Dr. BOBBY COMPLETE HAUSA NOVEL

Daga wnn page na kawo karshen Free pages dina sbd haka inayina kowa fatan alkhairi…wayanda sukayi patronizing a big thank u to all Allah ya saka da khairan????????
Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank…sai a tura evidence of payment ta 07063800556.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba…masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344…sai a tura evidence via 07063800556.
13
Basu suka baro hall din nan ba sai after seven…lokacin duk an gaji su hajia Aysha a gajiye aka dawo gida sbd rawa da aka tika wajen…kai tsaye ta fada bayi ta watsa ruwa a jikinta snn ta fito tasa kayan bacci tareda hayewa gado ta nade kaman wanda zatayi bacci…sai yanxu ta tunada wayanta data bari a school bag din daxun…shaf ta mance data dawo bata fito dashi ba ta mike da sauri zuwa inda ta ajiye jakan ta zaro wayan snn ta sake komawa gado…missed calls ta tarar guda 46 aikuwa ta wara ido sosai tana kallonsu..biyu daga ciki na Billy ne sai guda hudu na Besty sai kuma wata bakuwar Number mai sauran 40 din…ta danyi shiru tana nazarin number lokaci daya kuma sai ta wara ido tana sakin murmushi data tuna mai number…wnn sugar daddyn ne da suka hadu a Chicken Republic ranan…Allah sarki bawan Allah shine yayita jera mata missed calls haka?..tayi mamaki ma da bai ta6a kiranta ba sai yanxu…har ta danna zatayi dialing number dinshi sai kuma taga bari ta fara kiran Billy da bsty tukun dan kar ta fara kiranshi ya cinye mata time bata kirasu ba…Billy ta fara kira suka gaisa tareda yima juna ban gajia snn Billy ta jaddada mata tana nan zuwa gobe inshaAllah…suna gamawa ta kura bsty shi kuma korafi yaketa yi wai basu tsaya sunyi sallama dashi ba suka wuce ita kuma tayita aikin bada hakuri har ya hakura…bayan sun gama ta wani sake lafewa kan pillown da take kwance tana lumshe idanu tayi dialing number dinshi da yanxun nn tayi saving as Prof…yana shiga kaman jira yake ya dauka sai ya sauke wani wawan ajiyan zuciya before saying”baiwar Allah laifin me nayi ake ignoring calls dina haka?..”tana smiling tace”sorry bana tareda wayan ne”..yace”hankalina duk ya tashi na fara tunanin kodai ban samu kar6uwa bane”..murmushin ta kara saki tace”sam ba haka bane..bikin cousin dina akeyi shine na manta ban tafi da wayan ba”…yace”to shiknn hope ban takura maki ba?..”tace”not at all”..tana jiyo sautin smile dinshi kafin yace”to yanxu ya zakiyi dani?..inaso in ganki gaskia”..tace”bana Kano yanxu..na dawo gida”..yace”ohh ba kano kikeba?..”tace”yea Gombe”..ya wara idanunshi da kyau kafin yace”no wonder kikeda kyau..dama an fadamin gaba daya ‘yan Gombe kyawawa ne”..tayi murmushi kawai..shi kuma ya sake yin kasa da murya yace”to nidai inason ganinki and if kin bani dama har Gomben zan iya zuwa”..tace”haba da akwai nisa fa”…yace”bakiji ance garin masoyi bai nisa ba?..nifa da gaske nake sonki Aysha bada wasa ba..ban ta6a tunanin zan iya auren karamar yarinya ba sai a kanki..so please inaso a bani dama”…shiru tayi tana tunanin me zatace mishi…tadai san ko ta fara shaye shaye bazata fara kawoshi gidansu ba dan Lamido najin labari zaice ta fito da miji a nata aure tunda tara samari take..besides shi kanshi daddy won’t take it likely idan yaji ta kawo saurayi gida ba tareda ya nemi izini ba snn Ammi ma ba rufa mata asiri zatayi ba dan bakinsu daya itada daddyn..amma yanxu ya zatayi da wnn bawan Allah data farajin itama kaman tana sonshi…idea ne ya fado mata dan haka da sauri tace”to ka bari mu gama biki zuwa Sunday sai mu hadu a Bauchi”…yace”but why Bauchi?..ba kince Gombe ne garinku ba?..”tace”nan ne garinmu amma bazan iya kawoka gidaba sbd mahaifina zaiyi fada”..yace”zan iya turowa a nemi permission dinshi if kin amince cox banso da girmana in hadu da yarinha baa gidan iyayenta ba..it’s not proper ko ‘yata aka yima haka bazanji dadi ba”…ta dan shagwabe muryanta tace”nidai banaso kazo yanxu plss and Bauchin fa ba gidan wani zamu hadu ba gidan small mom dita ne..qanwar mamana”…shiru taji yayi for a while da alama yana tunanin yiwuwar hakan ne…kafin yayi mgn ta sake narke murya kaman wadda ke shirin fashewa da kuka tace”shikenan dama nasan ba damuwa kayi dani ba”…da sauri yace”subhanallah baby why zakice haka?..”tace”gashi nan sbd nace mu hadu a Bauchi kanaso kace ka fasa zuwa”..yace”alright ok don’t cry plss…kawai ina ganin rashin dacewar hakan ne a matsayina na babba bai kamata na biye miki ba amma zanzo kinji?..zanzo inshaAllah”…lokaci daya ta saki smile tanajin dadin yanda yake mata tace”shknn Allah ya kaimu…ranan sunday inshaAllah”..yace”no problem Allah ya kaimu i can’t wait to see you”..tayi daria tana feeling kanta kaman a sararin samaniya..wnn shine exactly dalinda yasa take son sugar daddies…tayi shagwa6arta son ranta babu wanda zaice don me..dan Allah ya sani tana son taga ana pampering dinta ita dai sai kuma Allah bai bata irin wann parents din ba don daga Ammi har daddy ba masu sangarta yara bane..itama din da takeyi kawai don abun yana jininta ne amma ba shagwa6ata suke ba shiyasa wani lokaci Ammi takan ce”wnn yarinya da shagwa6aki muke Allah kadai yasan iskancin sa zaki mana a cikin gidan nan”…sun dauki lokaci mai tsayi suna waya tanata zuba shagwa6arta yana biye mata aikam farin ciki kaman ta zuba ruwa kasa tasha to dama abun nema ne ya samu wai matar driver ta haifi mota????.
Washegari around 11 Billy ta karaso gidan…if u see yanda suka rungume juna sunata murna zakayi tunanin dadewa sukayi basu hadu ba nan kuwa jiya jiyan nn suka rabu…bayan sun gama hoge hogensu suka je ta gaisa da daddy da Ammi snn suka shiga daki…Billy take bala labarin yanda sukai da Sir Abdool wai ya kai karanta ta dena daukan wayanshi…Aysha ta wani cunno baki tace”wai bama fada miki abunda yayimin ba?..”Billy tace”and so what dan yayi pecking hannunki?..Lamido nifa banga wani abu a nan ba kawai kina nema kiyi complicating abubuwa”…da mamaki tace”seriously?..yanxu ke a wurinki ba komai bane namiji ya kama hannunki yayi kissing?..”Billy tace”of course ba wani abu bane mana indai da soyayya…kema fa da kina sonshi nasan wlh bazaki damu da hakan ba kawai dan bakya sonshi ne”…tace”Alhamdulillah da kika gane bana sonshi…ke ban fada miki ba jiya bakiga wayan da mukasha da wnn mutumin ba wlh..Billy he is so romantic nima harna fara sonshi wlh..gobe ma zaizo mu a hadu gidan Aunty fiddausi”…harara Billy ta buga mata tace”au yanxu har daman zuwa zance ma kika bashi mutumin da bakisan halinshi ba Lamido?..ba gara Sir Abdool din ba tunda shi munsan wayeshi?..”Aysha ta ta6e baki tace”ba dama ayi mgnr arziki sai kice Sir Abdool…nidai dan Allah ki taimaka ki roki Ammi kice zan rakaki gida sai muje tare plss”…a kufule Billy tace”bazanyi ba”..tace”C’mon Billy dan Allah fa nace?..”Billy tayi mata banza bata kulata ba.
Da yake event din ranar na dare ne basu suka fara shiri ba sai after magrib…yauma kaman jiya har gida make up artist tazo tayi musu wnn karon hadda Billy…Lace ne a jikinsu yellow da black flowers a jiki sai aka daura musu black head dinkin straight gown daya zauna jikin kowaccen su…karfe takwas da wani abu Hamma Najeeb ya kwashesu zuwa hall da zaayi event din…wurin yayi kyau sosai hakama Amarya da maids dinta tamkar a sacesu a gudu sbd kyau…Amminsu ma yau ba’a barta a baya ba dan make up akayi mata light wanda baikai nasu ba sai ta fito tayi das abunsa kamar yammata…biki dai yayi biki domin anci ansha anyi ruwan kudi snn an dirki rawa kaman ba gobe…su Aysha basu koma gidaba sai after twelve..wanka kawai sukayi suka kwanta bacci.