Dr. BOBBY COMPLETE HAUSA NOVEL

Suna kowawa gida ya shige bedroom dinshi yayi wanka sharp sharp ya fito ya saka pyjamas snn ya dauki wayanshi ya kwanta kan gado yana dialing number dinta…kafin ya gama ringing ta dauka cikin muryanta da yake ganin bazai ta6a gajiya da sauraronta ba tace”hello”..lumshe ido yayi ya bude yana jin wani irin feeling tattare dashi a hankali yace”La..mi..do”..tace”sir ina yini”..yace”lafia lau..how are u”..tace”fine”..suka danyi shiru na wani lokaci Bobby baisan lokacin daya furta”i missed u”ba..ta wara idanu sosai kaman yana ganinta tace”sir banji me kace ba”..kai tsaye ya sake cewa”i said i missed u..i missed ur rashin jin mgn”..ta dan turo baki tace”nidai inajin mgn”..murmushi ya saki yana shafa beard dinshi ko ba’a fada ba yasan turo mishi baki takeyi yanxu haka..kawai sai yaji yanaso yaga bakin datake turowan amma babu hali..ita kanta so yake ya ganta ji yake kaman yayi tsuntsu kawai saidai ta ganshi a hostel dinsu amma still babu halin yin hakan…rage muryanshi yayi can kasa yanda bazata jiba yace”i love u..i wish i can tell u”..tace”sir me kace?..”yace”cewa nayi yau na hadu Lamido a Abuja”..ta wara ido kaman yana ganinta tace”Lamido dai namu?..”yace”yea tareda dad dinki sukazo”..tace”amma dai bakace musu nayi wani abun ba koh?..”cikin zuciyarshi yace”nace musu mana..na fada musu kin sacemin zucia”..a zahiri kuma murmushi yayi kafin yace”ke me kike tunanin zan fada musu?.”tace”sir ban saniba..kawai dai banso kace nayi laifi sbd nasan Lamido ina komawa gida zai rufeni da fada..kilan ma yace in fito da miji amin aure”..ta karasa mgn tana turo baki…shiko Bobby shiru yayi wani tunanin na darsuwa a zuciyarshi…hakane fa Lamido shine zai bada aurenta tunda yana raye koh..sai yaji inama sun daidaita da ita kawai yacema Waziri yanaso a nema mishi aurenta…yasan kuma bazasu hana ba sbd a yanayin yanda yaga mu’amalarsu ya tabbata ba karamin zumunchi ke tsakanin Familynsu da Familyn Lamido ba…nan take yaji wani kwarin guiwa yazo mishi..zuciyarshi ke fada mishi inshaAllah kaman ya samu auren Lamido ne ya gama tunda yanxu baida wani problem da yake ganin yana iya sawa a hanashi aurenta..problem daya da yake fuskanta yanxu shine rashin sanin actual abunda ke mind dinta..shin tana sonshi ne ko kuwa bata sonshi?.
Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba…masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank…sai a tura evidence of payment via 07063800556.
35
Washegari gaba dayansu suka tafi airport bayan gwagwarmaya da akasha da waziri dan cewa yayi fafur bazasu tafi su barshi ba..da kyar da sidin goshi suka samu suka shawo kanshi tareda alqawarin dawowa nan bada dadewa ba…kafin su wuce saida aka zagaya dasu cikin Freedom Medical College suka gani sosai kowa sai santinta yake musamman su Aunty Munubiya da basu ta6a zuwa ba..daga nan airport suka wuce already dama sun siya tickets so suna zuwa duk suka shiga Plane dinsu da is about to flight sbd time din tashinsu yayi…karfe goma da wani abu suka sauka Malam Aminu Kano International Airport..Aunty Munubiya bata yadda ta wuce gida ba tace saita fara zuwa gidansu taga Mummy snn zata wuce..motoci uku ne sukazo daukansu daga airport ciki hadda Mummy data kasa hakuri har su karasa gida..suna haduwa da Aunty Munubiya nan ma suka rungume juna kowaccs tana hawayen tunawa da rayuwar baya..saida aka 6an6aresu daga jikin juna snn suka shishshiga mota suka wuce…ko a mota hiran yaushe gamo sukeyi kowa tana sake neman gafarar kowa dukda cewa ba wanda yayima wani laifi a cikinsu…bayan sun isa gida ma thesame thing ne yaci gaba da faruwa har saida yaran suka koma yi musu daria…Bobby dai samu yayi ya lalla6a zuwa Flat dinshi ya dau car keys dinshi ya fice zuwa FCNM ba tareda sun lura dashi ba..so yake kawai ya ganta ko bai samu yin mgn da itaba its ok amma he really needs to see her…kafin ya karasa College din ya kira Nur ya sanar dashi yanaso ya ganta..Nur yace bashida wani matsala kafin ya karaso ma zai kira mishi ita office dinshi…cikin sauri yake driving har ya karasa college din..yana gama parking ya fito zuwa office din Nur…zaune ya sameta office din suna duba wasu papers itada Nur..baisan time daya saki wani lallausan murmushi yana kallonta ba..seeing her really makes his day..addu’a kawai yake Allah ya karkato da hankalin yarinyar nan zuwa gareshi dan ya tabbata idan bata soshi ba matsala zai samu gagaruma ma kuwa…karasawa ciki yayi ya zauna seat dake opposite to her ita sai a lokacin ma ta ganshi..saita dan saki murmushi idonta a kasa tace”sir good morning”..kallonta kawai Bobby keyi ya kasa amsawa..ta dan dago a hankali ta kalleshi sai taga gaba daya attention dinshi na kanta tayi kasa da idon da sauri tana turo baki..itafa ba son wnn idanun nashi a kanta take ba ya sani amma shine zaiyita wani tsareta dasu salon yasa ta farajin wani iri..kallonta yakeyi sosai kamar yau ne ya fara ganinta..Nur da yaga haka sai ya lalla6a ya mike ya bar musu office din yana kunshe daria…kaman jiran fitan nashi yake ya matso da seat dinshi dab da nata har suna jin kamshin turaren juna..kallonta yakeyi har yanxu kuma baida alamar denawa dan haka Lamido ta runtse ido tanajin yanda gabanta har faduwa yake sbd kallon nan da yake mata..bakin nan kuwa ta gama turoshi tamkar zai tafi Gombe ya barta nan kano sbd tsabar tsinin da yayi…a hankaki yakai hannu yayi cupping fuskanta dasu tareda dora nashi fuskan ya hadeshi wuri daya da nata yana sauke wani numfashi da karfi kaman wanda yayi aikin karfi…sake runtse idanunta tayi and gabanta bai bar faduwa ba…shima nashi idanun a lumshe suke yanajin wani irin abu yana zagaya cikin jinin jikinshi har zuwa zuciyarshi…shi kanshi nashi gaban faduwa yake so yake kawai yajita a jikinshi ko dan yayane amma baisan tayaya ba…a yanda yakeji din nan yasan idan bai samu abunda yakeso ba yana iya zautuwa..wani irin karatu yakeji daga can cikin kwakwalwarshi ya kusa rasa hanyar da zaibi ya biya karatun…da kyar ya daga hannunshi da yayi masifar nauyi ya dorashi kan lips dinta da har yanxun suke a ture tayi wani irin zabura ta kwace face dinta daga hannunshi garin haka kujeran da take zaune a kai yayi baya saura kadan ta fadi yayi azamar janyota ya dawo da ita jikinshi…a tare suka sauke ajiyar zuciya kafin ta shiga kokarin kwace kanta amma ba rikon banza yayi mata ba..ji yake yau idan bai furta mata abunda ke cikin ranshi ba yana iya mutuwa…gaba daya zuciyarshi ta gama narkewa yana kuma da yakinin babu taimakon da zata iyayi mashi matukar bai furta mata what he’s feeling ba…a hankali ya bude baki cikin muryanshi daya canxa completely yace”i..i..l..ov”bai samu daman karasawa ba sakamakon kwace jikinta da tayi da wani mugun karfi har hakan yayi sanadiyyan faduwanta kasa tim kafanta ya bugu da wani table aiko ta kwalla wani mugun kara daya dawo dashi hayyacinshi..ya mike da sauri kafin ya isa gareta cikin kuka tace”don’t touch me”..tsayawa yayi cak yana kallonta da idanunshi da suka canxa launi kaman ba nashi ba…kallon yanda ta rike kafanta tayi tana sakin wani irin kuka yayi nan yake yaji kukan nata na damunshi..sake takawa yayi still bai karasa ba tace”i said stopp..don’t come near me idan ba haka ba zan buga kaina da wnn table din”..da sauri ya tsaya nan inda yake murya a dakushe yake fadin”No..don’t do that plss..am..sorry..i never meant to hurt u”..bata kulashi ba sai kokarin mikewa da take amma ta kasa dan da gaske kafan nata ba karamin buguwa yayi ba..Bobby da yakejin kaman tashin hankalin duniyan nan aka tattaro aka dora mishi ya dan sake matsawa da nufi ya taimaka mata amma wani hadadden kara data saki dole yasashi tsayawa daga nan inda yake gamida runtse idanunshi…ba tun yanxu ba dama yasan ta iya kara sosai yasan kuma idan yace zai cigaba da kokarin matsawa kusada ita tara mishi jama’a zatayi da wnn uban ihun nata…gashi kuma ta kasa mikewa da alama tana jin jiki sosai..hankalinshi yakai kololuwar tashi ya kuma rasa taimakon daya kamata ya bata…Nur ne ya shigo office din ganin abunda ke faruwa ya karasa ciki da sauri yana cewa”Subhanallah meya sameta haka?..”kallonshi Bobby yayi da jajayen idonshi da kyar ya bude bakinshi yace”i..i..”kasa karasawa yayi sbd wani irin sarawa da kanshi yayi kawai sai ya durkushe nan wurin yana sauke numfashi…Lamido dai kukanta takeyi bilhaqqi tana rike da leg dinta..ganin haka sai Nur ya karasa kusada ita shima ya risina nan gabanta yana fadin”Lamido meya sameki?..what happened?..”cikin sheshshekar kuka tace”kafana ne ya bugu..sir bazan iya tashi ba ka taimaka min”..a rikice Bobby ya dago yana kallonta jin abubda tace…yanxu knn ta gwammace Nur ya ta6ata akan shi?..wani irin kishi yaji ya lullu6eshi baisan lokacinda ya mike ya kama hannun Nur dake kokarin taimaka mata ta mike ba kawai sai yajashi sukayi waje…kallonshi Nur yake da mamaki ganin yanda ya wani hade rai yace”meye hakan?..”fuska daure yace”you will not touch her”…idanuwa Nur ya ware akanshi daria na son kufce mishi yace”seriously?..kai meya hana ka taimaka mata tunda kana gani ta kasa mikewa”..a hankali yace”she won’t let me..she is upset sbd na ta6ata and wlh Allah Nur ba laifina bane..kai kanka kasan wnn ba halina bane amma when it comes to her..i dont know what just got into my head..i..”kasa karasawa yayi sbd rauni da muryanshi yayi..idonshi ya sake kadawa yayi jajir ya kamo hannun Nur yace”dan girman Allah kada ka ta6ata Nur..kanayin haka matsala zan samu na sani”…kallonshi Nur keyi duk kuma sai yaji ya bashi tausayi…rike hannunshi yayi shima kafin yace”don’t worry bazan ta6ata ba amma bari inyi mgn da Meena da Billy friend dinta sai suzo su dauketa mu kaita clinic”..kai kawai ya gyada mishi tareda sauke numfashi…lokacin da suka koma office din kuka take wiwi kuma har yanxu bata bar rike kafan nata ba…wani irin sanyi da zafi yaji sun rufeshi all of a sudden..duk wnn abun daya faru laifinshi ne..laifinshi ne daya kasa controlling feelings dinshi har ya janyo mata wnn matsalan…tsoronshi Allah tsoronshi kada taje tayita langabewa har kafan yazo yana rurucewa sbd ya santa sarai da raki da kuma kin magani da allura…duk hankalinshi yayi 6agal 6agal ko mgn ma kasawa yayi…bayan mintuna kadan Billy ta shigo office din tareda Nurse Meena nan suka taimaka mata ta mike kafan nan a dangale ko takashi batayi ba sbd azabar raki…Bobby ya lumshe ido dama yasan za’ayi haka…yanxu Allah kadai yasan adadin tashin hankalin da zata haifar mashi dalilin wnn ciwon…yasan yayi bye bye da kwanciyan hankali idan har ba gani yayi ta koma normal ba…kai tsaye clinic suka nufa da ita Bobby da Nur na binsu a baya…suna kwantar da ita kan bed Nur ya dakko wani muscle pain killer ya mikama Billy yace”ku shafa mata”..ba musu suka amsa suka shiga shafa mata a kafan nata ita kuma sai gursheken kuka take tana cewa da zafi…kallon yanda suke shafa maganin a hankali Bobby yayi yasan indai ba murzashi sukayi yanda zai shiga ciki ba ba abunda zaiyi mata amma kuma shima murzawan yanxu aiki ne tunda ba yadda zatayi ba..ajiyar zuciya ya sauke yana cigaba da kallonsu har suka gama Aysha bata dena kuka ba kaman yanda zuciyarshi bata dena tsalle tana ce mishi bai kyautawa abar sonta ba…suna gamawa Nur ya dakko wani magani ya basu shima aka samu da kyar suka bata tasha snn ta kwanta tayi luf tana sauke ajiyar zuciya kafin a hankali kuma bacci ya sadado yayi gaba da ita…sai a lokacin Bobby ya sauke ajiyar zuciya mai karfi amma har yanxu hankalinshi bai kwanta da yanda yaga kafan har ya fara kumbura ba…ganin yanda duk yabi ya zama wani iri Nur ya kama hannunshi suka zauna ya shiga kwantar mishi da hankali..idonshi sun kada jajir yace”duk ni na janyo mata wnn suffering din Nur..da ban biyewa son zuciyata ba da duk wnn bai faru ba..ji nake kaman zan hadiye zuciya in mutu..ciwo nakeji sosai bazan ta6a yafema kaina idan wani abu ya sameta a dalilina ba”…ya karasa mgn cikeda wani irin rauni da tashin hankali…kama hannunshi Nur yayi yana kallonshi cikeda tausayi yace”ba laifinka bane..dama Allah ya rubuta hakan zai faru so ka kwantar da hankalinka”..girgiza kai yakeyi yace”hankalina bazai ta6a kwanciya idan ina ganinta cikin wnn halin ba”..daga hannun Nur din yayi ya dora saitin heart dinshi yace”ni kadai nasan me nakeji a ciki..ni kadai nasan tashin hankalin da nake ciki”..yana gama mgn ya mike da sauri ya fita daga dakin sbd hawaye da yaji sun cika mashi ido…barin clinic din yayi gaba daya ya bude office dinshi ya shiga tareda kullewa ta ciki..yanada bukatar ya kebe ya zubda hawayen nan ko zai samu saukin nauyin da yakeji acikin zuciyarshi…yana shiga ya wurga kanshi kan sofa kawai sai ya shiga dukan head dinshi da hannunshi yana fadin”why why why plss?..why me”…ya karasa mgnr yanajin wani zafi a cikin heart dinshi..hawayen da yake son su zuba ko zai samu sassauci ma sunki zuwa amma kallo daya zaka mashi ka gano tsantsar damuwa da rudanin da yake ciki…ciwo yake mishi daya kasance sbd shi ta shiga wnn halin..sbd son zuciyanshi..da bai aika abunda yayi ba yasan babu yanda za’ayi garin kwace kanta har taje tana faduwa haka?..ya tuna yanda mahaifinta yace ya yadda tarbiyyarshi shiyasa zai damka amanarta a hannunshi shine yanxu yici amanar tashi haka?..”oh Allah what a monster i have become?..”ya fada a sarari yana cigaba bubbuga kanshi..a takaice saida ya kwashi almost 30 mins yana abu daya kafin ya sarara…bathroom ya shiga ya wanko face dinshi dukda ba kukan yayi ba amma face dinshi ya canxa sosai..yana fitowa ya bude office din ya koma zuwa clinic…zaune ya sameta Billy da wata colleague dinsu na kokarin taimaka mata ta sauki daga gadon ita kuma sai hawaye take yi…wani irin daci yaji har cikin bakinshi yana karasawa ciki ta wani hade rai snn ta dauke kai tana turo baki…murmushin yake ya saki wnda akace yafi kuka ciwo yana kallonsu da kyar suka iya sauko da ita snn suka kama hanyan fita daga dakin…su Billy da basu lura dashi ba sai yanxu suka gaidashi snn suka fice kowacce rikeda hannunta guda suka barshi tsaye yana binsu da kallo…juyawa yayi shima ya fita ya tsaya daga bakin kofa ya rungume hannu yana kallon yanda ko daga kafan da kyar takeyi kilan sbd zafi ne ko kuma sbd tsabar raki ne irin nata…saida yaga sun 6ace ma ganinshi snn shima ya bar wurin ko office din Nur bai komaba ya shiga motarshi ya bar makarantan…a hankali ya tuka kanshi har ya isa gida..yana shiga yayi mamakin ganin har yanxu su Aunty Munubiya nan nan basu tafi ba shidai ya wuce flat dinshi sbd baison ma ya zauna nan cikinsu bare su fuskanci yana tareda damuwa…haka yayita zaune a daki yinin ranan har su Aunty Munubiya sukazo tafia ta aiko a kirashi suyi sallama amma yayi pretending yana bacci yaki fita…har dare bai fito daga Flat dinshi ba ko sallahn magrib da ishaa a nan cikin dakin nashi yayisu sbd fever da yaji ya rufeshi…hankalinshi gaba daya yana kanta so yake yaji halinda take ciki amma tsoron kiranta ma yakeyi sbd yasan ba dauka zatayi ba…yasan Nur ne kadai zai iya taimakonshi a halinda yake ciki dan haka ya danna masa kira..yana dauka ko salam dinshi bai amsa ba yace”Nur inaso inji halinda take ciki plss..kunyi mgn da ita?..”Nur yace”bamuyi ba..ka kirata a waya mana”..da sauri yace”ba dauka zatayi ba..nidai taimako na zakayi zako gida saika kiramin ita a wayanka..inaso inji ya jikinta”…ajiyar zuciya Nur ya sauke kafin yace”shknn gani nan zuwa”..da sauri Bobby yace”nagode sosai friend..nagode”..Nur ajiye waya yayi yana mamakin wnn so da Bobby kema Lamido haka?..duk yabi ya koma kaman wani soko sbd soyayya…shi kanshi daxu ba karamin tausayi ya bashi ba…yaji inama Lamido zata amince ta aureshi kawai a wuce wajen…keys din motanshi ya dauka ya fita daga gidan…su Mummy na zaune parlor lokacinda ya shigo tabishi da kallo kawai..tun daxu ta fuskanci akwai abunda damun Bobby zuba ido kawai tayi taga gudun ruwanshi and wnn zuwan na Nur ya sake tabbatar mata da lallai ba lafia ba…ko zama baiyi nan parlon ba kawai ya gaishesu ta wuce ciki Aunty Sumy da kanta saida tayi mamakin hakan…a kwance ya samu Bobby har yanxu eyes dinshi basu dawo normal ba..yana ganinshi ya mike zaune shima Nur din karasawa yayi kusa dashi ya zauna snn ya shiga kiranta yasa a speaker…har ya gama ringing baa dauka ba ya sake kira wnn karon yaji an daga amma maimakon ita sai yaji muryan Billy na fadin”bacci takeyi sir”..Nur yace”ya jikin nata?..”Billy ta juya ta dan kalli yanda kafan har ya fara swelling tace”sir kumbura kafan yakeyi..yanxu ta gama kuka sai da kyar muka samu bacci ya dauketa”..ba Bobby ba shi kanshi Nur din hankalinshi tashi yayi da sauri yace”i will get back to you”..daga haka ya kashe wayar yana kallon Bobby daya dafe head dinshi da hannu bibbiyu yana jujjuya kan cikeda tashin hankali yace”Nur na shiga uku..zuciyata bugawa zatayi wlh”..da sauri Nur ya kama hannayen nashi ya rike tareda fadin”ba abubda zai faru inshaAllah..ka kwantar da hankalinka yanxu zanje in nemi doc saratu muje can hostel din ta dubata”..mikewa yayi da sauri har wani juwa ke neman daukanshi yace”muje ka kaini in ganta plss..hankalina bazai kwanta ba idan banga halinda take ciki ba”..kamashi Nur yayi ya zaunar dashi yana dubanshi yace”relax dan Allah..kaga yanda jikinka ke rawa kuwa?..kaima kana bukatan medication sbd haka kasha magani ka kwanta ka huta ni zanje inyi duk abunda ya kamata ayi mata”..tun kafin ya rufe baki Bobby ke girgiza kai yace”u won’t understand..kona zauna hankalina ba kwanciya zaiyi ba..i need to see her”..shiru kawai Nur yayi yana kallon yanda yake mgn da kyar sbd tashin hankalin da yake ciki…basu san sanda Mummy ta shigo ba jin mgnrta sukayi kusa dasu…Bobby na daga ido daya ganta kawai sai ya mike tsaye da sauri ya fada jikinta murya a raunane yace”Mummy inaso inje in ganta plss..zuciyata bugawa zatayi”…da mamaki Mummy ke kallon Nur tace”Nuru meya sameshi haka?..”a nustu Nur ya bata labarin iya abunda ya sani itama nan take taji nata hankalin ya tashi..kada dai ace Bobby wani abu yaje yayiwa yarinyar mutane fa…dagoshi tayi daga jikinta tana kallonshi..tambaya take son mishi kan abunda ya haddasa faruwar haka amma sai ta kasa sbd tsantsar tashin hankali data karanto a fuskanshi da kuma yanda idanunshi suka juye lokaci guda tasan tsaf zuciyan nashi zai iya bugawa kaman yanda fada..batayi gaddama ba ta kalli Nur tace”kaje dashi ya ganta..snn duk halinda ake ciki ka kira ka sanar dani and make sure shima kayi mishi treatment sbd zazza6i ne sosai naji a jikinshi”…kallonta Nur yake kafin yace”amma Mummy shima yana bukatar hutu fa”..tace”idanma bakuje dashi hutun da muke so yayin ba samun yinshi zaiyi ba..banason zuciyar nashi ya samu matsala kaman yanda nace kuma nasan halinshi muddin baa kaishi ya gantan ba yana iya samun problem”..gyada kai kawai Nur yayi snn ya kama hannun Bobbyn suka fita…kwace hannunshi yayi daga na Nur yana cigaba da tafiya da kanshi gamida tattaro duk wani sauran jarumta da karfin halin da sukayi mashi ragowa ya dorasu bisa kanshi snn yacigaba da tafiya har zuwa inda Nur yayi parking..da kanshi ya bude front seat ya shiga shima Nur ya shima driver seat snn ya tada motar suka dauki hanyan FCNM..zuciyarshi sai bugawa takeyi sbd baisan me zai tarar a wurinta ba amma ya gwammaci duk wani wulakanci da zatayi mishi akan dai yayi zaune a gida batareda yazo yaga halinda take ciki ba..gani yake kaman Nur ba tafiya yakeyi ba don bai ta6a ganin nisan college din ba irin na yau…suna shiga makarantan direct suka wuce hostel nan ma Bobby yaga nisan hostel din kaman yau ya fara shigoshi…saida sukazo daidai gate na female hostel Nur yayi parking snn ya sake dialing number Lamido…Billy ce ta sake dagawa yace”gamu hostel din naku zaki iya fito da ita?..”juyawa Billy tayi ta kalli Aysha dake rikeda kafan tana sauke ajiyar zuciya cikin bacci itama kaman zatasa kuka tace”sir bazan iyaba..bacci takeyi tun daxu ni bansan yanda zanyi mata ba”…Nur kashe wayan yayi yana duban Bobby daya gama jin duk abubuwanda Billy ta fada…daya daga cikin matrons sukasa akayo musu mgn da ita…ta bada sanarwan zasu shigo hostel din snn ta dawo tayi musu jagora har cikin apartment din da yayi tsit sbd kowa ta shiga daki sbd sanarwar da akayi musu…kai tsaye dakinsu suka nufa Bobby najin each taku na kara masa adadin tashin hankalin akan wanda yake ciki already.