NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

Don Allah kuyi hakkuri wallahi kusan kwana biyar bamu da wuta layin mu a wahalce na samu har na karasa wanan din da fatan zaku fahince ni yanuwa nagode kuyi hakkuri don Allah.
17/11/2021, 07:22 – ????????????: Bayan Nafisa ta shige gurin hjyn su samira ta kada kai cikin izza da isa ta juya ta fita daga part din kowa na binta da kallon mamaki.
Ta na shiga part din ta ta wani sauke numfashi tare da sake dafa kirjin ta tana fadin ashe zan iya kuwa .
Waya ta dauko tana kiran mahaifiyar ta kira uku ta dauka bata jira sallaman ta ba ta fara fadin umma wallahi nayi duk yadda kikace in masu.
Koke fa da kin zauna kina wani kumshe a daki kamar wata matsoraciya dake nina fada maki kada ki ragawa kowa koshi maigidan da kuke zaman shi ya kawo maki wani gani gani ki face shi tas.
Da mamaki take tambayan mahaifiyar amma umma sai nake ganin shi ai ba daidai bane in masa rashin mutunci tunda kinga neman shiga muke a zuciyar shi.
Shiga ai mun rigada mun shiga samira kedai kawai ki zura ido kiga yadda za a kwasa dashi a karshen aikin kawai.
Ko yanzu me yake iya tabukawa a kanki sai dai ido kawai duk wani kulli kuma da aka aiwatar a kanshi zamu walwale komai da sannu.
Sun dan dauki lokaci suna tataunawa da yar nata kafin su gaji su kashe wayan don kansu .
A bangare na tana ficewa na girgiza kaina tare da kallon abincin dake gaba ina ci ina dan sakw murmushi a fuskana wanda ni kadai nasan ko na meye a lokacin.
Fauziya ce ta kawar da shirun tana fadin wanan matar kamar mara hankali komai nata ita fadane wallahi.
Ni tun ranan dana fara ganinta na gane tana da masifa don mun fita da yaya waje take bin mu da harara bata san na ganta ba a lokacin.
Eh dole ne tayi haka ai don babu abinda zata gwada a gun hjyna na kishi ga yaran nan da tsone ido jama,a duk wanda ya gansu sai yayi magana kan su dole hakan ya kara mata takaici a kansu.
Maria ke nan nace da ita nima kaina wanan abin yana min zafi don mutum wani baka san bakin shi ba sai zuwan mu nake dana sanin zuwa da yaran nan kasan nan a wanan lokacin.
Duk da nasan babu abinda zasu iya masu sai Allah don a tsaye nake kan diyana tun dana haife su don gudun irin hakan.
Na dade wurin zaune har lokacin na kasa tsayar da magana daya a raina wanda zanyi amfani dashi wurin nuna ma wanan samira din nima na iya kamar kowa.
Daki na shiga nayi alwala na gabatar da sallah a zahar da ake kiran sallah a ko ina dadina da kasata ke nan mu sanman arewa zaka ji abinda zai tunatar ma da addinin ka ta ko ina sai dai idan baka da niyar daukan darasi ga hakan.
Waya da nakeyi da anty Ramla ne ya dauke min hankali har lokacin shan maganin hjy yayi ban sani ba saida salma da ban san da shigowan ta gidan ba.
Muryan ta naji kamar daga sama tana fadin madam kece kwance haka a kasa da alama dai tun idar da sallah baki mike ba.
Ga hjy can tana zaman jiran maganin ta nace barin duba mata ke a nan na mike ina murmushi tare da fadin yaushe kika shigo gidan nan ne ?
Ban dade da shigowa ba don a hanya sallah ta riskeni ma mun gaisa na nufi bakin mirro dina na dan gyara muka fito tare da ita zuwa dakin hjyn don dubata.
Da sallama muka shigo dakin mun samesu a zaune dukan su har hjyn dake saman gadon dakin zaune gaida ita nayi tare da tambayan ta jikin ta.
Da sauki kawai ta bani amsa tare da fadin naga har lokaci yana shigewa baki zo kin ban maganin ba.
Sai na dauka wanan dan tsantsamin da kuka yi da samira ne yasakaki bacin rai har kikaki zuwa ki ban da mamaki na juyo a inda nake tsaye nace waye samira hjy don ni harga Allah ba wai na rike sunan ta bane hakana.
Nafisa ce a hasale take fadin kishiyar ki mana wanan yar iskan mai rainin wayau tana ganin kamar tafi kowa zata iya taka kowa duk lokacin da taso.
Salma ce ta tambaya da fadin anyi wani abinne kuma da ita a gidan nan bayan wancan sai mama Asabe ta amsa da fadin ai ita fitinan ta basai da wani dalili ba.
Kawai wai don me aka shanya kayan yara a kusa da bangaren ta shine fadan data shigo nan tanayi da yar uwa dazun.
Dake fatima take fadan hakan kodawa lalaima wanan ta samu wuri da yawa ni na rasa gane mai yaya ke jira har yanzu da ita bai sallame ta ba.
Salma ke nan da wani magana ina zai sallame ta tunda Alh yana son yaga iyakata da sune a yanzu.
Na fahinci komai Alh ne ya hana su daukan wani mataki akan abinda sukai min don kawai yaga iyakata dasu kawai.
Wa yan nan ai ba abin a barsu bane don wani dalili na kawu kisan kai fa suka tashi yi a nan badon Allah ya gyara abin ba .
Nan dai na shiga masu bayanin halin da hjy take ciki duk hankalin su ya tashi sosai nake fadin wanan likitan yaso ya cuta mata da wanan maganun da yake mata amfani dashi don bashi ya kamata ace tasha ba tun faruwan abin.
Mama Asabe ke fadin ai mun gode da zuwan ki don tun randa kuka sauka kasan nan muke samun barci da dare sabanin da can da muke kwana a zaune don zafin ciwon.
A ikon Allah wai yau Fatima ce tasan wanan aikin haka mama har kina fada lokacin data fara karatun nan kan baki yarda da hakan ba.
Ai karatun yana da amfani sosai musanman na diya mace yanzu wanan dawai niyar haka ai sai mace yar uwarka zata taimaka mata.
Ni dai har na gama na fita daga dakin dauke da dan salma da take goyo a lokacin ban kuma ji hjy tayi wani magana ba kuma.
Yaya bai dawo gida ba sai bayan sallah isha,i suka shigo gidan dashi da habbib dakin mahaifiyar su suka fara shiga suka duba jikin ta tare da dan zaunawa da yan uwan su suna dan hiran ciwon uwar tasu.
A lokacin Nafisa ta sako zancen abinda ta samu samira tanayi muna a gidan wanda banso hakan ba don matakin da nake son dauka a kanta lokacin.
Saboda na kula ba a part din ta ake girki ba gaba daya ake girkawa a part din mu akai mata tun bayan zuwan yaya garin ta hana mai aikinta yin girki taba masu aikin umurnin su girka su kai mata nata a can idan sunyi.
Duk da ran yaya ya baci dajin haka sai bai yarda ya nuna bacin ranshi a gurin ba ya hade abin a ranshi yana jin daci a zuciyar shi.
Tun da yamma na ba masu aiki umurnin kada su kara girka komai da samira a part dina da duk wani aiki da zata umurta suyi mata shi na hana ta ba shuganan su umurnin hakan.
Koda yaya ya shigo bai nuna min komai ba har yayi wanka ya fito suka zauna cin abinci dashi da habbib na fito ina gaida habbib din tare da tambayan shi iyalin shi .
Yace ai suna gari tare dasu ya shigo dazun dan washe baki nayi ina fadin ashe zamu hadu dasu wanan karon ma ke nan.
May ya hadaki da wanan yarinyar har ta shigo nan fada dake zahra yaya ya tambayeni cikin katse mu ga maganan da muke da yaya habbib a lokacin.
Wace yarinya ke nan na tambaye shi ina kallon fuskan shi da mamaki sai ya habbib ne yace samira yake nufi man.
Fuska na daure don jin hakan tare da kawar da kaina gefe ina fadin ina ruwana da tsabganta kawai dai tazo tana karanta min hauka a nan ne dazun.
Ya kara tambaya a kan me tazo fada nan din saboda an shanya kayan yara wurin bangareta da maria tayi wanki da safe.
Wanan akwai yar iska tana ganin har ta samu wurin yin hakan ga yayan mu kome habbib ya fada a hasale .
Abinci naga yaya ya fara zubawa kamar bai damu da zancen ba a lokacun hakane ya ban haushi na mike zuwa dakin yarana na barsu a gurin zaune.
Adduan kwanciya nayi masu kafin na juya zuwa dakina na fara kimtsawa don in kwanta sai dai tunawa da ban ba hjy magani ba yasa ni fita lokacin.
Yana zaune dakin wanan karon na samu su salma sun tafi ita da nafisa gida gaidasu nayi har lokacin babu walwala a tare dani.
Hjy magani za a sha nace da ita bayan na nufi wurin maganin kai tsaye ba tare da najira cewan ta ba na fara ballan maganin ina hada mata don tasha.
Har na gama bata maganin ban yi magana ba a dakin nayi masu saida safe na fito zuwa dakina kwanciya nayi don banda ra,ayin zuwa wurin shi ranan.
Can barci ya fara daukana naji shigowan shi dakin tare da kunna wutan dakin ya gauraye da haske lokaci guda.
Takowa yayi zuwa bakin gadon da nake kwance ga yarana sultana da Abbana sai Fauziya da muke kwana tare wani lokaci yauma a dakin ta kwanta.
Tashi muje daki ya fada a daidai lokacinda yazo ya tsaya a kaina ya fada yana mai tsareni da idanuwan shi.
Na dauka ai wacan mai fada a kan ka dani ce zata kwana dakai yau din na fada ciki ciki dan murmushin iya fuska kawai yayi yana fadin mene ?
Shiru nayi mai ban kara magana ba ina gyara kwanciyana ki tashi mu tafi idan zata kwana tare dani ai ba sai kin sani ba don da baki ganni nan ba yanzu yana fadin haka ya juya ya fice daga dakin.
Na dade wurin kwance kamar ba zan tafi dakin ba can dai dole na mike na same shi a dakin bai kwanta ba koda na shigo yana zaune da wayan shi a hannun shi sai dai har ya gama wayan ban iya fahintar maganan da yakeyi ba a lokacin.
Wuri na samu na kwanta kafin inji hannun shi saman jikina ban hanashi komai ba saidai bai samu taimako daga bangarena ba har ya gama abinda yake dani.
Washe gari bayan munyi sallah muka kwanta bamu fito da wuri ba don na fahinci yau hutu yake ba inda zai tafi ke nan .
Don tun zuwanmu kasan ba zance naga ya yini tare damu ba ko yaushe yana zirga zirgan harkan business din shi zuwa wurare daban daban don zuwan nawa ya taimaka mashi sosai ta fanin hjyn shi da sauran abubuwa.
Can cikin barci nake jiyo muryan Samira a kofan dakin tana masifa wanda ni na manta da dokan dana ba masu aiki a kanta.
Ta turo mai aikin ta karban abinci su kace madam ta basu umurnin kada su kara saka mata abincin ko wani aiki shine dalilun wanan ashar din da take dura min da farar safiyan nan haka.
Yun kurawa nayi da niyar tashi in fita don in same ta in bata amsa sai naji yaya ya rikeni daga inda yake kwance yana fadin ina zakije kuma ?
Dan jiyowa nayi na kalleshi ina fadin wurin wanan mara hankalin kada ta firgita min yara da safen nan kuma don duk sun tsorata da fitinan ta tun zuwan mu garin nan.
Is Over ki kyaleta kawai tayi haushinta ta gaji ta tafi idan kin fita abin ba zai kare ba kuma yanzu yace.
Amma dai yaya kana jin irin kalamin da take fada min marasa dadi haka da safen nan yace nace ki barta ko bakiji bane wai.
Hakan yasa na koma na kwanta na lafe ban tashi ba sai shi da yaji hayaniyar yayi yawa ne ya fita daga dakin ina kallon shi.
Tana tsaye a tsakiyan falon sai masifa takeyi ido rufe jin kara bude kofan ne yasa ta juyowa tana fuskantar kofan.
Jallabiya ce fara a jikin shi sai takalman daya zura a kafafun shi ya fito fuska daure yake kare mata kallo a cikin tsana.
Itama kallon shi takeyi sai taji dan nauyin ci gaba da masifan da takeyi din tana fadin ashe kana cikima dama wurin ku nazo don matarka ta hana wai a ban abinci dayi min aiki shine nazo jin dalilin hakan.
Ke dakata idan ta bada dokan hakan laifi ne ko kin manta cewa nan din gidan tane ita da yayan ta tana da ikon yin komai da taso da kowa.
Don haka ki bace min daga nan tun baki hadu da bacin raina ba a yanzu mara hankali kawai zaki shigowa mutane da sassafen nan kina karanto muna hauka .
Ban gane abinda hakan ke nufi ba ke nan nidin may ye matsayina kake nufi a gidan nan yanzu.
Zaki iya shiga ki tambayi wace ta kawo ki gidan ai tana cikin gidan nan ko yanzu kuma don kinyi mata rashin mutuncin alakan hakan ya yanke a tsakanin kune kuma .
Kofan fita ya kara nuna mata yana fadin ki fita tun kan ranki yafi nan baci a gidan nan yanzu.
Ganin da tayi babu wasa ko kadan a fuskanshi yasa ta juya ta bar dakin da sauri dan saura kiris hawayen da take boyewa ya zubo mata a wurin.
Na shiga uku take fadi a ranta har hannun ta na rawa wurin daukan wayan ta ta kira mahaifiyar ta da sauri take kira tayi sa, a ta daga wayan.
Samira me kuma ya faru da safen nan yanzu kuma umma wallahi yau mutumin nan ya gama dani a gaban kowa a gidan nan.
Gaban kowa fa ya fada min maganganu masu zafi har yake fadin wai zaman mahaifiyar shi nake gata nan daki inje in tambaye ta.
Gida na matar shine da yaran ta don haka tana da iko akan komai dake gidan bani ba.
Ke nan umma may yake nufin da wanan maganan nasa yanzu yana nufin dama zaman wanan matar ke nan nakeyi a gidan ba nasa b, , ,
Samira ki natsu ki min bayanin komai yadda zan fahinta kina hada min magana cikin magana bana ganewa.
Umma abinda ya faru ke nan nake fada maki ni wanan abin gaskiya a yanzu ya fara isata gaskiya.
Ke gani nan zuwa yanzu tunda yana gidan sai da muka kashe duk abinda ke gare mu zaki wani ce wai kin fara sarewa da zancen haka.
Dakin ya shigo lokacin har na mike zaune ina sauraren abinda suke fadi daga falon jin shigowan shi yasa na mike tsaye ina kokarin saka hijjab dina a jiki.
Ina kuma zaki tafi yanzu yaran basu falka ba don babu kowa a waje a cikin su har maria ya fada.
Zan duba hjy ne kada taga yau ban lekota ba har lokacin nan lokacin shan magabin ta ya dan gwauta kadan na bashi amsa ina fita daga dakin.
Bina yayi da kallo har na bace mai da gani ya sauke ajiyan zuciya tare da girgiza kan shi don yana ganin wautana kan abinda baikai na fushi ba na dauki zafi dashi haka.
Kai ya kara girgizawa yana kokarin cire rigan jikin shi don shiga ban daki ya watsa ruwa a jikin shi ya fito zuwa duba jikin mahaifiyar su.
Ban shiga wurin hjyn ba saida nayi wanka na gyara jikina tsab na fito inda kusan lokaci daya muka shiga don banbdade a ciki ba shima ya shigo suna gaisawa tare da tambayan yadda take jin jikin nata yanzu.
Hjy bata kai ga bashi amsa ba muryan hjy sabuwa ya katsesu tana fadin ina mara kunyar yake yana ganin yanzu yafi karfin mutane don ya samu daurin gindi a wurin iyayyen shi yasa kake son taka kowa yadda kakeso.
Har kan wanan yarinyar kake kokarin wullakanta yar uwan ka ka fifita agaolan gidan ku da aka cinna maku da sunan mowan gidan ka komay ?
Hjy kin ban mamaki kina gidan nan har umar ya tsaya yana fadin wanan magana ga yar uwan shi baki kwabe shi ba tana fada ra sawo kai dakin sai taja ta tsaya don ganin mu da tayi a dakin don bata zaci hakan ba a lokacin.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button