A ZATO NA COMPLETENOVELS

A ZATO NA COMPLETE

Nayi nisa cikin tunani, ban ankara ba sai ganin Dr. Na Abba nayi a kaina yana snapping hannuwanshi a fuskata. Nayi firgigit! Kamar wadda ta tashi daga barci na kalleshi.
Yayi dan murmushi, “haba Nas, wannan dogon tunani haka har ina? Idan dai don nine kada ki damu, gani a gabanki. Ba zan matsa ko nan da can ba har sai kinyi min iznin hakan!”.

Ban san sanda na saki dan murmushi ba, Allah ya zubawa mutumin baiwar iya ba mutane dariya koda mutum bai shirya ba kuwa, ko kuwa ni ce kadai?.
Yace “haba! Ko ke fa? Ba gashi har kyakkyawan murmushin nan naki ya fito ba? Wallahi ba karamin kyau kike yi ba idan kika yi murmushi!”.
Nan ma ban iya daurewa ba sai dana kara yin wani murmushin.

Yace “so what’s up? Kwana biyu na daina ganinki anan, nayi zaton ko kin bar ward dinne. Jiya sister Mairo take ce min ba canza ku aka yi. Kin san yanzu evening duty nake yi, ina ga shi yasa bamu cika haduwa ba”.
Na dan gyada kai tare da cewa “haka ne kam, ya aiki?”.
Yace “Alhamdulillah. Ko kina da yan mintunan da zaki taka min zuwa nan waje Na’ilah? Ba don kowa na shigo da wuri ba sai don ke”.

Sai lokacin na kula da cewa yau ba sanye yake da labcoat dinshi ba. Na juya na kalli su Janan da suke yan rubuce-rubuce da danne-dannen waya, amma ni nasan hankalinsu gabadaya a kanmu yake. Na gyada mishi kai a hankali tare da sauka daga kan kujerar da nake, ni dashi muka jera muka fita.
Bai furta min komi ba, nima kuma banyi yunkurin cewa komi ba har muka fita waje. Kaina a kasa yake, ina dai bin sawun kafarshi ne dake sanye cikin takalmi sau ciki, don haka ban san sanda muka isa wajen ajiye motocin likitocin asibitin dake ta wannan bangaren ba, sai dana ji ya ja birki sannan. Ya jingina da jar motar shi 406, ni kuma na tsaya ina fuskantar shi.

Yace “Wato Na’ilah dalilin da yasa na so mu kebance muyi magana dake shine, ina so ne inji inda maganar mu ta kwana ne. Shin, har yanzu kina ganin bani da chance ne a wajenki?”.
Na dan yi wuri-wuri da ido, kafin in tsaida su waje daya, murya a shake nace “to ni me zance maka kuma, ina tunanin tun ranar nan na fada maka anyi min miji a gida?”.

Yayi dan murmushi, yace “Hmm, Na’ilah kenan! Aka yi miki miji ko kuma kika yiwa kanki miji, kika fada min?”.
Nace “kamar yaya? ban gane ba!”.
Yace “come on mana, daga jin yadda kike cewa ‘ai anyi min miji a gida!’, ko dan jariri yaji yasan cewa kin fadi ne kawai don kiji dadin bakinki!”.

Ban san lokacin dana kyalkyale da dariya ba, musamman lokacin daya make murya wai shi ala dole kwaikwayo na yake yi. Shima yayi murmushin ya kara jingina da motarshi yana dan murmushi, nayi shiru ina girgiza kai, amma murmushin fuskata bai bace ba.
Yace “da gaske ba. So I’ll like it idan kika manta da zancen mijin da ba’a riga an san ko wanene ba, let’s talk about us for now. Kamar yadda na fada miki ranar nan, gaskiya kina burgeni. Kuma ina fatan ace zaki bani dama, mu samu fahimtar juna a tsakaninmu. Me kike tunani?”.

Nace “magana ta gaskiya ni a halin da ake ciki yanzu likita, babu wannan maganar a cikin raina yanzu. Ina fata hakan bai bata maka rai ba?”.
Ya girgiza kai, “ko kadan. Kin san ku mata da jan aji, hakan ba matsala bace a wurina. Zan baki iyaka lokacin da kike bukata, amma ina neman alfarmar dinga yin waya dake zuwa lokacin da zaki sauko?”.

Nasan wannan rana ba zata taba zuwa ba, don dai mu rabu lafiya dashi sai kawai na gyada mishi kai. Yayi dan murmushi, “yauwa, nagode. Muje in dan taka miki ko?”.
Nayi yar dariya, nace “nayi zaton ni na rako ka?”.
Yayi yar dariya, “a’ah, ni na isa? Kawai dai ina so ne mu dan tattauna dake ne a waje dama dai kawai”.

Muka sake kwasa muka sake komawa dai, anan ne yake dan fada min tarihin rayuwarshi. Gidansu yana palladan, har kwatance yayi min amma da yake ba sanin unguwar sosai nayi ba ban gane ba. Ya fara min bayani akan irin rayuwar da yayi, da kalar makarantun da yayi, muka koma wajensu Janan.
Muka yi sallama dashi ya juya ya tafi, ni kuma na zauna akan kujerar da nake. Ina zama naci karo da idanun Janan tana hararata. Nace “malama lafiyarki kuwa?”.

Tace “ban sani ba. Ni zo ki raka ni waje inje in sayo wani abu in ci”.
Ba musu na tashi na bi bayanta, da yake karfe sha biyu da rabi ta kusa, lokacin tafiya sallah yayi. Muka yiwa Aisha sallama muka fita, nace mata “ai nayi zaton kina azumi ne yau”.
Tace “a’ah”. Ganin tana amsa min magana dai-daya yasa nayi shiru nima.

Tace “wannan likitan da kike biyewa, son shi kike yi ne?”.
Na dan yamutsa fuska, “wace irin magana ce kike yi haka? Wani irin so kuma?”.
Tace “to sai wani yage mishi baki kike yi kina dariya, me hakan yake nufi?”.

Na girgiza kai, “don Allah kada mu ja maganar nan tayi tsayi. Ni babu wani son shi da nake yi”.
Tace “to sai ki daina bashi fuska, a haka kina leading dinshi ne kawai ba wani abu ba!”.
Na daga baki hangamgam, nace “to wai ke meye matsalarki ne? Idan na kula shi ko naki kula shi, meye damuwarki?”.
Har ta daga baki zata yi magana, sai kuma ta fasa, tace “oho dai, ke kika sani!”.
Muka yi shiru muka cigaba da tafiya, can kuma tace “ya labarin su Sailu?”.
Muka karkata hirar zuwa can, wanda hakan ba karamin dadi yayi min ba.

Mun je ta sayi abinda zata ci, muka biya ta masallaci nayi sallah sannan muka koma ward. Acan taci abincin, muka cigaba da ayyukanmu har lokacin tashin mu yayi.
Janan ta riga ni tafiya saboda lokacin da aka tashi, wani yaro nake yiwa dressing. Faduwa yayi garin wasa da keke. Don haka ta wuce saboda a cewarta, zata biya kasuwa ta sayi wasu kayan bukatu kafin ta wuce gida.
Sai wajen karfe biyar da kwata na gama, na yiwa mutanen wajen sai da safe, na fita.

Sai dai cak! Naja na tsaya lokacin da nayi arba da abinda ban taba tunanin zan gani a daidai wannan lokacin ba. Yaya Bilal ne a tsaye kyam, tsayuwar sojoji, ya zube hannuwanshi duka biyu a cikin aljihun wandon kaftani dake jikinshi.
Kamar wanda aka ce mishi ya dago kanshi, karaf muka hada idanu dashi.

Abu na farko daya fara zo min a cikin raina, shine in fyalla da gudu. Sai dai da nayi tunani, sai naga meye na gudunshi to? Hakan ba wata mas’ala bace. Shawara ta biyu ita ce in tafi in raba ta gefenshi kawai in wuce, in nuna kamar ban san shi ba. Sai dai matsalar itace, kafafuna sun kasa motsawa balle har suyi tafiya. Don haka naci gaba da tsayuwa anan inda nake, ina kallon Yaya Bilal.

Ganin bani da niyar yunkurin yin wani abu, yasa ya tako cikin wani nutsattsen taku ya tunkaroni. Sai lokacin naji kafata ta motsa, na fara ja da baya, amma bai daina tunkarata ba. Da dai naga ya kusa cimma ni, sai na juya na sake fecewa a karo na biyu.

Can A&E na tafi, na shige can wani lungu da mutane basu cika bi ba na labe kamar wata munafuka. Na kwashe fiye da mintuna ashirin a wajen, zuwa lokacin nasan idan ma nema ne Yaya ya gaji ya kara gaba, don haka na fito daga maboyata.
Sai dana karewa wajen dana ganshi dazu kallo na tabbatar da cewa baya nan, sannan na daga kafa da sauri kamar wadda aka cilla daga jikin mashi, na dauki hanyar komawa hostel.

Sai dai da yake kwata-kwata yau sa’a ba a sashe na take ba, sai dana fara hango gate din hostel, har ina kara daga kafa, kawai sai ganin mutum nayi a gabana kamar wanda ya diro daga sama. Nayi tsalle nayi gefe daya a tsorace ina rafka salati, kafin in daga kaina in sauke su akan dodon nawa. Shi din dai da nake ta gudu.
Na sake juyawa da nufin ranta ana kare, ya sake shiga gabana, juyawar da nayi da sauri, da niyar bi ta wata hanyar, sai naji ni shame-shame a jikin bango. Shi kuwa yayi babakere a gabana, ya tsare gaba da baya, ta yadda babu yadda za ayi in tsere, sai dai idan bangaje shi zanyi. Ko kuma in ratsa ta jikin bangon dana jingina.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button