SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL
SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

Ina kwamce dakin mamu inda na mayar gurin zamana a yanzu sai ga mamu ta shigo ta bude wardrobe din ta tana fito da kaya a ciki sabbi an dinka su ta zube saman gado a gefena .
Atika ta tashi ku shiya tana nuna kayan da zan saka a lokacin tare da mata bayanin sauran kayan lokacin da zanyi amfani dasu.
Sannu a hankali gida ya fara cika da mata yan wunin buki ko wani bangare yan uwan iyayyen mu mata ne suka cika shi idan an debe part din hjy da ba wani nata wanda yazo daga mata har mazan su.
Kawu tun safe ya maida salma part din Amma inda dukkan mu muka taru a can nayi mamakin ganin har sunyi karfin hslin gaiyato abokan su sunzo ashe.
Bangare na daga ni sai Atika da Allah ya rufa min asiri tazo muke dan kus kus din mu mu biyu.
Yan uwan kawu birni da kauye sun cika gidan fam sai faman kuskus ake na zancen hjy da bata gidan lokacin.
Karfe biyu akayi mothers daya da wankin amare sai lokacin ne mukaga yan uwan mazajen salma da ikilimi ashe sadiq din shagon kawu ne shima sun dade tare tun yana karami sai dai baikai Ahmed bunkasa ba a wurin.
Amma shima yana da rufin asirin shi gwargwadon hali don sun ginu daga Alh sosai shida Ahmed din yanzu.
Hjy maryam tayi kuka tayi korafi saidai fin karfin yan uwa da iyayye ya hanata motsawa ta saida hali.
Karfe hudu sai ga su mama hadiye sjn shigo suna fadin maza mu shirya kawu yana neman mu a falon shi.
Kusan a tare muka shiga falon bisa jagorancinn Amma mama hadiye mama Atine da matan kawu balarabe sai hjy maryam da mamu Addah da gwaggon Aisha daya.
Kowa ya samu wuri ya zauna yayin da nake manne gurin Amma gwaunin ban tausayi dani kawunan mu suna a duke.
Kawu ya dan dauki lokaci yana rubutu saman fararen envelop guda biyar sai kawu balarabe da kawu mustapha zaune a gefen shi.
Can ya dago kai yana fadin hajiya kunyi hakkuri ina rubutu koda kuka shigo ya fara gaisawa da mutanen wirin kafin ya dora da godiya ga Adda da gwaggon Aisha a karshe.
Ya kira sunan salma da rakiya sai Aisha da ikilima nice ta karshen kira nace na,am kawu ina wuni cikin dakusasshen muryan da ya gaji da kuka lokacin.
Ya amsa da kyat yana kallona tausayi yakeun don dai tausayin nake bashi sai dai ba yadda zaiyi ne don hakan ne mafita a gare mu baki daya.
Yace diyata har yanzu kukan bai kare bane kiyi hakkuri haka musulunci ya gadar damu mu raya sunna a tsakanin mu karfafa zumunta a tsakanin yan uwa musulmai.
Ya kare da kiyi hakkuri kinji na gyada kai kawai ba bakin magana gare ni shashekan kuka nake saukewa a hankali daga inda nake zaune.
Dago kai yayi ya kallemu dukan mu yace da farko zan fara da godiya da Allah ya nuna muna wanan ranan mai albarka ranan da ya nufa a cikin kudin tarihin ku zamu kaiku gidan mazajen ku lafiya.
Nasiha yayi muna mai kashe jikin bawa a gurin yayin da falon yayi tsit ga baki daya na dan wani lokaci ana sauraren shi.
Ya kare yana saka muna albarka tare da fatan zaman lafiya a tsakanin mu da mazajen namu yace a tsarin su ba zancen saki ko yaji a gidan nan din haka kowa yaje ya zauna lafiya da mijin shi.
Salma ya kalla yana miko mata envelop dake dauke da sunnanta tare da fadin wanan sadakin ki ne hannkin ki ne don haka muka yanke shawaran bawa kowan ku ga hannun ta don sadaki ba abin wasa bane.
Haka yai ta kiran mu daya bayan daya yana mika muna envelop din dake tare a gaban shi wanda muka samu yana rubutu a kai.
Bayan ya gama bamu ne yace yanzu sai ku shiya ga balarabe ga mustapha da gwaggonin ku zamu kaiku dakunan ku kfin yamma ya karayi.
Ke fatima ina ganin gobe zaku bar kasan nan ko zuwa jibi da fatan zakiyi amfani da tarbiyan da muka doraku akai.
Kada kikaga bamu kusa ki dauki wani tarbiyan daba namu ba ki dorawa kanki a can.
Shigan ki gidan dan uwanki yana nufin wani haskene a rayuwan shi daya manta a baya ke zakiyi kokarin dawo muna da akidun mu da al,adun mu a acikin zurian shi.
Don haka ashe aikine babba ja a gaban ki aka doraki kiyi ba kamar sauran da su mazajen su basu cunkushe da wasu al,adun a gidajen su ba.
Kawu balarabe ya karbe da fadin kindai san wanan kafiran matar tashi sai kin ture wasu al,adu nata kada ki yarda al,adunta yayi tasiri a gare ku ko kadan kiyi kokarin kafa naki akidan addin nin a zukatan duk na tare daku.
Kibi mijin ki sauda kafa yinayi bari na bari sai a zauna lafiya a tsakanin ku kuka mai tsuma rai nakara fashewa dashi a wurin saida naba kowa dake gurin tausayi Amma ma kukan ta fara tana fadin ko zaku barta gida ta kwana biyu alabashin daga baya idan yazo sai su tafi.
Kunga ko yanzu ba lafiyane a jikin ta ba a hakan kuke tunanen kaita cikin wanan halin ?
Dan murmushi kawu Alh ya sake yayi da kawu balarabe yace haba babba mai zaisa a barta gida bayan mijin ta yana gari ?
Daga haka kowa na falon ya shiga yi muna nasiha kawu yace mu tashi mu shiga muyi bankwana da iyayyen mu su bamu mintuna talatin a fito.
Kowa ya tashi a guri mamu na zaune kanta a duke tana zubar da hawaye a fuskan ta kawu mustapha yace kiyi hakkuri maimuna tashi kije kuyi sallama da yar ki ko ina take Allah ya tsare muna ita.
Kuka nake darza sosai a part din mamu saman jikin manjo mamjo din tana tayani .
Haka mamu ta shigo ta samay mu da bata kukan ana bata hakkuri sosai takardan hannuna na miko mata wanda kawu ya bamu tace dashi zaki sayadi hakkin kine a cikin sa.
Kaina gyada nace mamu ki aje a wurin ki tunda va abinda dashi a can ki karba Addah tace don kada ya salwance a wurin ta .
Basu tsaya jiran komai ba ko kebewa bamu samu yi da mamu ba haka su mama hadiye suka shigo suna fadin wai in fito kowa na waje ni ake jira.
Kukan da nakeyi naba kowa tausayi mota na samu a bude kawu balarabe ne maija kawu Alh yana zaune a gefen shi.
Amaren na zaune baya jeep din dukkan su sai kuka sukeyi kawu mustapha yana jan dayan motan dasu gwaggo Addah ke ciki harda su mamu da Hjy maryam su kawu sunce sufito su rakamu dakunan mu.
Aka dauki hanya damu zuwa gidanjen mazan mu sai fatan alheri a gare mu ga sauran mutanen da aka bari basu je ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:13 – ????????????: EID MUBARAK YAN UWA ALLAH YA MAIMAITA MUNA NA BADIN BADADA AMIN, , , , , ,
Allah sarki rayuwa aure yakin mata gishinkin rayuwan mace muna kallo abinda bamu taba kawowa a ran mu ba yau ya faru damu wai gidan aure za,a kaimu wanan fitan da mukayi gida.
Gidan salma aka fara zuwa nan muka samu gidan a cike da yan uwan Ahmed da sukazo daga garin su can jahar katsina.
Daga gidan salma sai gidan Rakiya gidan yana rufe babu kowa daga bangaren hjy ko Alh do bukin ba tsari akayi shi duk yan uwa nacan gidan kawu Alh.
Itama dai an mata nasiha sosai muka fito zuwa gidan Ikilima yan uwan sadiq sundan cika gidan daga jahar sokoto dama abokan arzikin shi.
Sai gidan Aisha inda muka samu yana gida da wasu abokan shi mutum uku bamu fita ba hjy Asmau tazo da kawayen ta da matan kawun su suna bada hakkuri .
Mun fito tare dasu ana raha sukace zasu riga isa gidan umar kada acisu tara hakan akayi don sun rigamu isa gidan.
Su suka tare mu ina jin mota ya tsaya na kara makalewa a jikin Addah ina rusa kuka haka Addah ta rikeni muka fito daga cikin motan.
Ta dan tsaya dani tana rada min a kunnena abinda zan karanto bissimilah kafa goma sha uku sai falaki da nasi da kulhuwallahu uku uku kowa harsu kawu aka tsaya daga kofa.
Muna shiga ina jin mutane na fadin masha Allah gida yayi kyau kusan duk gidajen sun fadi hakan bawai a nawa kawai suke fada ba.
Kawu ya riko hannu na yana fadin ina part din yata din yake aka nuna mai har dakin suka kaini su uku dashi sai kawu balarabe da Addah.
Ya zaunar dani saman gado tare da dafa kaina yana jero min addu,oi suna amsawa da amin yakare ya dan bubuga min baya yana fadin inyi shiru insha Allahu wanan auren zai zamo min alheri a rayuwana.
Zai wuce na riko hannun shi ina kuka tare da fadin kawu kada kutafi ku barni don Allah kawu yaya umar ba sona yakw ba dukana zasu dinga yi don Allah kawu kada ku wuce ku barni a gidan nan da kyat ya iya bambare hannun shi daga nawa yana share hawaye shima.
Nace wayo Addah na Addah kada ki tafi ki barni kema Addah mutuwa zanyi wallahi idan kin tafi kin barni.
Itama kukan ta fito tanayi kamar yadda kawu ya fito yana sharan kwalla a gaban jamma,a itama haka tafito hakan yasa masu saurin kuka yin kuka a lokacin.
Suka fice suka barni sai su hjy Asmau da yan uwansu da kawayen ta a gidan.