SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL
SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

Ina zaune a class fuskana yana ga littafin lissafi da aka gama koya muna don kawai in gane nake da naci ga karatu idan an koya muna malami ya fita ban tsayawa surutu kamar yadda da yawan mu ke samun sakewa idan ba kowa a cikin ajin mu.
Jin shiru da ajin yayi sai kuma kanshin da yadaki hancina yasa ni dago kaina da sauri a zatona wani malamin ne ya shigo muna.
Sai dai ina dago kai na gansu a gabana seniors din makarantan ne wanan da ranan su salma suka gudu don shi yana tsakiyan su mutum biyu biyu a gefen shi su biyar sun shi a tsakiya.
Gabana ne ya fadi na juya da sauri naga duk yan ajin a mike suke sai ni kadai da kaina yake duke lokacin da suka shigo ajin ban sani ba haka yasa nayi yunkurin mikewa a lokacin.
Kamar yadda naga kowa yayi masu a ajin sai ya nuna min hannu ba tare da yai magana ba alaman in koma in zauna.
Dam kara juyawa nayi in ga ko da wani yake magana sai naga akasin hakan gare shi ba da kowa yake magana ba kuma yaki budan baki yayi magana.
A hankali na koma kamar yadda nake da farko ina gyara littafina da ke saman table a bude ya juya ba ba tare da ya tafi ba sai wani yace min.
Ke may ye sunan ki na dago a hankali nace wa ni ina nuna kaina gare shi yace dake nake may ye sunan ki akace.
Fatima Abubukar azare na basu amsa a takaice ina fadin haka ya fara tafiya sauran suka bi bayan shi suma.
Har lokacin ajin na tsit ba wanda ke magana a cikin students sai da suka fice ajin da kamar minti biyar dan kus,kus ya fara a ajin sai ga su sadiya sani sun zo table dina sukace ke may kikai wa su gentle yau ?
Waye kuma gentle na tambaye su a cikin tsiwa don ban son abinda zai hada ni hurda dasu don na lura yin kawa babu abinda ke cikin sa sai munafunci da saka wasa yasa nake jaye kaina ga kowa.
Don ina ganin yadda kullun ake turke a cikin ajin ba mazan ba ba matan ajin ba sai kuma wasan banza a tsakanin yan mazan da mata da zaran babu malami a jin.
Ganin haka ke sa da zara babu malami zan dauko littafina in dinga bita da sannu har in gane abinda aka koyar damu may yake nu.
Da mamaki suke kallo na har suna hada baki wurin fadin ke baki san Gentle ba duk zaman ki school din nan ga yan mata na rushing a kasa duk yawancin seniors din son shi sukeyi.
Yana masu yanga da han aji kuma mahaifin shi a garin nan last done ne na kudi shi din ma ai ba a nan ya tashi ba daga baya ne suka dawo nan kasan.
Bansan shi ba kuma bani son sani don ba abinda nazo yi ke nan ba don Allah ku ban wuri abu nake anan yanzu.
Ina fadin haka na dukar da kaina naci gaba da karatun da nake ba tare da nasa abinda nake karantawa ba a lokacin.
Don haushi da takaici daya lulube lokaci daya karshe ma rufe littafin na kifa kaina a table ina tunanen da ban samu amsan shi ba don ban san dalilin tambayan sunana da seniors din sukayi ba.
Bayan mun tashi daga school har lokacin ban sake ba can na hangi kanne tafe yana dangyashi alaman yaji ciwo a kafa shi da sauri sauri na karasa gurin yaron.
Ina tambayan shi samir ke cewa wai wani moniter din su ne ta duke shi har ta fadi a hasale na dago daga duken da nake ina tambayan shi waye monitor din ajin nasu ya nuna mi wata bakar jeep dake gefen mu.
Ba tsaya wani abu ba na nufi motar a hssale rike da hannu kanina lokacin driver yana kokarin rufe kofan motar yara sun gama shiga ciki.
A tsiwace nace malam kada ka rufe kofa zanga yaro dake cikin motar nan dan Allah ya juyo da mamaki yana kallona duk da kakin dana gani a jikin shi bai sa naji tsoron shi ba.
A ckiin harshen turanci ya kara tambayana na fada mai sai yayi kokatin rufe kofan ashe ma bashi bane driver driver yana gaban mota yana jiranshi.
Rike kofan motar yayi kokari yi sai nasa karfina na tare kofan daga ciki motar naji ana bashi umurni da ya bude.
Ya sara kafin ya bude motar wanan ne da suke kira da gentle zaune a bayan motar tare da wani karamin yaro da yarinya dukkan su saye da uniform din school din.
Juyawa nayi wurin salim dake yamotse fuska nace kai waya tabe ka a cikin su yaron a hankali ya dago hannun shi yana nuna min cikin motar cikin tsawa nace bazakai magana ba ka tsaya kana nuni da hannu.
Yace a hankali wanan ne ya nuna min yaron gaba dayan su sun tsare da ido har security din nasu nace.
Kai may yai maka kajin masa wanan rauni haka a kafa halan a gidan ku ba,a koyama tausayin na kasa dakai bane?
Haiy haiy make faruwa ne wai wanan gentle din ya dakatar dani daga magana ta yaci gaba da fadin may ya faru ne da kafan tashi yana magana da karamin yaron a cikin yanayin kallon shi.
Banji may yaron yake fada mai ba sai dai karshe da yace nikuma na dake shi, nace don ka fishi girma ko may ?
Ke dakata su fada muna yace kamar baison magana shiru nayi ina murguda vaki har ya gama tambayan yaran ba,asin maganan su.
Ok ka bashi hakkuri yace bayan ya gama sauraren yaran akan abinda ya hada su tare da fadin John ina son mu kai yaron nan asibiti a duba kafan shi.
Nace ku barshi tunda ya bashi hakkuri ai maje gida a duba mai lokaci ya kure a yanzu ina fadin haka na juya zuwa wurin motar mu.
Wanda sai lokacin ns kula ashe hankalin mutane duk akan mu yake ban kula da hakan ba illa jan kanne zuwa wurin motar mu daya riga ya faka ko.
Muna zuwa na dinga tura yaran a mota sai da naga sun shiga sun zauna na yun kura nima na shiga wurin zamana dake can baya inda salma ta bani tun ranan farkon zuwana school din.
Sai dai ina zama naga wanan Gentle din yazo har bakin motar mu ya zura hannu ya dauki yaron ya juya zuwa wurin motar su.
Kkarin fita nake daga inda nake zaune sai dai kafin na iso har motar tasu ta daga daga wurin ko tana kokarin barin makarantar.
Na shiga uku ba furta ina kokarin bin motar da gudu sai dai ina motar har ta halba saman titin ko tana kokarin bace min da gani.
Ba sanin garin nayi ba don haka ban san inda suka dosa da yaron ba a lokacin iba kokari tsala ihu baji salma na fadin.
Kai wana masifan da daddy ya kwaso muna da may yai kama don Allah yarinya kamar yar mahakaciya gata nan kina shiga mota ko mu wuce mu barki a gurin nan yanzu.
Sai Adawiya tace don Allah kyale ta da haukanta anty salma akace mata bata zaiyi ne a wurin su waye bai san yan gidan general ba a garin nan ?
Koma sace shi sukayi ai sun rage muna fitina a gidan mu ne tunda ba su kadai bane yara Nafisa ke fadin wanan maganan .
Na kalleta shekeke tare da fadin dama kowa yasan fatan ku ke nan a garin nan kuna bakin cikin buda ido ku ganmu a gidan ku.
Sai dai kun makara don jini ya riga da ya gauraye da ruwa mun zamay maku ciwon ido ko sai kallo ko tsiyayyan hawaye.
Zama salma tayi a mota tare da ba driver umurnin da su tafi ina kallo sukaja mota suka barni gurin tsaye.
Sannu a hankali ake watsewa a haraban makarantar har aka dauki yaran karshe.
Ya rage saini sai security makaranta kowa har malamai sun watse a school din na hada kai da gwiwa ina kuka a hankali mara sauti ba abinda zuciyata keyi sai tunanen halin da dan uwana yake ciki.
Ko su din su waye da har zasuyi min gaba gadi haka da dan uwana jin karan motan da nayi baisa na dago kaina daga yanayin da nake ciki ba.
Muryan nan mai kama dana izza nasa ya karade min kunne yana fadin ke tashi kuje gida time na shigewa kada a ga kun dade.
Da sauri na dago kaina ina kallon su na sauke ga kanina dake rike a hannun shi an daure kafan da bandage.
Cikin wani kuzari na mike tsaye ina fadin samir ina suka kai min kai may sukai maka samir.
Maikon yai magana sai kawai ya jingina kansa a jikina yana lumshe ido kamshi na shafa a hankali ina ma yaron sannu samir.
Ina kokarin rike hannun yaron muka fara tafiya ba tare da nasan inda zamu dosa ba don a mota muke zuwa kullun sai gashi yau zamu a kafa tunanen da nakeyi ke nan a raina .
Horn din mota mukaji a bayan mu na juyo sune na kawar da kaina da sauri daga kallon su muryan shi naji yana fadin ku shigo mu sauke ku gida.
Kamar in ce a,a sai na tuna ban san hanya ba don haka banyi gardaman shiga ba wani irin kamshi da sanyi naji ya doki hancina da gangan jikina a lokaci daya.
Duk sai na raina kaina a karo na farko a gaban wani na zauna a takure wuri daya can nisa dashi kadan kannen shi da samir suna tsakiya mu haka yasa nagane basu je gida ba suma har lokacin.
Hanya kawai nake iya nuna masu ban san sunan unguwa ba lokacin da muka kai kwanan unguwan na nuna a cikin sauri da fadin wanan ne unguwar mu.
Da kwatance na nuna gidan muna tsayawa mamu da Alh tare daAhmed suna kokarin shiga mota muka karaso a gaban su muka sauka daga motar fuskokin su da alaman damuwa karara.
Ina kallon ajiyan zuciyar da mamu tayi da mukai arba da ita na fito da sauri ina fadin mamu wallahi ba da gangan na tsaya ba samir ne yayi targade a kafan shi shine, , , , ,
Muryan Gentle ne ya katse ni da yake gaidasu Alh a cikin ladabi tare dayi masu bayanin abinda ya faru tsakanin yaran a class.
Ya kara da fadin shine muka dauki yaron zuwa asibitin mu don a duba kafan idan baiji ciwo sosai Alhamdullahi mun samu dan targade yayi a kafan shine aka daure tare da bashi wanan maganin yana miko masu ledan magani.
Nasan zamu samu wanan a school don yarda muka barta hankalin ta ya tashi muna komawa muka samay ta can shine muka kawo su gida yanzu.
Ya kare da fadin don Allah ayi hakkuri ga abinda ya faru kuskure aka samu Alh yace babu komai dan albarka mungode hakika hankalin mu ya tashi.
Da yan uwansu suka dawo ba tare da su ba sai dai da suke fadin wai da yan gidan kune suke rikici yasa ban wani daga hankalina ba.
Don nasan gidan ku ba batacen gida bane a garin nan ayi hakkuri dai nagode da fahintana da kukayi mu zamu tafi ke nan.
Godiya Alh dake rike da hannun Samir ya kara yi mai suka wuce sai lokacin Ahmed dake kallon yaron tunda ya fara magana ya yi magana.
Ya akayi yan uwanki suka dawo ba tare dake ba nace da zasu tafi da yaron ban san inda zasu kaishi ba na fito daga motar shine salma tace su wuce su barni.
Nafisa kuma tace wai ina cika su da ihu in ma samir ya bata ai sun rage mugun iri a gidan su ido suka zubo min ina rabbata masu yadda akayi .
Muryan Amma ne bayan mu ta fito cikin tashin hankali tana fadin yaran sun dawo ne ko angansu ne ?
Mamuce tace yanzu aka sauke su ashe asibiti aka kai samir din shine ita kuma ta tsaya tana masu ihu yan uwa suka wuto suka barta a can.
A man tanada gaskiyar ta ina zata dawo tabar dan uwanta a can bata san halin da yake ciki ba su da dauke shi bai abin bai damay su ba ai kinga sun dawo ko ?
Hajiya wa yan nan yara ban san ya akayi haka ya shige su akan yan uwan su ba ga Alh na iya kokarin shi wurin hada kan su guri daya Ahmeda ke fadi cikin bacin rai.
Kaiyya kamar baka san tsatson da suka fito ba ai wa kumbo wa kayan cikin sa mugun akidar da ake cusa masu ne a zukatan su tun suna kanana shine ke aiki.
Hajiya mu shiga daga ciki Alh ya ce da ranshi ke mashi suya kan abinda yaran shi suka aikata amma sun zo gida sun fadi abinda ba shi ba da farko.
Ganin kafan ya farawa yaron tsami yasa na sunkuya na dauke shi na barsu a gurin suna karasa magana don Amma bilhaki take fada yadda wanda duk ke ciki zai iya jinta.
Kasuwan da Alh bai koma ba ke nan ranan ya zauna a gida gashi girkin mamu ne haka ya kara tunzura ran matan shi kunsan mata basu raina abin kishi sai suke ganin hakan da yayi yayi ne don ya gyarawa mamu ranta damu yayan ta.
Bai yi maganan ba sai dai washe gari da muka shirya zamu school naji mamu tace min mu dakance ta itace zata dinga sauke mu school daga ranan.
Hakan yai min dadi a raina sosai don zan huta da shaguben yayan gidan da suke min idan zamu school dasu gara da rana wurin zuwa islamiya don Ahmed ke yawan kai mu kamar yadda yayi alkawarin kaimu din kullun sai dai wani lokaci idan aiki yai masa yawa driver ya kaimu.
Idan kuma yarinya bata fito da sauri ba ko taki zuwa zai dauki matakin haka da kanshi don har kofan uwarta zai tafi ya ci mata mutunci a can sai ta fito ko an fada mai dalilin rashin zuwanta.
Hakan yana bakanta ran iyayyen sosai ba yadda zasuyi don maigidan ya bashi go ahead din haka dole ko subi umurnin shi.
Mun rigasu ficewa gidan don a zaton su bamu fito ba mun makara ne yasa sukaja motar su suka tafi ba tare da sun jiramu ba duk da su Aisha sun ce a dan dakanci fitowan mu mana.
Sai suka yayyako su da masifa dole sukai shiru suka kyale su hakana suna kallo aka tafi badamu ba .
Samir bai samu fita ba ranan saboda kafan shi da yai masa tsami ga zazzabi na barazana akanshi yasa mamu tace ya zauna gida.
Kai rayuwan gidan yawa da gidan da ake da zafin kishi sai a hankali duk wanan abinda ya samu yaron bai sa wani daga cikin matan gidan ta jajantawa mahaifiyar mu ba.
Don banga wanda ya leko part din namu ba da sunan zuwa duban yaron da ake fadin wasu sun tafi dashi a mota ni kuma an barni a school ina ihu.
Hakan yasa na kara fahintar zaman da mahaifiyar mu takeyi a gidan da abokan zaman ta abin duk da nake yarinya a lokacin ya ban haushi da mamaki a raina sai dai babu galin magana a gare ni don mamu ta kwabeni ga hakan.
A school kuma tun bayan gama assemble ina class din mu zaune sai dai ban sani ba ashe maganan ya karde school wai nayiwa headboy rashin mutunci jiya a gaban kowa har yasa security din sa suka zane ni.
Wasu kuma suce ba haka bane kanina ne yayi rashin kunya wa head boy din da kowa ke tsoro ya sa aka hukunta yaron karya dai iri iri gashi nan irin na students ranan yana yawo a school.
Haka yasa yan matan dake rawan kai gare shi sukaji zafi suka shirya daukan mataki a kaina duk ina classa ban san anayi ba ciki kuwa harda salma don itama senior ce a lokacin.
Bayan breakfast sai gashi wata ta zo kirana wai in samay su a bayan shop din school ban faye fita ba during break sai idan zan duba kannena ne nakan dan fita.
Na tattara kayana na nufi inda suke nema din na samay su sun kai su goma sha a wurin ko wace ta murtuke fuska ga wani dogon bulala a hannun wace ta fisu tsaruwa da girma a hannun ta.
Cikin rashin ko in kula na isa gurin tunda nasan ban masu komai ba asalim ko yan ajin mi ni ba abinda ke hadani da kowa.
Ina zuwa nace ance kuna nema na anan ko gaba dayan su suka hayyayako min lokaci guda wai may na taka da bazan rusuna ba zan zo masu a hakan.
Wata tace inda ba ke din yar wata da wani ne wace ke labe a gidan mutane take agolanci zakiwa mutane daukan kai.
Raina ya baci da kalaman ta nace dadin abindai ba shegiya akace maku nake ba mutuwa ce inda ubana yaje uban kowa zai iya zuwa can.
Daga kirana sai ku kama zagina may ya hadani daku ba ruwana da kowa a school din nan abinda iyayyena suka kawo ni yi nakeyi.
Taaaa naji saukan wanan bulalan a jikina sai da na murde a wuri daya kafin in rike bulalan da tayi niyar kara zabga min a jikina again.
Sake yar iska ko na illanta ki yau a school din nan inga uban da kike takama dashi da zai tsaya maki a garin nan.
Ke har kin isa kiwa gentle rashi kunya na rasa may ye dalilin shi na rashin daukan mataki ga wanan yar iskan mara kunya.
Banda kowa sai Allah kamar yadda aka fada maku ina zaman angolanci ne a wurin mijin uwata kuma kawuna.
Allah ne gatana shine gatana a garin nan ke da ubanki zai zauna gadin duniya sai ya zauna na karasa fadi ina mikewa tsaye tare da kokarin tattara bujena don na shirya masu bala,in dana boye a ranan.
Wata tace ji yar iska har mikewa tayi bayan ana fadi tana fadin da takeyi nace ke uwata ce da zanji tsoron ki komay na san dai ban maku komai ba a kan gaskiyana nake don haka wace ta isa ta kara buguna ta gani.
Salma tace ba na fada maku yar iska bace bata da kunya dama yanzu ai zaku gani da idon ku nace salma rufe bakin ki naki bala,in yana zuwa don nasan kece da hadin wanan sherin.
Sai wata tace kunga ku kyale wanan yarinyar ta tafi kunga dai wanan abin ba zai haifa muna da mai ido ba tunda tafimu gaskiya bata san komai ba tace.
Sukai cikin ta da sababi dole tayi shiru a wurin ta koma gefe tana kallon ikon Allah ga bulala na rike a hannu na da shirin bala,i gare su sauran yan makaranta har sun fara zagaye wurin don mutane basu raina abin kallo balle sun samu ana rike tsakanin prefect da jinior din school.
Kokarin kwace bulalan tayi sai ko na hanata nan kokawa ta kaure muna da tasan inda na fito da ita tashin falo tuntube da remote bata gwada hakan gare ni ba ranan.
Na iya kokawa da yan matan gidan baffa shiyasa na samu lafiya ga matan sai mazan kan jibgeni son ransu.
Batai aune ba sai gata a kasa na kashe ta nan sukayo kaina da duka nace in bakayi bani guri suna kai min duka ina ramawa na haukace masu gaba daya sai wuru ya dauki ihu baki daya hankali ya dawo gare mu.
Muryan maza ne suke fadin amma ko kunji kunya wanan yar ficiciyar yarinyar ne kuke haka da ita ta gagare ku wata ta kawo min duka na kustsa cikin taro suna ja da baya sai dana cin mata muka kaure da ita.
Sai da malamai suka zo suka raba da kan su aka kwashe mu zuwa staff room inda da farko aka ban laifi sai na fashe da kuka ina fadi don anga ubana ya mutum zai sa su zageni.
Ina zaune na ban san hawa ba ban san sauka ba suka aika in fito suna nema na ina zuwa suka hauni da zagi da duka wai nayiwa wani gentle rashin mutunci wanda nima ban san hakan ya faru ba don tunda safe nake aji zaune ban fito ba.
Will you keep quiety malamin ya fada da karfi sai wata malama tace amma malam sadiq kabi maganan nan yarinya ka fahinci abinda take fadi.
Nan jikin shi yai sanyi ya fara bin ba,asin maganan dalla dallah har suka fahinci abinda ke faruwa aka gane duk salmace mai hadin a kaina.
Har mansur din da suke kira da gentle aka kira a wurin yayi masu bayanin abinda ya faru tsakanin mu jiya bai rage komai ba nan malamai mata sukai kansu.
Zane su akayi akai muna assemblen kan mu ranan ni hukuncin yin ruduness ga senior na aka kamani dashi inda aka hukunta ni wanan yasa aka san da ni a school din.
Bayan mun dawo gida ban fadawa mamu abinda ya faru dani ba sai yamma ta tsinto maganan a dakin Amma ida su Aisha sukaji a wurin su ikilima yaran hjy maryam suke zancen.
Ran mamu ya baci sosai tace zata canza min makaranta tunda abin yaki ya kare a tsakanin mu sai da Amma tace ta bari Daddy ya dawo zasuyi magana akai.
Ta dawo part din ta ta samay ni ina wa kanne na assigment din su take tambayana may ya hadani dasu salma a school har mukai fada haka ?
Nan dai na kwash komai na fada mata sai naga ta tsura min ido kawai lokacin da nake mata bayanin har na gama sai naji tace ke kan baki biyoni da hakkuri ba hakama mahaifin ki.
Dago kai nayi na kalle ta don jin kalamin ta gare ni tace kwarai da ki barsu ga Allah idan ma sun zageki din ai kansu suka zaga din .
Ita salma tana maki hakane don haddasa wani bala,i a tsakanin mu don su kawo rigiman da Alh zaiji ya tsaneki a gidan nan don su a kullun karshen mu suke son gani a gidan nan.
Daga yau ban son in karaji kinyi fada da wani kan ko may nene ballae wanan dan zagin da hakan yana kan kowa ai kema bada son ranki kike zaune a gidan nasu ba da sunyi hakkuri kwana nawa ne ke mace ce fa kin kara gaba kin bar masu gidan su.
Sannu a hankali mamu ke fahintar dani manufar su salma a kaina wanda ina fahintar ta saida a lokacin kurciya da wauta yasa ba zan gane komai ba don banji zan iya kyalesu suna zagan min iyayye ba a banza su tashi free.