A ZATO NA COMPLETENOVELS

A ZATO NA COMPLETE

Yace “to matso maza ki sa hannu ki ci, bana son zama da yunwa”.
Na matsa a hankali kusa dani, na dauki wani cokalin nima na ci. Wannan karon ma har muka gama babu wanda yayi magana a cikinmu, ya tashi ya kwashi wayoyin hannunshi daya ajiye a kan center table, yace min ya fita.
“Allah ya tsare”, kadai na iya ce mishi. Yasa kai ya fita.

Bayan fitarshi na maida kayan kicin nazo na zauna ina kallo cikin rashin dadin rai. A haka Janan ta shigo ta sameni. Zuwanta ne ma ya dan sanya na saki jikina, muka shiga hira da ita. A bakinta ne naji ashe Yaya da kanshi ya cewa Anty Sarah kada ta kara turo mana da girki nan. Nayi kwafa a cikin raina, amma ban ce komi ba.

*

Yau ma ana yin sallar isha’i ta tsere sashen Anty Sarah. Ashe a can ta kwana jiya ma, wai Raheemah rufe mata kofa tayi. Na jinjina girman al’amarin, nace ‘Allah ya kyauta’, tace ameen.

Yau tun kafin in kwanta Yaya ya dawo. Na kai mishi abincin dana girka mishi, ya ci ya tashi ya tafi dakinshi, ni kuma na dauke kayan. Na koma daki nayi shirin barci, na kwanta.

Ina jin lokacin daya shigo dakin har ya kashe wuta, yazo ya hayo kan gadon ya kwanta shima, ban motsa ba.

Lokacin da naji ya matso zuwa tsakiya gadon, hannunshi yana ratsawa ta kan ruwan cikina, kanshi kwance akan kafadata, ji nayi kamar an tsayar da duk wani gudun jini a jikina. Nayi sak, hatta da numfashina sai daya tsaya cak.

Cikin wata irin murya, kamar ba ta Yaya Bilal din dana sani ba, yace “amarya ta!”.

Naji wasu irin emotions a cikin raina kala-kala, iri-iri, har na rasa da wanne zan ji. Idanuna suka ciko da hawayen dana rasa dalilin su, murya a cushe, kamar zan fashe da kuka, nace “amaryar da ake fushi da ita?”.

Ya sake janyo ni cikin jikinshi sosai kamar zai balla ni biyu, yace “to Na’ilah ya kike so inyi ne kam? Kiri-kiri fa haka kika fito kika nuna duk duniya baki da makiyi kamata, kika ki aurena, saboda tsabar rashin so ma har suma kika yi fa da kika ji labarin an daura miki aure dani ba wani ba. To ya kike son inyi? In dinga binki sawu da kafa, duk da rashin son da kika nuna min? Anya Na’ilah, anya baki so kanki da yawa ba kuwa?”.

Na hadiye wani yawu daya tarar min a baki, nace “wa yace maka na tsane ka?”.

Yace “ko baki fada ba Na’ilah, yadda kika badawa idanunki toka kika ki aurena kadai ya isa ya tabbatarwa da mutum cewa baki so na. Ba wannan ba, tunda abinda ya faru ya riga ya faru, me zai hana ba zamu bar abinda ya faru a bayanmu ba, mu fuskanci gaba? Mu fara rayuwar aurenmu ta hakika? Don in fada miki, aurena dake babu saki. Idan ma zaki hakura ne, ki hakura. Ba ki tunanin jan aji da yawo da hankalin ya isa haka?”.

Na turo baki kamar yana ganina, “wa yace maka jan aji nake yi?”.

Ya kara matsoni jikinshi, kanshi yana kara nutsewa a cikin gashin kaina, yana kara shakar daddadan kamshin da yake yi.

Muryarshi bata fita sosai saboda yadda ya gashin kaina ya rufe mishi baki da fuska, yace “nace miki rashin so, kin ce ba haka ba, shima jan ajin kin ce ba haka ba. To menene? Tsabar so ce, uhmm??!”.

Na daga baki da niyar bashi amsa, hannunshi da yake kan ruwan cikina ya fara zana circles, jikina ya dauki rawa kamar ana kada min mazari, na rasa muryar maida mishi martani.

A hankali naji ya juyo dani, hannunshi daya yana shafa gefen fuskata zuwa bayan wuyana, kafin ya hade bakinmu waje guda. Na lumshe idanuna a hankali, savouring the moment.

Zuciyata tayi nauyi, tunanina yayi nisa, babu abinda nake ji kuma nake fahimta a lokacin sai Yaya Bilal kadai da abubuwan da yake min, da kuma abubuwan da suke haddasa min a jinin jikina.

Zuwa can naji komi ya tsaya cak, kamar da can babu abinda yake faruwa. Na bude idanuna a hankali, na daga kaina da niyar ganin abinda yake faruwa.

Sai dai abinda naci karo dashi ne ya bani mamaki, ta wani bangaren kuma yaso ya sanya ni kyalkyalewa da dariya.

Yaya Bilal barcinshi yake shaka tsakaninshi da Allah akan kirjina, har da jan minshari!.

F.W.A

             *☆⋆37⋆☆*

Da asubah Yaya Bilal ya tashe ni, ban ma san lokacin da barci ya dauke ni ba jiya. Ya fita masallaci, ni kuma na dauro alwala nayi sallah ta.
Yau bai tsaya a waje ba, gari yana fara yin haske ya dawo cikin dakin. Ina zaune ina lazumi ya shigo, ya koma kan gado ya nade, ni kuma naci gaba da lazumi na. Ina gamawa kuma kicin na shiga, na hada breakfast mai kyau, na gyara ko’ina ya fito fes, sannan na koma daki. Har yanzu Yaya barci yake yi.

Na shiga bandaki da niyar yin wanka, kafin in fito Yaya ya bar dakin. Bayan na fito, na shafa mai, yar hoda da man lebe, na janyo wata doguwar rigar buba ta atamfa na sanya. Na bade jikina da turare kamar ko yaushe na fita falo.

Har yanzu Yayan bai fito ba, don haka na zauna akan daya daga cikin kujerun falon ina jiran ya fito. Kafin ya fito dinne na kira Maryam wadda naga missed call din da tayi min jiya da dare yau da safe, muna cikin hira da ita kofar dakin Yaya ya bude, na juya na kalleshi lokacin daya leko daga ciki.
Yace “kawo min abinci na nan Na’ilah”.

Muka yi sallama da Maryam, na dauki kayan na wuce dakinshi. Yana tsaye a gaban mirror yana fesa turare a jiki na shiga, ya ajiye kwalbar turaren, ya matso ya karbi kayan hannuna ya ajiyesu a can gefe. Na koma kicin na dauko babbar ledar cin abinci nazo na shimfida, sannan na zauna na hau zuba abincin.

Ya gama abinda yake yi, yazo ya zauna, na tura mishi abubuwan dana zuba gabanshi. Sai daya zauna sosai sannan na gaida shi, ya amsa min fuska da walwala da fara’a, hakan ya sanyaya min zuciya kwarai.

Ina kokarin zuba nawa abincin, ya katseni, “dauki cokali ki sa mu ci wannan, idan mun cinye sai a kara. Ko ba zaki ci dani bane?”.

Nayi saurin girgiza kaina, “ni ban ce ba”, na dauki cokalin nasa na fara ci, Yaya yayi dan murmushi.
Shiru tunda muka fara cin abincin, babu wanda yayi magana.
Zuwa can yace “an riga an gama komi, a can Abuja zaki yi internship dinki. Ina fata babu matsala?”.

Da sauri na girgiza mishi kai, nace “a’ah, babu. Nagode”.
Yace “meye na godiya kuma? Kunshin hannunki yayi kyau matuka”. Ya canza akalar hirar tamu.

Na dan saci kallon hannuna na hagu dake kan cinyata. Ni kaina da kunshin yake hannuna yana burgeni sosai, don ya tsaru ne.
Ban tantance ba naji ya kamo hannun nawa cikin nashi, na kalleshi a dan kunyace, amma shi ko a jikinshi. Ya cigaba da cin abincinshi a nutse, kamar babu abinda ya faru.
A hankali nayi kokari na zame hannuna daga nashi, sai dai ina maida shi inda yake da, naji ya sake janyo shi. Wannan karon kyam ya rike idanuna cikin nashi kamar wanda yake challenging dina akan in sake janye hannun, sai nayi kasa da nawa idanun, na kuma kyale shi. A haka muka gama cin abincin.
Nayi tsam na tashi, na fara hada kan kayan na kai kicin. Na tsaya na wanke su ma ajiyesu a inda yakamata, sannan na koma falo. Na dauki remote na kunna tv ina kallo har Yaya ya fito cikin shirin fita.

Ya tsaya a gefena yana daura agogon hannunshi, “zan fita, nasan sai zuwa dare zan dawo yau don haka kada kiyi abincin rana dani. Babu wata damuwa dai ko?”.
Na girgiza mishi kai.

Ya sanya hannu ya dago habata yadda muke kallon juna ta cikin ido, kallon tsakiyar idanunshi ba abu bane mai sauki, ji zaka yi kamar an sanya sarkoki an daure duk wasu gabban ka masu motsi, yayin da a gefe guda kuma zaka ji kamar an dauko wani dutse ne an aza maka aka, ka kasa motsi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button