguwar su.
Malam sale wane ga marigayi Abubakar mijin hjy maimuna na farko da Allah yayiwa rasuwa shekaru biyar da ya wuce inda ta dawo kano da zama a lokacin ta bar yarta can a hannun kakanta mahaifiyar marigayi din.
Sai lalura ya kama tsohuwar zaman su yanzun ya dawo misau din gidan danta wa ga marigayin danta.
Kamar yadda kowa yasan mutan misau da karatun addini dana boko suna noma da kiyo kamar yadda yake al,adane hakan ga kasan hausa sai wani dan sana,an daba,a rasa ba.
Sai dai gidan malam sale abin yasha bambam don yaran gidan gasu da son hutu sun ki tsaya su dage ga karatun boko ko na addini wanda hakan yana cikin matsalan da hjy maimuna take hangowa yarta akan zaman gidan.
Wanan yasa da zaman su fatima yar gurin hjyn ta dawo nan karatun nata ya fara rawa aje yau gobe ba a zuwa har ma a debi lokaci ba a je ba.
Gashi ba wani kula a gidan zakaga yaro ya shigo da ledan idomie yana dafawa ya bad abincin gida bai ci ba duk da malam salen yana iya kokati shi gurin ganin ya kawo abinda za a sarafa aci a gidan wanda shine ya jawo mashi wanan bakin wahalan bayan yayi ritaya.
Ko dan makarantar da take zuwa sai da taimakon gwagon ta kanwar mahaifin ta Adda ta samu take zuwa makarantar jefi jefi don ba,a sata da zaman su ya dawo garin ba.
Da kyar yaran gidan suke kare secondary school di wanda dags nan sun kare karatu ke nan sai zaman bin gari da yawon buki.
Wanda duk wanan abubuwan yana cikin abinda ya tayar da hankalin hjy maimuna da zama ta gidan ba wanda ke kula lamatin wani kowa kansa ya sani a gidan daga manyar har kananan.
Dan abinda kakan ke samu take tallafawa rayuwan yar jikan nata dashi idan kuma bata dashi sai dai su hakkura ke nan.
Hakan baisa yarinyar ta dan canza ga tarbiyan da take dashi ba sai dai akwai inda take da dan rauni wanda zaman gidan yasa ta koyi rashin kunya sosai don hakan taga anayi a gidan itama ta koya ta iya.
Ga yawo bin makwata saboda gudun aiki da aike tula mata a gida don sun ganta da zafin nama aiki baya sha mata kai ko kadan
Kamar yadda kowa ya sani mutanen azare gauraye ne sai dai akwai fulani da yawa a cikkn su hakan zuri,an su fatima ma fulani usuline don har yanzun kakar tata bafa jin hausa a baki ta sosai sai ta hada da fulanci.
Itace komai na kakan tata da farkon zuwan su babu mai taimaka ma lalurar kaka sai da Adda tazo gidan tayiwa mata gidan yankar kauna kafin su fara dan taimakawa dattijuwar.
Yau ma zaune take a gaba kakar nata tana ci dan abincin da ka saka masu wanda wani lokaci dole kaka ke hakkura ta barwa jika nata tacinye sai dai tausayi kakar nata wani lokaci bai barin yarinyar taci abinci sai tace ai taci a gidan su kawar ta Rahama gidan da ke makwabtaka dasu inda duk yawon ta idan ka nemay ta ana zaka samay ta.
Dan kadan ta taba shinkafa da waken da take ci tace da kakar tata ta koshi don kakar ta samu itama ta taba bawai don ta koshi tace hakan ba.
Sai da yarinyar mai tausayi ta tabbatar da kakan ta koshi ta debo ruwa ta kawo mata ta wanke hannu ta kawar da kayan ta dawo ta dan zauna a dakin nasu wanda ke ta wajen gidan da aka gina aka kewaye da kwano ya shigo ta cikin gidan.
Ganin kaka nata ta dan kishingida yasa ta mikewa don tasa yanzun za a kwala mata kiran aike ko wani aiki na gidan wanda ya kamata ace yan matan gidan sunyi gasu zagada zagada dasu amma basu kawar da kara a gidan nasu.
Na fito ke nan daga dan dakin mu da aka ware muna a gidan ina sanda don kada wani a gidan ya ganni ya aike ni ko yace in mashi wani aikin.
Ta kai daidai kofan fita tajiyo muryan mama saude tana kiran ke ke ke Fatima ina ji hakan tuni ba baza da gudu na bar gidan ina jin tana fadin ai zaki dawo ko yaushe kika gama gantalin ki kika dawo wanke wanke yana nan yana jiran ki a gida nan.
Jin hakan ya falkar da kakan nata da bata san fitar yarinyar daga dakin su ba sai murya taji ana kwala mata kira daga waje kuma tasan bata dawo ba tunda taji kalamin saude din kan yarinyar.
Da kyar ta samu ta mke ta dan dogara kafan ta zuwa waje ta samun sauden a zaune tana wanki tana sauraron wankan yan wasan hausa tana bi.
Sai murya dattijuwar saude taji a kanta tana fadin haba saude yar nan ita kadaice a gidan nan ina ga yaranan birjit a gidan nan su ba yayan moriya bane sai wanan yar marainiyar Allah kwaya daya tilo a gidan nan da ba uba uwa kuma tayi mata nisa ita kadai ce ko yaushe tsaye a gidan nan.
Yarinya babu daman ta motsa kowa dai fatima fatima don Allah ku bar yar nan ta huta hakana mana, ko kwatanta a kan ku idan haka ya samay ku ko yayan ku.
Tsohuwar bata kai ga ci gaba da maganan ta ba tajiyo muryan Tj bayan ta daya daga cikin jikokin ta na gidan yana fadin dallah ji wanan tsohuwar.
Yomar idan ba a saka ta aiki ba wani moriya take dashi a gidan nan bayan dan aikin da takeyi mafarin ki lalata yarinya kawai.
Shiyasa ai yanzun bata tsoron kowa a gidan nan wata jikan nata da taji ana maganan ta fito daga daki tana daura dankwali a kanta zata fita yamma yayi zata ta zubar din da suka saba .
Take fadin kema wai manjo ina ruwanki kiyi fama da kanki mana kina wani fada kan wata fatima can kamar ita kadaine jikan ki a gidan nan.
Da anyi magana kice yeyeyeye, , , , wai yar marainiyar Allah ce ita kada a taba ta ubanta ya mutu waye waye da sauran su.
Ikon Allah yanzun ni kike kwakwayo yar nan komai abinku dai nice na haifi uban ku sai yaro farko yace yo ai shi kika haifa bamu ba sai kije ki ta haihuwar su can.
Badai zaji taba haihuwan mu ba mu tace wa ni Allah ya tsari gatari da saran dutse da in haifi irin ku ai gara in zauna ba haihu yafi mun jika ji shigan ka kamar ba dan musulmai ba ji kanwar ka a haka zata fita uwayen ku na ganin su.
Shine bakin cikin ki inji yarinyar da ke murza janbaki a bakinta ta gyaran fuskanta ko inzo in shaga mak ne dallah ban wuri gantalaliyar da bata san ciwon kanta ba .
Diba uwarki ne nan zaune take wankin kayanta da kanta baki san ki kama mata ba aini yarinyar nan Fatima tafi mun ke sau dubu wallahi a gidan nan.
Ke tafiwa ba muba inji namijin kai rufe mun baki mai sufar arnakun farko jika ji wanan shigan a haka kake bin gari kamar wullakantace.
Haba babba zagin yayi yawa hakana ai shigan zamanin nan ne haka ba wai ra,ayi bane Saude dakan ki kike fadan haka a gaban yaran nan.
May ye a ciki babba yanzun akan yar jikan ki da kike so kike wanan tada jijiyan wuyan haka yaron ya matsa kamar zai mangare yar tsohuwar.
Salati ta saka tana fadin yau naga yaron kawai Allah ya ban lafiya in bar gidan nan da kafana.
Aike ne dai da aiki fatima ba zatayi ba yau a gidan na soke wanan a gare ta caraf uwargidan malam sale ta fito daga dakin ta tana fadin.
Babba kibar wanan zancen don Allah kada yarinyar nan taji dadin kara finjiraiwa a gidan nan hinjira kan ai ga hinjirarun nan a gaban ku su da ba a iya aike ko nan da can.
Aikine daga yau idan fatima bata yi shi ba bazata kara cin ko loma a gidan nan kunji na fada maku.
Manjo dake kallon ta a ciki mamaki ta kasa magana sai cewa tayi Allah ka kawowa yar nan dauki a gidan nan ta huta ganin wanan warin a gidan wan ubanta.
Ta juya da kyar zuwa dakin ta na faman mita akan abinda akewa yarinyar a cikin gidan.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button