SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL
SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:13 – ????????????: Barci nake hankalin kwance don ina jin dadin barci a irin wanan lokacin na ba safiya ba ba rana ba don barci kan min dadi sosai balle yanzu da ga ciki a jikina.
A cikin barcin da nakeyi ne nake dan jin murya sama sama wanda hakan yasa har nakai ga bude idona a hankali.
Bubu kowa a dakin sai sultana dake barci a dakin saman gado a kwance kusa dani ta makale mun a jikina.
A hankali na cire yarinyar a jikina na yunkura na sauka daga gadon na nufi bandaki na kewaya .
Falo na fito mamune ta dauki abu a kitchen zata fita da sauri daga part din mamu meke faruwa na kuma na tambaye ganin yadda take a rude.
Kawun kine baida lafiya ya rikice muna lokaci guda ta bani amsa tana fita daga dakin.
Hankalina naji ya tashi lokaci guda da sauri na bi bayan mamu muka isa falin tare lokacin na sami har Amma tana falin itama.
Yana kwance sharkaf gani daga wurin yin lazimine laluran ya same shi koda mamu ta fita bai karkare fita hayacin shi ba zuwa ta dauko abu ne muka samu ya fita cikin hayacin shi ga baki daya.
Duk yan gidan suna rude sai kuka suke sun rikice a lokaci daya.
Kwatsawa nayi tsakanin su hjy da hjy maryam ina fadin a bani cibi da sauri kada ya datse harshen shi lokacin.
Da sauri aka miko min cibin dake saman table na daga kanshi ina kokarin samun sa,an cibin ya tsaya a bakin shi.
Da dai an kira likita yazo hjy tace ban kula taba sai aikina nakeyi da sauri na dago ina fadin zan samu dan igiya ko yagwai karami haka ?
Wanan ba mafita bane kada aje a jawo mashi matsalan da bashi ba kuma ta kara fadi.
Ba dai wanda ya kula ta a lokacin sai hjy maryam ne tace cikin kidimewa hjy ya zamuyi dashi haka tunda an kira wayan likitan ba,a sameshi ba shikuma Ahmed nasa bai shiga ba.
Tai makon daya samu a lokacin yasa yai wani irin ajiyan zuciya yana fitar da numfashi a wahale.
Zan samu ruwan sanyi da tawul yanzu na fada da sauri hjy maryam ta nufi wurin fridge mamu ta shiga daki ta dauko min tawul ta miko min na dan zuba ruwan ina dan mana mai a goshi da saman zuciya zuwa babban yatsan shi a hankali.
A hankali na dago kai ina fadin don Allah ku dan rage murya kadan idan son samune a dan rage zuwa waje.
Kafin in riki hannuwan shi ina dan murzawa a hankali a lokacin hjy tace kai a daukeshi aje asibiti yafi wanan shiriritan da ake mashi ai.
Hjy wanan halin da yake ciki ina mu mata zamu iya daukan shi haka zuwa waje ai kafin mu fita ya wahala da yawa mamu ke fadi.
Can kawu yai wani irin ajiyan zuciya wanda hankan ya dawo da hankalin kowa a gareshi.
Yace ku dagani don Allah sai dai maganan nasa baya fita sosai daga inda nake gefe rugume da kanshi nace kawu yi shishiru na dan lokaci hakan zai taimaka maka sosai ya rutse idon shi a hankali.
A daidai lokacin na dago kaina wurin mamu ina fadin mamu wayana don Allah.
Ta juya da sauri zuwa part din mu sai gata dauke da wayan a cikin sauri ta miko min na karba har lokacin ina nan rike da hannun kawu ina dan murzawa a hankali.
Karban wayan nayi na dakatar da abinda nakewa kawu na kira wani layi runging aka dauka nace Auwal kana kusa kazo nan gidan kawu da kai da mai aiki guda don Allah yanzu yanzu.
Ya amsa da fadin gamu nan zuwa yanzu hjy na kashe wayan ba a dauki lokaci ba sai ga shiya kirani yana fadin suna kofan gida nace ku shigo gani tafe.
Na fita nayi masu bayani sai gasu da sauri suna bina a baya muka shiga dakin da taimakon su suka kama kawu suka fitar muna dashi zuwa wurun mota yana fadin a barshi yaji sauki ai nace kawu bari aje asibiti dai tunda taimakon gagawa na baka kawai dama.
Auwal da musa mai kula da duk wani kayan gidan suka zo sune suka shiga dashi mota musa ya zauna tare dashi a bayan motar ya dan rungumay shi a jikin shi hjy ta shiga gaba tare da Auwal driver.
Da sauri na shiga dakin mu na saka dogon riga da gyalen shi nacewa mamu ta taso muje tace ai ba sai naje ba tunda ga hjy a can.
Mu tafi nace mamu zuwan mu yana da rana a wurin don Allah jakkata na dauka muka rufo kofa takai yara wurin Amma hjy maryam ke tambaya can zamu tafi na bata amsa da eh muka fita tare har mama hadiye.
Auwal na kira na tambaye shi inda suke ya fada min da kwatancen su mukai asibiti don ni ke jan motan mamu danaji shi duk ya tsufa sai manejin ashe takeyi hakana.
Mun same su a waje ko karban shi ba,ayi ba don akwai mutane damkare a wurin lokacin .
Mun samu hjy tana masifa da masijan kofan likitan kan yayi masu alfarma a duba shi.
Masijan na fadin dole sai sunbi layi zasu ga likita da kike son ganin shi da wuri me ya hana kuyo sammakon zuwa nan.
Ran hjy ya baci ta shiga fada ma masijan bakar magana yana fadin ko dukana zakiyi saidai kiyi amma yau sai kin bi layin nan.
Wani likitane yazo shiga office din yaji hayaniyar yayi yawa ya tsaya yana tambayan ba,asi ana mayar mai na karaso ina mai bayanin halin da kawu ke ciki yana buka gagawan kulawa a lokacin yadda nake mai bayani ya tsaya yana kallona da mamaki har na cikin office din suka fito ya shiga yaga likitan bai dade ba sai gashi ya leko yana fadin muzo mu shiga.
Auwal ya tura keke ina bayan shi hjy tana fada har lokacin muka shiga office din wanda na gani zaune a matsayin likitan mai duba mutanene ya bani mamaki sosai a lokacin.
Shima sunana ya ambata da fadin Fatima Abubakar bauchi yaushe kika dawo kasan nan na kwana biyu na bashi amsa ina fadin kawuna ne baida lafiya yana bukatan kulawan gagawa.
Yace gaki babban likita tare dasu ni wani kulawa zan bashi yanzu a nan ya juya wurin likitan da yai muna hanya yana fadin ka ganeta tare mukai karatu a London sai dai ina gaban ta da shekara uku.
Haba yadda take min bayani yasa na gane tasan wani abu a ciwon mara lafiyan don sai kuma yai shiru .
Bawani bane D Guy ne likitan da muka sama ya mike da kanshi ya taimaka aka dora kawu saman gado lokacin dayan likitan yace mu basu wuri.
Take ya jona mashi ruwa a office din da allurai daya dace ayi mai kafin su fara mashi aune aunen daya dace suyi mai.
Ga na,uran numfashi da zai taimaka mai wajen dawo mai da numfashin shi daidai.
Saida suka gama ya kiramu da hjy muka shiga ya dago kai ya kalleni yace Fatima tun yaushe haka ya same shine ?
Hjy tace haka ya kwana yana jin jikin nasa da safen nan ya karkare rikice muna a gida.
Hjy shine kuka kyaleshi da ciwo haka a gida ke fatima kin san illan hakan kuka barshi har wanan lokacin ?
Idon daya kura min wanda yake min manyattacen kallon da banson nan nasa yana karewa yadda jikina ya kara fresh kowa ya kalleni yassn ina samun hutu lokacin.
Ganin na tsargu da irin kallon da yake min a fakaice ya mike ya koma wurin kawu ya kara masa wani allura har lokacin kawu barci yakeyi bai san inda yake ba.
Muna zaune shiru a gefe daya nida hjy yaci gaba da duban marasa lafiya dake shigowa yanayi yana dan jana da hira ina bashi amsa da kyat game da aikin mu.
Saidai hankalin shi yana gurin kawu yanayi yana dan dago kai lokaci lokaci yana kallon inda kawu yake akwance da ruwa a jikin shi.
Nayi zurfi cikin tunane naga ya mike zuwa wurin kawu likacin na dago kai ina kallin shi ruwan ne ya kare ashi yaje ya zare mai a hankali.
Tare da cire mai na,uran daya jona mai ga hanci na numfashi ya dawo ya zauna yana fadin he be alright insha Allahu.
Amma Fatima kin daddy ki yanzu bukatan hutu da kwanciyan hankali yake so mai yasa kike barin kuna daga mashi hankali hakane ?
Dan satan kallon hjy nayi da take zaune kamar na dole a wurin nace kasan mutum mai iyali ai sai sannu dole a yanzu.
Yace to amma a stage din da yake yanzu bai kamata kuna barin abu yana bata mashi rai ba ko wani lokaci don zaku iya rashi alokacin da baku zataba.
Kawu ne dayayi dan tari ya ja hankalin mu zuwa gareshi ya mike da sauri zuwa bakin gadon yana dan tatabashi a hankali.
Salati kawu yayi lokacin da yake kokarin bude idanuwan shi mikewa nayi na nufi wurin gadon ina mashi sanu da jiki ya bude idon gaba daya ya sauke su gareni yana fadin fatima kece ?
Kawu nice yace Allah yai maki albarka Fatima kinji nace amin kawu a sanyaye.
Muryan hjy ce a bayan mu tana fadin sannu Alh a daidai lokacin da likita take tayar da kawu zaune daga kwancen da yake.
Ya zaunar dashi tare da jinginar dashi a jikin bangon da gadon yake na dan fita zuwa wurin su mamu dake waje nace su shigo kawu ya falka.
Tare muka shigo dasu office din sai faman sannu suke mashi da godiya ga Allah da likita.
Nunani likita yayi yana fadin ga wace ya dace kuyiwa godiya don ita ta bashi kulanwan gagawan daya dace kasancewar ta babban likita data san aikin ta.
Da badon ta bashi abinda ya dace ai mashi da faduwan shi ba da abin ya zama babban matsala yanzu.
Hjy maryam.tace ko za dan bashi ko tea ya shane don bai karyaba koda abin ya faru dashi.
Yace komai zai iyaci a yanzu ba wani matsala ai ta juya tana fadin bari aje gida a dauko kayan tea ke nan.
Likita yace No zaku iya zuwa dashi ai gida ba abinda zai faru insha Allahu ai ita aikin tane ta sani yana nunani da hannu.
Muryan hjy ne take tamnaya nawa zamu bayar likita sai mu koma gida yace haba dai mama.
Kuna iyayyen Fatima kuma zan karbi wani abu a hannun ku kawai dai a daina bata mashi rai dan gujewa irin haka yanzu.
Ga wanan maganin su zaku saya ya dinga amfani dashi ya kalleni yace kin dai san doze din da zaki bashi ai.
Da dai ka fada muna likita zaifi ya danyi dariya yana fadin hjy sai naga kamar kin raina karatun wanan yar taki dai ?
Wanan fa ko a can London babban likitace don bata taba faduwa karatun ta ba har ta gama nayi mamakin da ta dawo kasan nan ta labe a guri daya haka gashi ana neman manyan likitoci irin ku a kasan nan yanzu don matsalin mata da yai yawa.
Kyaleshi tayi don da ba don taimakon da yai muna ba da yasha bakar magana a wurin ta lokacin yadda ya bata haushi yana wani yabona gaban kowa haka a samu abin bara,dawa kuma.
Kawu da kanshi ya taka yana kara yiwa likitan godiya suka fita na juyo a hankali na kalli likita nace a sanyaye doctor mun gode zamu tafi sai wani lokaci kuma ?
No ba godiya tsakani mu ai kin sani nace nagode na juya na zan fita ya bini da kallo har nakai kofa na kama zan bude yace wai ina mijin ki ne Fatima ?
Yana nan na bashi amsa yaran ki nawa yanzu naga ga wani ciki a jikin ki kuma uku na bashi amsa a takaice yace mijin nan naki ya faye wayon tsiya ya tare ko wani kafa.
Ni dai na juya na fita daga office din da sauri zuwa wurin dasu mamu suke na samu suna jirana don key yana hannu na lokacin .
Kafin mu zo har hjy tasa an tayar da mota sun dauki hanya sai motar mamu ya dan bamu matsala wurin tashi da kyat na samu ya tashi ina fadin mamu wanan motar take ai ta tashi aiki sai wata sabuwa kuma ke nan .
Kowa sai mamakin yadda kawu ya murmure kamar bashi aka kwasa ruwa ruwa zuwa asibitu ba a lokacin.
Falon na kawu suka nufa nikan na shige part din mu don in watsa ruwa a jikina kafin inyi sallah.
Sai da nayi sallah na fito na samu abinda naci don ban ko karya ba muka fita daga gidan.
Bayan sallah la,asar na shiga wurin kawu in kara gaida shi da jiki a nan na samu matan nasa duka yana zaune kasa ya mike kafa kamar ba kawu bane da safe ya daga muna hankali sosai.
Da sallama na shigo falon na samu karshen kujera dake kofa na tsuguna ina gaida shi da jiki yace Fatima jiki da sauki.
Aiku keda sannu keda likita hjy maryam tace ai yaron nan yasan aiki shi sosai wallahi jifa Alh kamar bashi ba ni abin ya bani mamaki sosai irin hakane fa kwanaki har ya kwantar da Alh kwana da kwanaki asibiti.
Mamu tace bakiji a waje yayi karatun shi ba ga kuma kayan aikin da suka saka asibitin yanzu ai shi yasa mutane yanzu suke tururuwan zuwa asibitin nasu.
Wasu dai ke karatu waje su karanto abin kwarai wasu kan insunyi sai dai su rike kwali sunan su likitane ba a san komai ba.
Amma a gaban kowa yace fatima tafishi kokari don ita tayi abinda ya dace kafin aje can hjy maryam tace .
Kai maryam da wani magana kike wallahi zai fito fili ya fadi gaskiyane a gaba kowa kai hjy komu fa nan munsa yarinyar nan tayi kokari kafin aje can.
Tayima kanta ai ba wani ba murmushi kawu yayi yana fadin Fatima yaron wani garine wai nace kawu dan garin nan ne ko dan gidan Alh canji naji akace yake .
Au kice dan manyane ya samu karatu yadda ya dace ko can ai inga kudi kudin suna aiki sosai.
Kawu yace yanzu ai na samu likita sai dai matsalan kada na takura mashi don farawa da iya yaki karban kudi.
Kawu muna mutunci dashi tun a nan dan aji su anty salma ne shi yana gaban mu sosai a makaranta.
Ai kaji abin hjy ta sake fada yanzu ina wani mutunci ga macen aure da wani namiji don Allah ai irin abinda akewa gudun ke nan.
Na mike ina fadin kawu Allah ya kara sauki ya amsa da amin fatima na gode kinji nace kai haba kawu.
Ina fita mamu tace umhumm kai duniya yau aka fara karatu ina dai karatun nan dan kowa yayi shi a gidan nan kowa kuma yasan yadda yanayin karatu yake ai.
Maimuna kawu yace ki bar zancen nan don Allah kinji abinda likita ya fada kafin mu dawo gidan nan.
Duk wanda yai jifa a kasuwa yasan wanda ya jefa akace don haka tankawa yabawa tunda ita bata girma a rayuwan ta.
Tau yau kuma taron dangi za ai mun ne a gidan nan don na tabo ya gwal din ku ai komai zanji kenan a gurin ku ashe ?
Ke bari na fada maki jimmai ba tsorin ki nake ji ba gidan nan baki haifeni ba baki kuma girmay ni ba asalima a karkashina kike zaune.
To wanan fitinan ya isheni haka ki sakewa yar mutane mara tayi fitsari a rayuwan ta kin hana yarinyar nan zama da danki.
Yanzu kuma kina kokarin neman sheri ki lakamata naji karatun banza fatima tayi ashe tayi kokari tunda tayi har ta karbi kwalin ta.
Ke aiko secondry naga kin kasa tsayawa ki karbi kwali shi a hannun ki saboda takwallancin tsiya.
Kai haba wanan abin naki da me yai kamane haka a duniya kullun mutum bai maka kirki sai kokarin ganin sherin mutum kike nema ki fada.
Keko ba mai fadan maki hakan baisa kin gano ida matsalanki yake ba balle ki gyara kowa gidan nan yasan bakin cikin ki da yarki ya kaini kwance bawai ba a sani bane .
Ido na saka maki ingani ko zakiyi nadama da abin kunyar da kuka jawo min a garin nan dakuma wurun yan uwana.
Yanzu Alh ni kake fadawa wanan maganan haka yace an fada ke wacece da ba za, a fada maki ba jiran yaran ki suzo garin nan nakeyi muyi zaman karshe dasu akan matsalan ki da yarki.
Yanzu Alh akan maganan nan danayi kake fada min wanan magana haka dan waye baida matsala a duniyan saukin abin dai a tare muka haifeta tare kuma muka bata tarbiya dakai.
Tana kaiwa nan ta mike tabar falon fuuu ta fice acikin fushi taji zafi da nauyin wanan maganan da yayi mata a gaban kishiyoyin duk da tasan sun sani.
Saidai bata bada kafan da wata zata samu fada mata shiba a gidan shiyasa ma yanzun din bata yarda taji kunya ita kadai ba .
Zama nayi ina tunanen kalaman hjy gareni na dan murmusa don zuwa yanzu na gama fidda rai ka kaunar hjy a gareni kuma.
Wayana na kalla dake gefena namika hannu dauka naga ya kamata in kira inji na daukane naga miscall din yaya har biyu.
Kiranshi nayi ya dauka bai bari nayi mai sallama ba koshi yayi yace ina kikaje kibar waya na ringing baki daga ba.
Mun tafi asibiti ne wallahi subbahanallahi baki da lafiyane komai nace a,a kawune yau jikin nasa yadan rikice masa amma yanzu da sauki mun dawo gida dashi.
Innalallahi ya fada kafin yace mai ke damun shi ne har asibiti nace damuwane kawai nake gani don faduwa yayi sume dazu din Allah dai ya kawo sauki wallahi amma abin ba dadi gaskiya.
Yana ina yanzu nace yana gida yanzun ma nafito gaidashi ya danyi shiru can yace Allah ya sauwaka.
Ina Sultana tana barci na bashi amsa zan kashe in kira daddy yanzu inji yaya yakeji da jikin nasa nace a gaida min da yara zasuji yace yanzu sunyi barci tun dazun.
Muna kashewa ya kira daddy sun gaisa yake tambayan shi yaya jikin nasa yace da sauki suka dan taba hira dashi akan jikin kafin ya kashe wayan shi.
Anyi haka da kwana biyu sai ga yaya da yan uwan shi sun shigo gari da dare sun dade a falon mahaifin su kafin su fito zuwa part din mahaifiyar su.
Basu tsayaba don dare yayi a lokacin don haka ban ganshi ba a ranan sai washe gari da suka shigo ya fara shiga wurin mu suka gaisa da mamu daya samu a falo.
Jin muryan shi yasa na yunkura na fito falon ina mashi sannu da zuwa lokacin mamu ta fita daga part din ta barmu.
Ya dago kai ya kalleni yana fadin may yasa wanan kunnuwan naki basa jin magana zahra ya fada yana kallona.
Cikin mamakin abinda nayi na dago kai ina kallon shi fuska dauke da mamaki shi nace may kuma nayi yanzu yaya ?
Kin san nazo gidan nan jiya baki fito kin ga saukan mu balle har in samu darajan samun tarbo daga wurin ki zahra.
Ciki shagwaba nace yaya shine nafito fa yanzu in maka danaji muryan ka ka shigo ya miko min hannu na make kafada na alaman ban zuwa.
Yace me kike nufi da hakan nace kaima kasan ba daidai bane ai tunda an muna iyaka a tsakani mu.
Kema kinbi zancen kenan yanzu nace tun ranan da kawu ya furta hakan na dauki zancen don har yanzu wace kawu ke jiran saukowan ta bata da niyar sauka daga maganan.
Illa ma kiyayya a tsakanin ni da hjy a kullun kara karuwa yakeyi a zuciyar ta don haka dai nake ganin ya kamata mu hakkura da junan mu zaifi mu alheri musanman ma kai yaya da maganan a wurun mahaifiyar ka yake.
Zahra you are very stupid ni kike fadawa wanan maganan haka a tsakiyan idona .
Ki fada min laifina a cikin zancen da kikeso yanke mi hukunci haka banga laifi ki ba don kinga kamar na daga maki kafa da maganan yasa haka yana fadin haka ya tashi ya mike yabar falon .
Ya barni zaune ina binshi da kallo nikuma ban damu da fushin shi ba don yin haka shine mafita a wurui mu.