SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL
SARKA COMPLETE HAUSA NOVEL BY ZAINAB IDRIS MAKAWA

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:25 – ????????????: BISSMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AMINN YA ALLAH,
GA MASU BUKATAN LAYINA ZASU IYA KIRA TA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 08036959257 DON TURA KUDI KUMA ZAKU IYA SAKA KATIN KIRA KO TA ACC NOBA KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK NAGODE DA KULAWAN KU.
Ki sani shi hakki kona haramun ne kamar yadda wasu ke fadi hakki daine, don Allah mu kula yan uwa .
Tunda na samu naja kafata zuwa daki da kyat ban kara fitowa falon ba ina kwance ina faman tunane ga ba wanda zan iya fadawa wanan halin da muke ciki.
Wani bangare na zuciyana yana bani in sulale kafin sakin ya biyo baya in koma gida da kaina inyaso ya kawo min takardan nawa a gida.
Ba irin shawaran da banyi ba a lokacin har rana tayi lokacin sallah yayi nayi sallah ina kwance ina abu daya a da(kina har lokacin bancin ma manufa ba saidai ina ga shawaran in gudu in koma gida har lokacin.
Tambayan kaina nayi ta yaya zan iya guduwa bayan banga visa dina ba tun lokacin da muka sauka a kasan ya karba daga hannuna.
Sai bayan sallah la,asar ya shigo dakin ina kwance rub da ciki saidai ba barci nakeyi ba a lokacin.
A hankali ya karasa shigowa dakin yana kallona don jin shigowan shi dakin baisa na dago daga yadda nake kwamce ba a lokacin.
Zarah kinyi sallah kuwa ko kina nan kwance kina tunanen banza tun dazun idona da ya cika da kwalla na dago kai ina kallon shi dasu nace ciki ciki nayi dazun.
Zama yayi bakin gadon yana kallona cikin yanayin tausayi daya san maganan da mama zatai mashi ke da yabarni natashi kamar yadda nayi niyaryi da farko da banji abinda zai daga mim hakalina ba yace a zuciyar shi.
Ki tashi muje falo kayana da na sayo danaje china sun iso akwai kayan dana sayo maki a ciki ko zasuyi maki kyau ban sani ba.
Bandago na kalleshi ba ina daga inda nake kwance a raina nace shike nan ta faru ta kare har ya soma min shirin zuwa gida ke nan ashe ?
Ganin ban motsaba yace zarah ke nan badai maganan mama ce ya tayar maki da hankalin ki haka ?
Zarah kin fara sona har hakane yanzu baki son kiji ance za a rabamu ko mai da har kika shiga tashin hankali hakan.
Da sauri don ya fahince ni nace dole ne yaya ya sake kallona a cikin yanayin tausayawa a gareni yace mama bata sani bane ai komawan ki gida yana daidai da komawan ta nasu gidan itama.
Bayan hakan ku zarah sai naga yadan girgiza kai kafin yace idan nace maki yanzu babu mai iya rabani dake zaki gamsu da magana ta kuwa ?
Da sauri don in kwantar mai da hankali kamar yadda naga yana kokarin yi shima nace mai zai hana yaya in yarda da kai tunda ban gaka da mugun hali ko kadan a rayuwan ka da zaka iya cutana sai naga yayi dan murmushi ya sake kalloni ya gyada kanshi da alama ya gamsu da maganata.
Ke nan zaki daure da duk wani halin da mahaifiyata zata nuna maki na kiyayya nan gaba ?
Nace nima ai mama mahaifiyatace koda ban aure ka ba yaya yanzun ma zafin kishin mamune ya shafeni ai har take jin bata sona a tare dakai.
Naga ya saki wani laulausan murmushi a fuskanshi yayin da hannayen shi ke dunkule a wuri daya yana dan buga kafan shi daya a kasa.
Zarah ke nan kin dai iya magana kamar wata babban mace to wai in tambayeki zarah shin kinsan taba noticing mai kalman aure yake nufi a wurin ma aurata ?
A daidai lokacin na mike zaune daga kwancen da nake ina bashi amsan duk wani magana da mukeyi sai da nadan yi murmushi nace .
Nace yaya ke na indai zaman auren kowa wace mace zatayi dace da namiji kamar ka to ina ganin kaman mata sun gama dace maza da jin dadin aure.
Don baka rageni da komai ba na rayuwa yaya kana ban cida sha ga sutura maikyau sai wanda na zaba zan saka uwa uba ga karatu inayi babu matsala ko kadan a cikin sa babu kyashi ko hattara a zaman mu.
Sai nake ganin indai auren namiji ne kamar ka babu wace tafini dace da aure wanan zamanin kaf a duniyan nan.
Dadin zancena ya kamashi ya jawoni zuwa jikin shi tare da dan bubuga min baya yana fadin nima ina alfahari dake zarah taso muje falo kiga kayan dana sayo maki idan zasuyi maki in basuyi ba sai in sayo maki wasu a nan don kinsan wani sati zaku fara shiga school.
KANO NIGERIA.
Murjanatu ce tsaye a bakin famfon waje na kofan part din su tana wanki don ko wani part akwai famfon a kofan wurin do laluran waje.
Ganin yadda hjy maryam ke dan waige waige zata shiga part din yasa tasan ba alheri zata kullawa ba a lokacin.
Samun kanta tayi da bin bayan ta ta window gefen dakin hjy jummai dake bude ta labe tana sauraren su.
A daidai lokacin da hjy jummai ke fadin ai na fada maki yadda suka kona muna mai a gidan nan sai na konawa ko wanin kaf rai agidan nan fiye da nasu.
Nayi waya da babawo da safen nace ya sako masu yar iskan diyan su yasata jirgi da takardan ta ya turo ta gida karatun da yake fadi tanayi ban yarda koshi ta karasa ba.
Da sauri murja ta dafe kirji tana fadin na shiga uku A ruwa kena za,a sako kowa da sauri tabar wurin jin yadda suke faman aiban tani da mamu.
Kayan ta tataro ta nufi part din su Amma da mama hadiye dake zaune suka kalleta bayan ganin ta da himin kayan da ta fita dashi don wankewa ta dawo dashi kuma.
Ke dai malalaciyace kin kuma kasa wanke kayan ki dawo dashine hakana sai kinjera kina sawa sun kare, daga baya ki dawo ki damay mu da korafi kuma.
Murja batai magana ba sai da ta mayar kayan daki su ta dawo ta zauna jiki ba karfi tayi shiru tana tunane haka yasa uwar ta farga da halin da take ciki a lokacin.
Kasa daurewa mama tayi abin da da mahaifi tace wai yana ganki kin dawo haka jiki ba kwari kuma kamar wace tayi gamo kuma data fita.
Kallon Amma tayi tana fadin Amma Allah yayi gaskiya daya hana lebe a rayuwan bawan shi don mutum zai iya jiwo kanshi ranan mutuwa shi a bakin wani.
Labe kika fara yar nan wallahi amma labe nayi na jiyowa kaina abi tashin hankalin da ban taba jiba yau.
Aiko baki kyautawa kanki ba ga maryam nan har girmanta ya zama mata cuta har yaran ta komai mutum yace sai yaji ko sai ya gani ya hana zuciyar shakat dagangan da gangan.
Wai ma may ki jiyo kinzo muna hankali a tashe haka kamar wani ya aikeki yin mugun abu ?
Wallahi mama ruwan famfon mu nai fita da sauri nace barin tafi shiyan hjy intara sai in kawo inda nake wanki din.
Sai ga hjy maryam da saurin ta zata shiga part din hjyn su salma har tana tuntube wurin sauri shine naji zuciyana bata yarda da ita ba lokacin sai na matsa bakin windon ina sauraren su mama kinsan abinda najikuwa ta fada tana kallin mama.
Sai kin fada uwar labe mu ina zamu sani tunda bamu aikeki ba kiyi labe.
Umhumm mama labena kila yai rana Allah dai ya yafe mun wallahi ji nayi suna fadin wai hjy su salma tasa ya Umar ya sako A ruwa ya turo jirgi da takardan tana saki kada ya hado ta da komai yadda sukaji zafin abinda kawo yai mata suma nan suji shi kamar su.
Taci gaba da fada masu sauran maganganun da taji suna fadi a kaina da mahaifiyata a lokacin.
Abu ga tsufa hankalin Amma in yai dubu ya tashi nan ta shiga sake salalami sai da mama hadiye ta taushe ta.
Kada su bari a san an gane wanan magana zata kira mamu yanzu ta tambaye ta layina nacan akan zasu kirani suji lafiyata daga nan sai suji mai ke gudana a tsakanin mu.
Amma kafin nan murja karbi kudi ki sayo mun kati don kiran kasar waje saida kudi mai yawa a layi.
Ta cire dubu daya ta mikawa murja ta fice da sauri a daidai lokacin hjy maryam ta fito daga part din hjyn su salma a cikin fara,an ta.
Murja tace munafuka mun daiji shirin ku bake kadai kika iya wanan laben ba muguwa kinsani yin abinda Allah ya hana yau.
Mamu mama ta kira a waya tana son layina don Allah mamu sai bata turo mata ba kamar yadda tace saida ta gama hadaw yara abincin bayan ta gama na kawu da yake ci ta nufo part din da kanta.
A daidai lokacin kuma murja ta dawo daga sayen katin dataje ta samu mai shagon ya rufe ya tafi sallah.
Maimakon mamu ta tafi sai ta zauna suna hira da Amma wace bata cikin hayacinta abuga wanda kasan halin sa take tambaya gwaggo wani abu ke damun kine ?
Da sauri mama tace mutumiyar dai nata take son jin muryan ta yau da ita ta tashi a rai shine zan kira mata ita ko hankalin ta zai kwanta.
Murja ta gama loda kudin a waya ta miko ma mahaifiyar nata wayan ta kira layin nawa akai dace ko kiran ya shiga.
A daidai lokacin da muna zaune muna cin abincin daren daya tursasa min cin shi don dole ya kafeni da idanu kuma.
Wayan na ringin ban kula in dauka ba yai min alama in dauki wayan da idanu nakai hannu na dauka a hankali.
Gani bakuwar nombane na bata fuskana tare da fadin ban san mai lauin nan ba saidai daga nageria ne kiran.
Yace dauki mana kiji ko waye kika sani ko daga gidane aka kiraki nayi received din kiran daidai lokacin danaji muryan murja na tambayan ya shiga ?
Fatima naji murya mama ta ambata da sauri na amsa da na,am ina wuni tace lafiya kalau sai na danyi shiru tace kin gane dawa kike magana nace a,a bangane ba.
Yana zaune ya kuramin ido yana saurarena tace mamanki hadiye ne da sauri nace lah mama kece ashe ?
Ina Amma dasu mamu ya murja da sauran mutanen gida tace kowa lafiya yake nan yaushe zamu ganki halan sai na dan kalli inda yaya yake zaune nace yaya yace sai na gama karatuna zanzo gida.
Ai hakan nada kyau kinga lokacin da jikokin mu zaki zo muna ke nan na danyi dariya cikin kunya nace kai mama wasu jikoki kuma.
Na katse zancen da fadin ina Amma a bata waya don Allah inj muryan ta ina nan na cika da kewan ta ina jin suna dariyata ta mikawa Amma wayan.
A ruwa kuna lafiya ko nace Amma zamu bata idan kina kirana da wanan sunan har yanzu fa tace to yar nema kin canza sunane daga wanda muka sani da farko nace kada ki bari mijina ya jiki kina batawa matar shi suna da wani aruwa can ?
Tace ja,ira har yanzu dai halin na nan har kike kiran mijin ki a gaba shi sadaukin bai fada maki bayana kuke ba kaf matan nasa .
Muryan mujane ke fadin miss you Aruwa nace a wuta dai yar iska ya labarine sai Amma tace ke A ruwa kina jina nace ina jinki Amma.
Tace badai lafiya kuke ba nace lafiya kalau amma babu wani matsala a zaman naku dai ko nace babu komai sai alheri Amma.
Bansan lokacin da yadago ba sai ji nayi ya karbe wayan a hannu na yana fadin to yar leken asiri muna nan lafiya may kike son ji kuma.
Ta danyi dariya naji muryan ta tar a kunnuwa na saida na lumshe idona don kewanta danaji a lokacin naji yayi shiru yana sauraren abinda take fadi.
Yanayin fuskanshi ya baci can naji yace Amma wani abu ya faru ne da kike fadin haka shiru nayi ina sauraren su tare da canza yanayin fuskana a lokacin.
Saida ya gama yace kashe wayan zan kiraki muyi magana a natse ina wayan ki na nan tace bata da waya yanzu ya lalace kasan kuma mahaufin ku ta kansa yake yanzu kada ki damu za a kawo maki waya yau din nan yace mata ya kashe wayan ban karasa magana dasu ba na dago na kalleshi fuska da mamaki.
Ya zauna a hankali ya kalleni kafin yace kin kira wanine kin fada masa wani magana ?
Da mamaki nace harga Allah ban kira kowa ba ko mamu da muke waya munkai sati bamuyi waya da ita ba.
Yace dole wani yasan umurnin da hjy ta bani a gamay dake maganan Amma yanzu ya danganta da wanan magana sak.
Anyway barin kira nasir ya kawo mata waya zan kirata an jima muyi magana sai dai ina son ki da rike sirin mu a tsakanin mu na sake fadin wallah Allah banyi waya da kowa a gida ba ka duba wayata ka gani mana.
Karshe ma haushi naji har ya fita ban sake magana ba naga ya dade bai shigo na mike na shige har nayi kamar in kwanta a dakina sai naga in nayi hakan banyi daidai ba duk kokarin shi na ganin ya inganta min rayuwan da yakeyi din ta fanni tunda ba haka mahaifiyar shi ke so ba a nata bangaren.
Can cikin barci nake tsinkayo muryan shi yana waya Amma na fada maki ku kwantar da hankalin ku don Allah babu abinda zai samu aurena matata.
Wanan kada ya tayat maki da hankalin ki don Allah idona na bude tar ina jin yadda suke maganan karshe dai Amma nata saka mai albarka sukai sallama ya kashe wayan .
Ke zarah na amsa ciki ciki yace wai fushin may kike hakane ni banyi hushi ba tunda ni ke zargin ki da rashin addana sirin mu sai ke yanzu amma ta fada min komai jinsu sukayi suna kitsawa da hjy maryam.
Ni ai dama ba fushi nakeyi ba na bashi amsa yace may kikeyi in ba fushi ba kina jin na shigo amma kika kyaleni tun dazun ban son irin haka koda kuwa mun samu sabani ne a tsakani mu dake.
Gane cewa danayi hankalin kowa yana a kanmu ashe kamar auren mu yafi na kowa rikicewa ne kuma ga yadda shi yake kokarin kwantar wa kowa da hankali yasa nayi danmaran bin mijina sau da kafa a zauna lafiya kamar yadda kowa ke bukatan hakan a tare damu.
Wanan ke nan haka yasa shakuwa da kaunar dani dashi duk muke a sabon shiga don ba rayuwan aure irin na malam baushe yasan dashi ba irin wanda mukeyi a yanzu kuma muke fatan kafawa a gidan mu nan gaba in Allah ya nufa muna raye.
A wanan lokacin da hjyn su ke zuba ido taga dawowanane gida kuma salma suka samu matsala da Ahmed inda yai mata dukan tsiya ya korota gida a wani safiyan.
Wanda hakan ya dagawa hjy jummai hankali sosai don a daidai lokacin da take gani fa,idan auren Ahmed din da salma tayi a lokacin ne kuma aka samu matsala mai karfi a tsakanin su.
Don hjy tasha tambayan shi kudi ya turo mata ta account din ta dayaga abin ba zai fishe shi ba ya daina koda sun roke shi din sai ta tura salma na zaran mata idan ya shigo da kudin shago kafin su kai banki.
Ganin zata kashi a kunya ranan ya shigo da kudi sunyi dare bai samu kaiwa banki ba sai ta zare dubu hamsin a ciki.
Washe gari da ya tursasa ta ta fito da kudin tace ba ita ta dauka ba inda ya matsa mata taki fitarwa ya bata wa,adin kafin ya dawo ta tabbatar da ta aje mai kudin shi a inda ta dauka din.
Saida ya fita ta kira uwar tana sheda mata abinda ya faru nan ta hau diyar da fada yaya akayi har ta bari ya gane tana zara .
Tace hjy bafa darin da kikace in dauka ba na diba hamsin kawai na diba kuma saida ya gane na taba kudin.
Hjy tace kaji dan kawai yo kudin na waye da zai hanaki taba kudin uban ki ina nashi shi wahalan banzane nasa a ciki don dole ya baku dukiyan ku a karshe a raba maku bayan ya gama wahala daku.
Hjy amma dai da kibari in mayar mai da kudin shi don yayi fushin haka sosai wallahi tace na fada maki ba za,a mayar ba duk abinda zaiyi yaje yayi.
Da Ahmed din ya dawo ya samu bata mayar mai da kudin ba shine yai mata duka ya kuma amshe yarsu dake shan nono a lokacin yace kada tasha nonon sata.
Ya turo salma gida da sasafe yace taje gida ta fadi halin da take mashi da bakin ta .
Salma ta dawo da kukan ta da yawa na gidan sunga shigan ta a cikin wani yanayi tunda safe haka .
Ran hjy jummai ya baci sosai da dukan da yaiwa salma hakan yasa ta samu kawu a falon shi tana fada wai kamar Ahmed don a wullakanta mata ya anbashi zai mata duka irin haka.
Har ta gama kawu baice mata komai ba ta gaji da bambami ta fita a lokacin ya kira mamu yace ta kira mai mama da gwaggon ta Amma ke nan.
Bayanta dawo ne ya tura dan wajen hjy din autan su yaya Umar ya kira mashi salma a part din su don ko da yaushe yaron yana lake da mahaifin su.
Bayan sun zo sun zauna ne ya kalli salma yace uwata sai naji wani labari kuma da banji dadin shi ba duk da nasan halin Ahmed tun farko amma baka shedan mutum yanzu.
May ya kawo wanan dukan haka har kuma ya koro ki gida da safen na ya karbe yarshi cikin kwanciyan hankali yake mata tambayan.
Salma jin yayi shiru ta dago kai a hankali ta kalli mahaifin nata tace a cikin kuka daddy ka gafarce ni ya Ahmed yana da gaskiya.
A daidai lokacinb lokacin hjy ta fado dakin tana fadin ni bansan abinda yasa ba a bani yancina yanzu a gidan nan matsalan kowa zai taso ayi shi asiran ce amma idan yazo kaina sai kowa ya gama sanin komai.
Ki fada min nan waye bare a gurin nan yanzu mahaifiyata da ta kawo ni duniya ko yar uwar haihuwata abokiyar shawarata ko bana raye zata kula da abinda na haifa.
Kallon inda suke zaune ta danyi ta yatsune fuska kafin tace nidai bana jin dadin hakan don ba haka akewa kowa ba bai kulata ba ya juya wurin salma yana fadin ina jinki uwata .
Ganin ma haifiyar ta a zaune yasa ta kasa fadin abinda tayi niyar fada din a lokaci sai kukan da takeyi.
Waya ya dauka ya kira Ahmed yace gashi tafe an dan jima sai gashi ya shigo da sallaman shi yana rungumay da yarsu a kafadan shi da alaman yarinyar tasha kuka na rashin uwar tane.
Ya gaida su a jam,i ya dago kai ya kalli Alh yace gani Alh yace eh na kiraka ne don naga uwata ta dawo gida ga duka ga ka kuma ka karbe mata ya da wani zataji wanan hukunci yayi tsauri sosai mana mlm Ahmed ?
Dan dukar da kai yayi kasa yayin da hjy daga gefe take sake mai magana a fakaice ya dai girgiza kai yace Alh ka gafarce ni dole nayi wa salma wanan danyen hukunci don tana gap da sakani a kunya idan banyi hankali ba Alh.
Kunya kan ai kariga da kaji shi tunda har kake iya dukan ta kan abinta don baka da ta ido hjy tace daga gefe.
Hannu kawu ya daga mata tare da fadin jummai banson i kara jin maganan ki a nan gurin don ban gaiyato ki ba kin sani.
Ya juya wurin Ahmed din yace ins jinka malam Ahmed sai Ahmed din ya dan gyara zama yana gyarawa yarinyar kwanciya ajikin shi mama hadiye tace miko tana aida farko naki karban ta ne don da baifi da ba ni ka linkidawa nawa yar duka zan lalashi naka yace dolene gwaggo in duki salma.
Yana mika ma ta yar yake magana a lokacin, muna jinka Amma dake gefe a kule ta fada eh kaka wallahi salma gata nan ba a binda ta nema a gurina ta rasa.
Koda banda halin shi a lokacin zanyi kokari inga na saya mata daga baya sai dai tun lokacin da naga suna son jefani a cikin wani rikici ita da hjyn su na fara canza mata a karshe da sukaga na sauya hali sai kuma ta koma zaran kudi shago idan na shigo gidan dashi.
Sadiq ya ban shawara in dinga kirgawa tunda ina zargin ana tabawa nakoyi hakan sai gashi na samu ta zare dubu hamsin a ciki daga safiya zuwa washe garin jiya.
Innalillahi kawu yace salma yashe kika fara haka a ina kika koyi wanan halin mara kyau dole ko nine ylin karbe ya yata ka kyata min da baka koro muna ita gida ba kawai saida sheda halin da kai mata don nima da ina da karfi da yau na karamata akan wanda kai mata.
Ya juya wuri hjy yace jimmai kinga abinda kikaja wa yarki ko har kikazo nan kina fadan karya da gangan dama daji nasan kece da matsalan komai donma mlm Ahmed ya saya wani abin bai fada duka na ke nan.
Yes nasan ka saya duk wanda yaji bayanin ka kuma yai nazarin sa zai sanda hakan ka saya maganan don kawaici.
Yanzu ga yarki nan ba zan bashi hakkuri don ya mayar da ita dakin ta tunda bansan lokacin da kika koya mata yin hakan ba.
Dama ba inda zata koma tunda banda duka har kazafin sata yai mata kuma salma naji haka tasa kuka tana fadin daddy ka bashi hakkuri na daina dama mamace ta dorani a hakan don Allah daddy kada kai fushi dani ina son mijina wallahi na daina daga yau din nan.
Ke tafi can albasa batayo halin ruwa ba wallahi akan namiji namijin ma wanda keci a karkashin mahaifin ki har zaki zauna kina wanan kukan haka ?
Ke ya isa haka mara kunyar banza kawai dama haka Allah yake sakamakon shi idan kace ruwan wani baya tafasa kai naka ko dumi baiyi.
Kinso a sako yar mutane ai mata wullakacin da ba ita keda laifi a kanshi ba sai Allah yaki ta taki aka koro maki yarki gida da mugun sheda.
Mai yafi haka zafi da akaiwa yarki jimmai har don baki da kunya kike budan baki kike fadan magana hakan nan ke kan bansan lokacin da hankali zaixo maki ba wallahi.
Mutum da riko kamar jikan fir,auna haka a,a hajiya may ye laifina a cikin zancen nan da har kike laka min wani zance da ban sani ba can inma nace a sako wata ai danane ko ba dan wani ba kowa yayi iko da nasa dai.
Tana fadi haka ta tashi tafita daga falon kallo Amma kawu yayi yana fadin da alama dai tayi wani abin kuma aka boye min Amma ta mike tana fadin tana fasawa ne ita kasan mai hali baya barin halinsa ai.
Ta kalli Ahmed dake zaune tace kaga jikana kayi hakkuri idan tana da hankali wanan ya isheta ishara ai.
Babu komai kaka kamar yadda yake kiranta komai ya wuce tunda ta gane laifin ta kawu ya kalleta yace ina kudin da kika daukar mai salma ?
A hankali ta dago kai tana fadin naba mama da nazo dama ita tace tana son kudin .
Ya girgiza kai tare da fadin kin gani uwarki zata kashe maki auren ki salma naku bai hadaki fada da mijin ki ba gashi ta turaki yin abinda ba daidai ba.
Kada ki kara haka na rokeki kiji uwata wanan ba tarbiyan zuri,an mu bace ko kadan sai ya dukar da kanshi kasa don bakin cikin da yake ji a lokacin.
Abin gulma ya samu a babban gida irin wanan nan danan maganan ya fara yaduwa a gidan kowa na fadan albarkaci bakin sa.
Alh bai kara bin ta kowa ba saida aka kwana biyu har salma ta koma dakin ta a lokacin shi da kanshi ya mayar da ita yaba Ahmed hakkuri kan abinda tayi mai.
Ya samu hjy jummai har dakin ta bayan ya dawo daga kaita din suna zaune da Nafisa a falo suna kallo da dan autanta dake kwance saman kujera yana karatu yana kallo.
Shigowan mahaifin nasu yasa yara tashi bayan sun gaida shi ya samu wuri ya zauna da kyat hjy dake zaune ta zubamai ido don tsan magana ya shigo dashi wurin ta.
Ya danyi shiru yana kada sandar hannun shi kafin yace jimmai guri ki nazo yau sai dai magana nake son yi dake na karshe a kan diyana.
Ina sauraren ka tace yace haka na da kyau yanzu kinga abinda nake gudu har yakai ga diyana ko halin da kike min a gidan ina daga maki kafa don ba girman ki bane yin hakan.
Yau gashi kin koyawa yarki zatayi magana ya daga mata hannu yace dakata in gama magana ta.
Yanzu ke dadin kine mijin salma ya kawo karanta gidan nan karan ma akan sata jimmai satan kuma ma da hannun ki a ciki don salma ta fada muna rana kudi data dauka nasa yana hunnun ki ta baki do ke kika turata ta daukar maki.
Ita salma ta fada maku haka ita salman tace ni tabawa kudin kaga Alh idan wani sheri kake nema ka lakamin ka fito fili ka fada zaifi.
Ba sheri a ciki maganan nan idan nayi maki sheri in karu damay kina uwar yayana damay zai karani dashi.
Kin san dai muyi haka dake a shekarun baya har kika koma gida irin haka tun kan a haifi ita kanta salma di ko kin mantane ya fada yana tsure ta da idanuwan shi da sukai ja tsantsan bacin rai a fuskan shi.
Ina kin tuna hakan yanzu yau kuma ga yata zaki koyawa wanan halin jimmai ya fada yana kada kanshi.
Yau ko yar rikon gidana akace tana wanan halin ba zan yafe mata balle ace yar cikina ne tayi hakan.
Shin kin san abinda yasa na kyale salma ban dauki mataki ba akan maganan nan ?
Don zafin ciwon da kike dauka ya yi min illa baikai yadda kike zato ba jimmmai duk kika karbi girki tun kwancina ciwo kada ki dauka don ban taba magana bane dan kudaden da nake ajewa gidan nan da wanda nake samu bana gane kansu sai ranan Allah ya nuna min kina dauka a zaton ki ko nayi barci ne saidai baki san idona biyu ina kallin a safiyan ne kuma da zaki kula nace na dakatar daku girki a gidan nan bado komai ba kada in maki ke daya ayi zaton abu.
Duk da ita maryam tana da nata halin a wani bangare bakuji tausayina ba a halin da nake ciki jummai sai yaushe zaku tausaya mi kuma.
Yau matar da take da zuria haka irin naki a gidan nan zatai maka haka inaga wata dabaka tara zuria da ita ba.
Yau idan diyan ki sukaji wanan jimmai yaya kike son suyi da ranau mai suka kasa maki dashi na rayuwa jimmai ?
Ni dai a bangare na ba wanda zaiji wanan zancen sai idan ke da kanki kika dabawa cikin ki wuka kika fito fili kika fada amma ina rokon ki jummai kiyi min addalci kada ki bata min yara da halin banza mu sam man matan nan don wuyan aure zasuyi ga al,umma insha Allah ga mazan ma banda abin da zance dasu sai addu,a a garesu.
Sai magana na karshe zancen yaran nan dake kasan waje jimmai ina rokon ki daki bar min yara su zauna lafiya do Allah kin daiji abinda hajiya ta fada a kanki.
Yana fadin haka ya mike ya digara sandan dake kara mai karfin tafiya ya bar dakin a jiyan zuciya ta sauke da karfi tabi baya shi da kallo har ya fice.
Dama tayi tunanen ranan ya ganta do a yadda yake kwance ba haka ta juyo ta samay shi kwance din ba sai dai ta dauka ya gyara kwanciyane kawai ashe duk yana ganin ta hakkuri irin nasa yasa bai mata magana ba.
Jikin ta yayi sanyi sosai tare da na daman sai kuma danta babawo daya ya fado mata a rai tace cikin takaici yanzu dan nan babu halin yin siri dashi tsakani da shi ke nan daga lokacin ta dauki fushi dashi sosai.
Bata kirashi ba sai dai shi kan turo mata sakon gaisuwa kullun garin Allah ya waye ko sakon barka da jumma,a sai kaji gidan shiru kwana biyu fitina da tsegumi ya rage sai an samu wani haka babban gidan ya gada dama.