NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

Ta shiga ta fito daki hankalin ta a tashe tana jan tsuki tana magana ita kadai kamar mahaukaciya mama saude ne da abin ya dama tace wai yaya lafiya yau kuwa ?
Tace uhumm bari saude abubuwa ne suke son yi min yawa a kaina yau ta fadi tare da shigewa dakin mama saude ta bita da kada kai tana fadi a ranta mugun nufi yabi mai shi.
Daga gidan su samira mun shiga wurin gida biyar muka dawo gidan su Atika muka yada dandali bayan karfe hudu.
Hankalina yana gida wurin manjo saidai kamar an kashe min jiki da zuwa gidan bayan muyi sallah na kwanta a gurin ina dakilan wayan Atika shiya dauke min hankali na manta da komai dake gabana a lokacin.
Bayan sallah magariba dana isha, kuma na dasa wani kallo ina kallon ci gaban shi hakan ya jani har goma da rabi ban shiga gida ba.
Saida umma ta leko dakin tana fadin nikan yau a gidan nan zaki kwanane dare fa ya somayi sosai take fada min na zabura da sauri ina kallon lokaci a wayan na mike ina fadin yau nasan zan sha fada wurin manjo kan don nace ba zan dade ba da zan fita.
Har cikin gidan mu Atika ta rakoni muka shiga dakin manjo da muka samu har ta kwanta a lokacin sai dai batayi barci ba.
Tana ji mu ta daga tana fadin yaran nan ina kuka shiga haka tun safe kuka fita nace wallahi manjo ina nan gida su Atika muna kallo ne ya dauke mi hankali.
Jin hayaniyar mu ne ya sanarwa umma mun dawo sai gata kofan tana fadin yau ina kuka shige haka yarnan tun safe ?
Umma muna gidan su Atika kallo mukeyi ya dauke muna hankali umma ayi hakkuri don Allah tace hankalinane ya tashi rashin dawowan ku gida har wanan lokacin.
Daga haka ta juya ta fita Atikama tace zata wuce sai manjo ke fadin ni yau bansan wani imani yazowa lami ba don tunda rana take neman ki gidan nan fa.
Kallon juna mukayi da Atika muka bar dakin har muka kai waje ba wanda yai magana sai da muka bar gidan kadan Atika tace yanzu yaya za a yi fatima.
Wanan matar fa da gaske take da nufin ta a kanki nace yaya kuwa Atika addua dai nake ko yaushe Allah ya tsare ni a duk inda na samu kaina.
Mun dan jima muna hira na koma ciki na samu wai miyar kaza umma tayi ta debo min bana nan taba manjo ta aje min.
Ina shigowa manjo tace wanan zuwa kan kinci da fari ga miya nan ummar ku ta kawo maki wai dazun tayi shi tace kinga ni dake gidan ko kashi bata ban ba.
Nace miya kuma tace eh wai kaza aka yanka mata yau shine ta zubo maki ki daure kici kafin ki kwanta.
Na bata rai duk dagabana dake faduwa da Naman nace na koshi bancin abinci da dare kuma ai na fada maki nama bai damay ni ba yanzu.
Kokarin mikewa naga tanayi tare da fadin bari indan taba kada tace ba a ci tayi maki abin arziki tana kokarin jawo kwanon silver dake gabanta.
Da sauri nace manjo kada kici naman na do Allah na fada ciki daure fuskana gare ta.
Wani kallo tayi mun na tuhuma nace manjo barta da halinta kawai tana dauka ban san komai bane da take shiri mun.
Wani abu ke nan kike nufi nace ba dai zakici naman nan ba wallahi naja kwano zuwa baki kofan mu na aje.
Sai kallon mamaki manjo ke mun na share ta ina shitin kwanciya abina ba tare dana kulata ba har na gyara wuri na haye kusa da ita tana zaune tana kallona da mamaki a fuskanta.
Bata iya ce mun komai ba don ba fuska a guna da zatayi min tambaya a lokacin sai da na tabbatar da manjo tayi barci baffa ma har ya shigo naji rufewa part din su na fito a cikin sanda na kai nama waje na zubar dashi can nesa na dawo gidan na kwanta.
Washe gari tunda asuba saiga umma dan dakin kwanon namu ta leko tana fadin babba an tashi lafiya ya dare ?
Lafiya kalau muka tashi manjo ta bata amsa da hakan tace fatima fa yar gidan babba an tashi lafiya ya gajiyan unguwan dai.
Umma ina kwana nace bayan na shafa addu,a a fuskana da jikina na waigo ina gaida ita idon ta na yawo tana neman kwanon naman ta.
Nace umma jiya na dawo na samu miya na gode shi naci na kwanta da guntun bread din daya rage bari in fito in wanke kwanon in kawo maki.
Tace ba sai kin wanke ba indan kinci ai shike nan bukatar maje hajji sallah dama ta duka ta dauki kwanon ta fita.
Kallo mamaki manjo ke mun har lokacin kafin tace A ruwa kaddai ince wanan lami din neman rayuwan ki take yi.
Kusan haka nake hasashe na bata amsa koma may ye ai ya kare a kanta shiru tayi kamar tana nazari na dan wani lokaci .
Wunin ranan sai ban fita ba ko girkin da nake muna sayowa na kira Atika akai muna umma ko taje ta dawo wata kila bokan nata ya fada mata wani abu zai samay ni ne ranan takewa wanan zawaron daga part din su zuwa namu tana dubawa.
Sauran kwanakin daya rage mun kuma sai naga umma ta canza min fuska ba kamar lokacin da take tarkona ba.
Shirin komawa na fara yi tunda akace min kwana hudu zanyi a nan don a yanzu na gaji do akwai tsoro da fargaban tarkon umma a kaina yanzu.
Na bar gidan kawuna ina murna zanzo gidan mu inda yan uwana jini zasu kaunace ni sai gashi nazo naga gidan kawun nawa ma ya fiye min nan kwanciyan hankali a yanzu.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:12 – ????????????: BISSIMILAHI RAMANIN RAHEEM HAS BUNALLAHU WA,NIMAL WAKEEL, , , , , ,

Da kyat na yarda zuwa wurin kumshin da kitson da Atika tace zata kaini don kada na koma hakana gida ban so ba sai dai ba yadda zanyi don ummata da ta saka baki tana fadin kinzo haka ba kumshi kice kuma haka zaki koma.
An min kitso da kumshi wanda hakan ya kara haskani sosai na fito wata shar dani ranan, na koma gwanin ban sha,awa dani.
Ni kaina nasan da nayi kyau matuka a gidan su Atika umma tasa aka wanke mun kaya na almarin su ya gogemun su koda muka dawo mun samu an kawo kayan wurin manjo.
Sai da na dan dade gidan su Atika muna hiran ban kwana nadawo gidn lafiya na shigo gidan Amma ina shiga kaina ya dan fara min ciwon da bansan dalilin sa ba.
Sai dai na dauka duk gajiyan kitsone don banson abinda zai taba min lafiyan kaina ko kadan shiyasa idan muna hutu nayi ba kwana da kitso ke nan sai mun koma school kuma.
Ganin ciwon kan nason ya kaini kwance ne manjo ta fita ta sayo min magani nasha kafin ta dawo ne a dakin ina kwance kawai akaji na yanka wani uban ihu ni kadai.
A cikin razana duk wanda ke gidan baffa a lokacin saida ya fito waje don karan ihun dana yaka din.
Suna tsaye cirko cirko suna son gano mai nakewa ihu haka don su basu masan manjo bata gidan ba a lokacin.
Wani ihun na kara karde hidan dashi da kubura saratu da mama saude suka nufo dakin da gudu don ganin abinda ke wakana da ni a cikin dakin.
Ni dayace a dakin an wani murdeni a lankwsa ni kamar ruboce jikina idanuwana sun wani firfito ga baki daya a lokaci guda.
Innalillahi mama saude ke fadi tare da tambayan ina tsohuwa ta fita ne ko mai ina babba ta shiga ko tana bandaki ne ?
Tana tambaya a kidime hankali tashe babu mai bata amsa don duk su kubura sun dare daga kofan dakin .
Ta juya zuwa bandakin manjo bata ciki haka yasa ta fita a gigice zuwa hanyan kofar gida hankali tashe sukaci karo da manjo da ta dawo dauke da leda maganin da aka hado mata chemist.
Ganin mama saude a kidime yasa manjo tambayan ta ko lafiya mama saude tace babba ba lafiya tafi ce a cikin wani yanayi a daki.
Wani itin rikicewa manjo tayi habkali a tashe suka shigo gidan tare kamar ba itace mai jan kafa ba na ciwo lokacin.
Ga su kubura da saratu cirko cirko da sauran yaran gidan nesa da kofa manjo din dun tsaya.
A ruwa, ke Aruwa lafiya ta fada dakin ganin yanayin da nake ciki yasata kara rikicewa tace ayi maza a kira mata baffana don Allah kada yar mutane ta mutu mata a daki ba a san sanadi ba.
Ganin kamar baffa zai dade baizo ba tace mama saude ta kira mata umma Atika da sauri a gidan su ta tafi don hankalin kowa ya tashi gidan .
Sai umma lami da bata gida itace bata san abinda akeyi ba gida tare da umma da Atika da wata bakuwa da sukayi suka shigo cikin tashin hankalin labarin da mama saude taje masu dashi din nawa.
Wanan karon ina wani abu ne kamar na kutare abar bankare ni din sai kuma abin kutare nake zaka rantse da Allah wata tsohuwar kuturawa ce ni.
Can kuma na juya ina wani marmar da idanuwa kamar wata yar bariki ina wani kwalliya da sauran su bakuwar tace wanan iskace gare ta haka dama ?
Iska kuma yaushe ta samay shi hakan ban sani ba don dai uwarta bata fada min ba gaskiya manjo ke fadi.
Matar tace kuban tsaba idan akwai mama saude tace babu tsaba agidan gaskiya sai umman Atika tace Atika tai maza ta debo gyaro a gidan su.
Bata jima ba sai gata ta dawo da gyaron matar ta fara surkule tana fadin kuke ganin mu bamu ganin ku kuyi hakkuri ku tausaya wa wanan boyar Allah ta huta hakana don Allah.
Abindata saka a baki ta tauna shita furza min a kai har sau uku ta juya tana fadin kunyi ajiyan komai da ruwan ka ko hantiti gidan nan ?
Mama saude tace sai dai babba itace mai yawan sayen sa don kafanta manjo ba baki sai da hannu ta nuna inda yake imani ya kashe ta.
Dauko mu shaka mata da yardan Allah zasu sauka daga kanta insha Allah wanan iskan baya zuwa haka babu dalili dole akwai dai wata a kasa don manyan iska ne a kanta gaskiya.
Kaina ta daga ta shaka min hantitin a cikin hancina wani irin atishawa na sauke lokaci daya tana shaka min komai da ruka din a hanci na.
Sau uku ina sauke atishawa mai karfi kowa ya fara fadin alhamdullahi sun sauka wai sannu fatima ikon Allah wai dama yar nan tana da wa yan nan mutanen a kantane haka ko dai yanzu ta samay su ?
Umman Atika ce ke tambaya manjo da tayi mutuwan zaune bata iya bata amsa a da baki ba sai kai ta kada mata don imani ya kashe ta lokaci guda.
Suka fara jera min sannu ban amsa ba sai can kuma na fashe da wani irun kuka mai cin rai da ban tausayi .
Sunyi kira sunyi kira ban amsa ba sai matar tace wani ne yazo kuma nake gani basu gama takawa a kanta ba ke nan .
Matar tace idan da alheri kuka zo muna maraba daku don Allah kuyi magana musan abinda kuke so ?
Babu amsa har lokacin sai da ta kara fadin fatima kila sun sauka ne wani murya kamar na kato yace ba fatima bace mune .
Ba fatima bace kaine wa sai na ci gaba da kukan tana ta roko maishi yayi magana sai can akace ina ina wanan baiyuyuwa.
Muna kallo a cutawa jinjiran mu daga zuwa zumunci sai kuce zaku cuta mata yau akwai kaniya a gidan nan kaniya kaniya.
Subbahanallahi don Allah kuyi hakkuri ku fadi may kuke so ai maku ku tafi sukace bamu tafiya don tabamu akayi mun dade akan jinjiran mu bamu cuta bamu cutarwa amma ake son halaka muna jinjiran mu.
Ikon Allah manjo tace kun dade kuna tare da ita ya kada kai yana fadin duk inda take muna biye da godiyar mu mu ba masu fitina bane amma yau an taba mu an taba mu.
Haka kawai sai bakina ya dauke kuma dip ba magana ko kadan sai na fara abin kuramay salati umma Atika ta saka tana fadin kurma ke nan yazo kuma ?
A daidai lokacin ne bafa ya shigo a cikin tashin hankali ya samu abinda ke faruwa salati ya fara tambaya yaushe na samu wanan laluran haka ?
Yau dai muka ga wanan laluran gare ta manjo ta bashi amsa sai bayani nakewa matar nan tana bada amsa don da gani ita tasan halin iska can dama.
Ta juya tana masu bayani tana fadin abin da kurma ke fadin yau suna da fada a gidan nan don an daukowa jinjiran su mugun abu.
Matar tana fassara masu abinda kurman ke fadi tana fassara masu abinda yake fadi din hankali tashe.
Manjo tace ni hauwa,u wake bin yar marainiyar Allah nan da mugun nufi haka a rayuwan ta ?
May wanan yarinyar tamai wani har ta tsune masa ido sallaman umma lami data dawo zufa zufa gidan daga unguwa ganin yamma yayi ta dawo kafin ta laga na dare ta fita.
Kamar an tsikare ni na mike zubur na nufi waje ina tafiya kamar gurguwa sai wurin umma nako shake ta take diyan ta su hashim da su kubura suka hau bambarana har baffa sai dai sun kasa kwatar ta daga shakan da nayi mata din.
Gida ya rude da ihu da kuruwan neman agaji da kyat da boni ta samu kanta tana hakin ceton numfashin ta.
Har lokacin ba baki a gare ni sai kwatance a gareni kawai nake iya masu ina nuna ledan baka mai kauri data shigo gidan dashi a hannun ta.
Nan hayaniya ya tashi wasu na fadin tunda na dage ina nuna ledan dole akwai abinda ke cikin ledan ke nan ga umma duk shakan data sha taki sake ledan hannun nata.
Sai da kyat aka kwaci ledan tana wiki wiki da idanuwanta tare da fadin sheri zaki mun daga dswowana ban san hawa ban san sauka ba ki kulla min sheri ?
Sai da naga ana bude ledan na kuta sai gani kasa suuuu na fadi a cikin kasa kwalliyan da nayi duk ya baci wurin turmuzan dana sha.
Da sauri du umman Atika sukayo kaina hankali tashe yayin da baffa da manjo suka tsare ledan da ake budewa da kallon babu komai ciki sai wani abu da aka soke da allura da sauran tarkace itin na surukulle.
Fatima fatima umman su Atika ke kiran sunana na amsa a wahalce kin ganeni umma tace na gyada mata kai to wacece ni na sake kallon ta nace ummace tace sannu.
Na amsa mata suna fadin sun sauka sai sukaji na fashe da wani ihun kuma na tashin hankali nan kuma akayo kaina cikin tashin hankali.
Kamar bebiya nake fadin ba zamu yarda ba sai mun dauki famsa kan macutan godiyan mu kuyi hakkuri tunda kun baiyana komai don Allah ku sauka haka ku bar godiyan ku ta huta.
Ranan dai na sha wahala sosai kafin su sauka nayi barci sosai ban falkaba sai dare mutanen unguwa dama gari sun ji labarin komai daya faru gashi washe gari zan koma idan Allah ya kaimu.
Washe gari haka na tashi jikina ko ina yayi min tsami babu dadi ga kayana ko karasa shiryasu ban yi ba.
Ban iya tashi inyi komai sai manjo ne da Atika suke dan hada mun kayan ina kwance har suka karasa baffa bai fita ba don hankalin shi bai kwanta ba.
Ya shigo dakin ganin shi na yunkura zan tashi yace kwanta abinki gurin babba nazo muyi magana jin haka sai Atika tayi saurin ficewa a dakin.
Daga kofa ya samu wuri ya tsugunna ya sake duban inda nake yana fadin Fatima yaya jikin naki nace da sauki baffa yace zaki ko iya tafiya yau din kamar yadda sukace za a zo a daukeki ?
Zata iya idan ma ba zata iyaba sai mu tafi tare mu ratse mu dauki Adda mu kaita gida muyi masu bayani don ba zamu saketa haka a cikin wanan yanayin ta tafi ita kadai ba.
Ganin Atika ta fita dakin na mike da kyat nabi bayan ta a waje na samay ta zaune na zauna a gurin muna dan hira.
Baffa yace Nima hakan na gani babba tunda dama ga wanan zancen da bamu san ya ake ciki ba ranan jumma,a nima zan shigo kamar yadda nayi masu alkawari zamu zo din nidasu sha,ibu da sauran yan uwa.
Ina ga in zai yuyu da sai ku tafi koda lami ne ko kukai ku uku ke nan kunga a nata bangaren dai anga yan uwa aiko .
Da naso bayan tafiyan tunda yabar kudin motar zuwan ku din a dauki mota wasu mata suje ranan.
Yanzu ma wanan abin zai faru ga wanan al,amarin dayazowa yarinyar nan haka kuma zai yuyu mana wanan ba lalura bane babba taba su akayi shiyasa suka tashi da waya santa dashi.
Amma dai kuma sai naga idan kun bita da yawa kamar zaku bata masu shirin su don ba hakan aka tsara ba da farko.
Amma dai sai yadda kika gani babba tace maganan ka gaskiya ne kawai mu barta ta tafi din Allah zai kare a duk inda take ai manjo tace.
Karshe dai suka aje shawaran abinda zaifi zuwa rana ko sai ga driver yazo har lokacin bamuyi arba da umma lami ba .
Dana shirya zan tafi na shigo har part din su na sallamay su da kyat ta leko mukai sallama ta koma.
Na samu rakiyan yan uguwa da sauran mutane haka motar ya daga raina babu dadi na rabuwa da yan uwa da nayi ko kadan.
Bamu shiga kano ba sai gab da za a fara magariba ina takure a bayan mota ni kadai daga misau zuwa kano ina fada da zazzabi mai karfi a jikina.
Haka muka iso gida babu kowa waje har ya shiga min da kayana part din mu mamu na zaune a falo cikin damuwan rashin isowan mu taga na shigo.
Sai dai yanayi na bata babu lafiya don yadda na shigo falin ina gaida ita cikin makyarkyata na samu dogon kujera na haye na dunkule a wuri daya.
Ikon Allah ba lafiya ne kuma a hanya zazzabi ya kamaki ko tun can ne ban iya magana ba tace bari zo sai wayan ta yai kara tana dauka naji tana fadin sun iso yanzu sai dai gata tadowa ba lafiya kuma.
Nasan da kawu take wayan yana tambaya ko mun dawo a lokacin shine ta fada mai mun dawo din.
Sai bayan an sallamay sallah kawu ya shigo part din kai tsaye yana fadin fatima ba lafiya kuma kika biyo hanya hakana ai da sun barki har kiji sauki.
Mamu tace ina ganin dai a hanya ta kamu da masasaran kila don ba zasu barta ta taso haka ba ki shirya zan turo wani ku tafi asibiti.
Da sauri na dago kai nace kawu a bani magani kawai naji sauki murmushi yayi mamu tace kasanta da tsoron asibiti ruwan ki aike ke wahala a jikin ki ba wani ba.
Bamu dai je asibitin ba tasamun ruwa masu zafi nayi wanka asha tea mai zafi da magani sai na kwanta.
Koda su Amma suka shigo dubana duk nayi barci mai nauyi a lokacin ban san shigowan su dakin ba ma.
Washegari na tashi jikin nawa da dama ya rage min ciwon da nake ji ina son fadawa mamu abinda ya samay ni ina jin tsoron fadamata.
Don ban san halin da zata shiga ba idan taji yasa na kyale na bar maganan a cikina ban fadawa ko Amma da take abokiyar hirana ba.
Na dan daure naje part di Amma don na rage yawan tunanen da nakeyi din a raina muna falon duk dasu Aisha sai hira sukeyi ban saka baki na.
Ga hiran su Aisha tace lalai wata tana kewan gida dan murmushi nayi ban kullata ba sai murja tace wai baki san yadda muka matsu kidawo bane halan .
Yi nayi kamar ban jita ba saida ta dan zungure ni Amma tace kyaleta ai tana jinki tunda ta dawo take da wanan miskilancin haka ko kuma ciwon ne ya sakata haka oho ?
Kamar daga sama naga mutum yayi sallama falon Amma din ya shigo duk sai na tsargu don ban san da zuwan shi ba sai ganin sa nayi yanzu ya shigo.
Gaishe mukeyi kamar bai son amsawa ya dan tsaya hakan yasa muka mike don barin falin mu barshi da Amma.
Hanyar fita na nufa Amma tace tafiya zakiyi kuma bayan baki dade da shigowa ba nace a shagwabe Amma zanje in kwanta ne kaina naji ya fara min ciwo yanzu na juya na suce ba tare dana jira inji abinda zatace ba.
Kasan gida akwai dadi tun jiya data dawo mun rasa gane kanta a gidan nan har yanzu yi yayi kamar bai jita ba tace sadauki anya kuwa zaka iya rike wanan Amanan kuwa ?
Ya dago kai yace Amma kina magana ne tayi mai dakuwa da hannu tana fadin miskilin banza ai kunyi daidai da ita don yanzu tagamauna miskilanci wuri nan

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button