NOVELSSARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL

SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:13 – ????????????: YA AR-RAMANIN AR RAHIM YA HAYYU YA KAIYUMUN, , , , , , ,

Ina shiga part din mu na samu baki a part din mama saude da umman su Atika sai Atika da manjo da Addahna da wasu mutum biyu dana sani a azare.
Ina ganin su na fashe da kuka maimakon farin ciki jikin umman Atika na fada na darji kuka na wanda duk wanda ke falon sai da yai hawaye.
Daya daga cikin kannen manjo da suka zo tare tace ki share hawayen ki yar nan aure ba mutuwa bane abin farin cikine tunda kikaga har munzo murnan haka.
Ya kamata ace farin cikin ganin mu kikayi sai kuma ki aza muna kuka haka maza ki share hawaye ki daina wanan kukan haka.
Yadda tace hakan nayi don yadda take magana umurnine take bani a lokacin haka yasa nayi saurin dakatar da kukan da nakeyi din.
Umma ta dan bugi bayana tana fadin ai saiki saka mu jin ba dadin zuwan mu nan nidakewa Atika fatan samun nasara irin haka har yaushe zaki tsaya kina kuka.
Duk wata uwa yana cikin farin cikin zuciyar ta yau ace ka kai yarka aure haka cikin lumana aike ba karamin sa,an aure kikayi ba yar nan.
Tashi ku shiga ciki da Atika kuci abinci nasan ke take jira ta kasa cin komai tun da muka iso.
Mikewa nayi muka shiga daki nida Atika nan saida mukai kukan mu muka share hawaye muryan Aisha ne ta shigo tana fadin yanzu mai kumshi tazo zamuyi dama ai nace naki yana nan kamar yau akai maki shi.
Saida ta kalli Atika ta dan rage tsawo tana fadin ance kun fita tare da ya Aliyu dazun dana shigo nace gurin photo ya kaini nayi.
Photo kuma wani irin photo ke nan ko kuma harda photo zakuyi ne na amarya da ango wai ?
Ango da uwargida zamuyi ba photo na harareta ina fadi tare da ya Aliyu muka fita ashe haka yake da saukin kai sosai .
Wani dadi taji tana kaiwa zaune tare da fadin don Allah da gaske kikeyi A ruwa ?
Harara na kara aika mata nace a,a a wuta don Allah tafi nama fasa baki labarin ta rungumoni tana fadin haba yar kanwata fada min don Allah yadda kukayi dashi mana.
Yayi maki magana na don Allah ta fada tana tsurenu da idanuwan ta tana son jin amsa daga bakina.
Kai na girgiza mata nace ko daya bai mun maganan ki ba wallahi ya dai bani shawara sosai kuma naji dadin hakan da yai min don ya kwantar min da hankalina kadan.
Rarashi na take wai in dan fada mata abinda yace mun nace ki bari kema zai fada maki ai idan kun hadu.
Hannuna ta kama tana fafin haba yar kanwata kin san fa bamu haka dake a gidan nan keta hannun damanane aru wai fatima.
Na kara hararanta nace ba zaki daina kirana da sunan nan ba ko ?
Bakina ya saba hakan saboda Amma dake yawan kiran sunan kulun nace ni rabu dani don Allah na kashe wanan sunan dai tace naji matar yaya.
Ashe baki son kiji komai ke nan gara ma bakin ki ya saba da kirana da kanwar yaya din zaifi maki sauki.
Ni ba wani abu yace min ba magana kawai yai min akan inda zanje shine ya ban shawara kawai.
Ina fadin haka nakai kwance tace waike ko kina shirin wankin amare da za ayi muna gobe ?
Yi nayi kamar ban jita ba na kyale ina kallon gefen da nake kwance ina tunane a raina.

Suna zaune a dan karamin falin gidan yayan su gidan da hjy su take zaune duk kansu su uku ne a zaune suna fuskantan mahaifiyar tasu da suke zaune ita sisters din ta duka uku.
Tace kundai ji abinda mahaifin ku yai mun ko saboda ku har wanan yar banzan salma zance tafito mu bashi gidan shi taki fitowa.
Ba wanda ya iya magana daga cikin su sai habbib da yakai iya kuluwa da zancen yace.
Amma mama kema kina da laifi gaskiya yau kuke da daddy bai taba cewa ki barmasa gidan shi ba sai kan wanan zancen .
Mun fada maki ki kwantar da hankalin ki tun farko tun abin nan bai kaiga haka ba kinki kwantar da hankalin ki.
Abi abin a sannu cikin hikima da muke shirya kin dai san ba son abin nan muke ba dukan mu muna hakane saboda farin cikin ki.
Amma mama kikaki bin shawaran mu har abin yakai ga muni haka garemu dake don daddy ya hau fiya da yadda kike tsanmani gaskiya.
Yayi ta hawa mana shine may don ya koreta gidan shi akace nufanshin ta aka katse ko may ?
Look mama rabi wanan magana ne tsajanin mu da mahaifiyar mu don ba zamu so wanan abinda ya faru yayi tsauri ba don Allah ina rokon ku idan ba zaku tayamu kwantarwa mahaifiyar da rai akan zancen nan ba kuyi shiru.
Babawo ni zaka fadawa haka ko kin fimu son tane zaka nuna min yau ka tuna uwa daya uba daya suka haifemu don haka ba zaka nuna min son ta ba yanzu.
Kuna son ta aka hada kai daku akai mata waban cin fuskan da yankan kauna wai har kanwarku ne za a dauka a hada da almajirin gidan ku don rainin wayau ?
Please mama ciki hade hannayen shi habbib ne ke magana na rokeki kamar yadda dan uwana ya rokeku ku fitar da bakin ku ga wanan zancen don Allah.
Ba zasu fitar ba ai bansan kunzo nan kuyi muna rasgin kunya bane da kuka koyo a kasan turai.
Karya tafada ba gaskiya bane bakin ku hade da mahaifin naku don a tozartani haba mama ya kamata ki fahince mu yanzu mafa mun zauna da daddy akan maganan nan ya kidaya muna sharudan shi akan in har kince ba zamubi zabin shi ba gare mu a bakin auren ki.
Mama yaya kike son muyi da zuciyar mu wanan abin fa don farin cikin ki muka yarda mukayi shi ba wai son ran mu bane Aliyu ya fada shima rai bace.
Tace haka yace yace kwarai kuwa don mun zauna dashi da baba balarabe ya kara jaddada muna hakan da yamman nan.
Kallon juna sukayi sai hjy rakiya tace ya kamata Alh yai muna uzuri tunda muma muna hakki a kan ku ai.
Musanman salma da akaiwa wanan bakin hadin dakai babawo di yan matar shi cefa yayiwa gata amma mu namu ya bata mata asali.
Habbib ya kalle ta yace kada kuce haka mama don salma tana son mijin ta munyi magana da ita tana son mijin ta.
Kabar wanan zancen wai salma nason mijin ta uwar tace kabar wanan kazamin zancen habbib .
Yace wallahi mama da bakinta ta fada muna da muka zauna da ita bawai mun tursasa mata ta fadi ba.
Kallon juna sukayi kafin uwar tace zanko halaka yar iska idan tace wanan dan almajirin take kauna mutum da naki jinin shi a duniyan nan.
Haba anty ki bar fadin haka don Allah tunda yanzu ya zama surikin ki nifa naga ku bar Alh kawai yayi iko da iyalin shi yadda yake son yi shine saukin mu.
Ki samu ki koma dakin ki don zaman nan ba zai fishe ki ba tun mutane basu farga da hakan ba.
Bazata koma ko ina ba Asmau idan bamu samu sabani dake akan wanan zancen ba a wurin nan may nake ?
An gaya maki kowa irin kine da namiji ke takawa kina kurun don ruwan cikin tsiya nina rasa inda kika kwaso halin nan kamar ba Auta ta haifeki ba.
Ku tashi muje umar daya mike yace da sauran ku tafi mana mai bakin zuciyar tsiya dama nasan bayan ubanka kake ai.
To bari kaji muddin ina raye yar iskan yarinyar nan ba zata shigo min cikin zuri,ana ba .
Amma anty da kin kyale kamar yadda sukace suna bin mahaifin nasu a hankali ne ba a san manufan su ba ai.
Su kan sun fice sun barsu a nan ba wanda yaiwa dan uwa magana daga cikin su har suka shiga motan da suka zo a ciki.
Saida safe hjy keji wai ranan ne tarewan amare don Alh ya aiko ma kawun su da yayan su yace a fada masu yau salma zata tare gidan mijin ta tare da sauran Amare.
Don haka yake sanar dasu idan akwai mutum biyu daga bangaren su da zasuzo da dare akai salma dakin ta.
Yayan nasu ya kare masu bayani hjy tace yasha karya wallahi babu inda salma zata gidan wanan mijin da zuciyar ta bai amince dashi ba.
Yayan nasu yace kinga jummai tashin hankali yanzu ba naki bane zan tafi in samu kawo a gyara zancen nan naku ki koma dakin ki ki kai yarki aure kikuma tari sarakan ki da zasu shigo hannun diyan ki.
Maimakon ta saduda sai kawai tace amma yaya in kun min haka baku min adalci ba sam yadda yake tunanen banda amfani a gidan yanzu ya koreni sai idan yazo da kafan shi zan koma don nasan barazana yakeyi bazai kai mu aure bani gida ba.
Hjy Rabi tace ni dama nasani wanan kamay kamay da yakeyi don dai ta dawone barazane kawai yakeyi .
Nan dai suka kananaye shi da dasin bakin mata har yaji ya gamsu da maganan shi bai neme kawun nasu da sukejin maganan shi ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button