SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL
SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
16/11/2021, 22:43 – ????????????: JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YASA MUNA CIKIN YAN, TATTATUN BAYIN SA ALLAH KA KARA MUNA IMANI A ZUKATAN MU AMIN, , , ,
Falom yayi tsit babu mai magana kowa ya natsu don ganin yadda Alh ke magana rai bace ga kowa dake falin a lokacin .
Inda ya jaddawa matan shi idan sun kara fada zai dauki mataki akan ko wace mace data kawo masa fitina a gida.
Sai kuma ya juyo kan yaran gidan inda yake fada sosai akan dole ne mu hade kai bai son nuna bambaci kuma ya zama dole na baya ya girmama na gaban shi.
Haka ku ya zama dole ga babba ya tausayawa na kasa dashi bai yarda da akidar nuna banbanci ba a gidan shi.
Ranan dai yayi fada sosai akarshe ya sallami kowa daga falon yace a bashi wuri yana son ya huta.
Mu yara muka fara fita sai ga manyan mun hango suna firowa suma haka ya nuna yana son ya kadaice ne a lokacin.
Muna shiga part din mu ina kokarin shigewa dakin mu muryan mamu ya dakatar dani daga shiga dakin da zanyi.
Sayadi mai ya kaiki dukan Nafisa don Allah har yaushe kika zo gidan nan da kika fara fada dasu ?
Mamu zagin ki fa tayi a gabana ni kuma ba mare ta dan murmushi naga ta sauke a fuskanta ni kuma naci gaba da fadin kuma tun ranan da na fara zuwa school suke min rainin wayau a gidan nan kullun hakuri nake dasu.
Kai ke kan da ace zagi yana tsiro a jikin mutum ai da ban saura da fata a jikina ba don zagi kullun a cikin sa nake gidan tunda na auri mijin su.
Baki na dan turo gaba ina magana ciki ciki tace don Allah ki daina biyewa shirmay su kuna zama daidai dasu a gidan nan in munyi hakkuri watarana wucewa zaiyi.
Duniyar har guda nawa take ma da mutum zai biyewa rudin ta shedan ya ribance shi.
Kinga neman magana dama suke a kan mu don zaman ki gidan nan bai masu dadi ba ba dai yadda zasuyi damune don Allah ki bar biye masu kuna wanan jidalin haka.
Nace na bari mamu tace kin kyauta Allah yayi maku albarka ki kula da kannen ki dakyau duk lokacin da kuka fita don haka idona yake a kansu zuwan ki ne ma har suka daina shiga tsangwama sosai.
Bayan mun gama na shiga nayi wanka ranan dai zukatan kowa ba dadi a gidan don su a nasu bangare duk da adalcin da Alh yayi hakan bai masu ba.
Sai suke ganin ai ya goyi bayan mu nida mamu ne don baiyi masu yadda suke so ba haka yasa hjy ta daga waya tana kiran yayanta tana labarta masu abinda ya faru.
Sai dai ta canza maganan inda ta fada masu abinda ba shi ba rayukan su ya baci sosai kan irin abinda mahaifi su kewa hjy akan sauran matan shi yanzu
Washe gari ko da muka tafi school har muka dawo gida ba wanda yai mi magana a ciki su nasan sun hade min kaine don su matseni a gidan.
Sai dai mun dawo mun samu farin ciki a gidan don a ranan Alh ya gabatarwa matan shi da kyautan motocin da dan shi ya turo masu.
Haka yasa mamu zuwa part din hjy jummai tayi godiya akan alherin da danta ya aiko masu don yaba kyauta ai tukwaici ne.
Sai dai tayi da ta sanin zuwa duk da dai ta debe mata hakki zama a tsakanin su dan ta yayi masu alheri kuma ta gode.
Don hjy cewa tayi bani ya kamata kiwa godiya ba ai tunda bada miyau bakina aka sai maku motar ba aima baku iya ba da kuke son gasa dani ai da sai diyan da kuka haifa su sai maku ba dana a tillasata mashi ya saya maku ba don kawai ana son yin gasa dani a gidan.
Mamu dai godiyan ta dada yi mata ta fito ta barta tana mita akan zancen danta ya saya masu mota wai a munafuce ta .
An tillata mashi dole don ya sai mota mota suma sai ya saya masu mamu na fita daga part din ta takasa hakkuri ta nufi part din Amma a fusace.
Muna falon lokacin muna dan hira da Amma sai su Aisha da bilki dake kitso a gefe daya ganin ta haka Amma tasan ba lafiya ba wanan shigowan da tai mata a part.
Wanda yanayi ta ya kara tabbatarwa Amman da hakan don bata shigo idan ta zo da safe sun gaisa sai kuma wani washegarin idan ta shigo gaida ita.
Gaida ita mukayi nice ta karshe bata karba muna gaisuwan namu ba sai makarin hawa fushi da tayi.
Tun daga tsaye take fadin hajiya gurin ki nazo Amma tana fadin ai gani nayi but na mike ina fadin yan kanne suzo muje.
A daidai lokacin ta juyo inda muke tana fadin ku bamu guri zamuyi nagana sai tayi rashin sa,a don ni har na daga zan bar wurin ko.
Amma tace ai ita wana tasan ta ido do harta mike kafin ki kora su ko idanuwan ta sun kada sunyi ja saboda fitina.
Sai da taga ficewan mu a falon ta kara kallon Amma tace hajiya gurin ki nazo Amma ta dago kai ta kura ma yanayin da take ciki na tashin hankali ido kafin tace.
Samu wuri ki zauna ki natsu jimmai naga ranki kamar abace yake a yanayin da kika shigo wuri ta samu ta zauna kafinta fara fadin.
Hajiya Alh bai son zaman lafiya a kidan nan asalima shike kawo rikicin komai a cikin gidan nan yanzu hajiya ya dace ace Alh ya turasawa yaran don sun min abu yacd sai sunyiwa sauran matan shi .
Babu haufi babu ko jin nauyi da dogon turanci Amma tace kwarai don ko shi ya haife su kamar yadda kika haife su matuka suna son albarkan mahaifi ya bibiye su.
Sai dai ban tari numfashin ki ba na kai ga baki amsan maganan ki bansani ba ko yayi haka ta hanyar da sharia ta hanane kinga anan kuma maganan ki gaskiya ce.
Kallon Amma takeyi kamar ta kurma ihu a lokacin saidai jin maganan ta na karshe ya bata kwarin gwiwan cigaba da maganan ta.
Tace hajiya kin san komai a gidan nan yanzu ya dace don kawai yaran nan sun saya min mota Alh ya tursasa su akan sai sin sai ma sauran matan shi dole.
Shi sanin ya akaita hakan idan ko hakane bai kyauta ba Amma ta fadi tana gyara daurin dan kwalin ta.
Hakan ne ma hajiya don ban sani ba sai da motocin suka zo dana yi magana yace min ban isa ba Amma ta katse ta da fadin.
Shi umarun ya fada maki da bakin shi an tursasa shi ya sai masu mota ko wani ya fada maki haka ?
Hajiya kin san halin yaron nan ba zai fito fili ya fada min kai tsaye ba da binkice nane na gano hakan ya faru.
Amma ta girgiza kai tana fadin hasashen ki da binciken ki ya fada maki karya jimmai idan ma gaskiya ne haka ne ina abin farin cikine ya samay ki a gidan nan.
Yau har Allah ya nuna maki ranan da dan da kika haifa zaiyi alheri irin haka kinga ke nan ko a nan kin nuna kina sama dasu ke nan tunda har danki yana iya aiko masu da alheri irin haka.
Kinga Allah ya nuna masu ke har kullun kina gaba dasu ke nan don har dan ki bake ba zai iya kyautata masu da abinda basu dashi.
A lokacin hjy jummai ta sauke wani ajiyan zuciya Amma taci gaba da fadin kin ga kuma maganan nan Allah yasa a gabana akayi shi.
Zaki tuna da ranan da kika daki tagwayen nan har zazzabi ya kama su aka kaisu asibiti bayan sun dawo uban ya shigo dasu nan ya zauna ke nan sai ga umar din ya bugo wa mahaifin nasa waya.
Suna gausawa yaji kukan yaron da murya na ina fadin yaron yayi shiru uban yayi waya shine umar din ke tambayan ina kusa ne yaji murya na a gurina uban yake yace eh.
Shine yakd fadin a bani wayan mu gaisa bayan na karbi wayan yakd fadin ke dawa ke fada nake cewa nida kanin ka mai irin zubin ka ke muna kukan banza don raki.
Nan dai nake fada mai abinda ya faru a lokacin ne yace damu suyi hakkuri zai saya masu mota maman su taita shiga dasu.
Jimmai kinji yadda zancen sayan motan nan yazo don haka ba wanda kike tunane bane ya tilasata wa danki sayen motan nan.
Ta lumshe ido a hankali tana mai jin zafin tsohuwar kan maganan dafa fadi mata lokacin
16/11/2021, 22:43 – ????????????: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM TAWAKKALTU ILLA, LAH, LAUHAULA WULLA KUWATI, INNA BILLAHI ALIYAL AZEEM, , , , , , , ,