Dr. BOBBY COMPLETE HAUSA NOVEL

Tun daga wnn lokacin ta fara bashi cold attitude..ba wai dena kulashi tayi ba saidai kwata kwata ta dena sakewa dashi…zataje har office ta gaisheshi kmr yanda ya bukata amma fa bai cika ganin dariyarta ba…haka zatayi duk wani abu daya sata amma dai bazai ga walwala da farin cikinta ba…ya rasa me yayi mata take bashi wnn traetment din don ko Allah yasan ba karamin damuwa ya sakashi a ciki ba…tun yana tambayan if yayi mata wani abun ta fada har ya hakura ya bar tambaya sbd amsa daya kullum take bashi shine ba komai…duk hakurinshi saida ta bashi haushin dan haka shima yayi alkawarin cigaba da treating dinta yanda takeso tunda ita batasan mutunchi ba…ita kuwa tanayi mishi haka ne ba don komai ba sai dan abubuwa biyu data fahimta tare dashi..cikin dayan biyu dole za’a samu daya..ko dai sonta ya farayi kmr yanda su Billy ke fadi ko kuma mutumin banza ne shi kmr yanda tasan yawanci inyamurai haka suke…wnn dalilin yasa ta daukan ma kanta alkawarin yin baya baya dashi sbd gudun koma mene a cikin zuciyarshi gameda ita don itadai tasan ko daura mata shi akayi a kafa zata kwance don ko kusa baya daga cikin jerin mazajen da takeso…kuma da taga shima ya fara sha mata kamshi sai abun yayi mata dadi dan dama so take ta yadda kwallon mangoro ta huta da kuda.
Har aka fara azumi suna a wnn halin yayinda ita Lamido take harkokin gabanta hankali kwance don har mantawa takeyi dashi..shi kuma yana can zuciyarshi na neman bugawa sbd tarin matsalolin da sukayi mashi yawa…bai taba tunanin haka ya damu da yarinyar nan ba sai yanxu..ya damu da abubuwanda takeyi mishi fiyeda tunanin mai karatu…rayuwar kawai yakeyi a haka ba don yanajin dadinta ba..ya zamana baijin dadin duk wani abu sbd wnn attitude da take bashi…gani yake idan bai samu daidaitawa da itaba yana iya mutuwa amma taurin kai bazai barshi yayi abunda ya kamata ba…ya gwammace idan ma mutuwa zaiyi ya mutu akan dai ya cigaba da binta tana walakantashi haka.
Ranar da aka kai azumi na goma ana gobe zasu fara exam din first semester daddy yace yana son idan ba damuwa Bobby ya kawo mishi ita airport suyi sallama sbd daga Kano zasu tashi…baiyi musu ba amsa mishi da zai kawota saidai cikin ranshi yana tunanin yanda tafiyan nasu zai kasance bayan ba wani jituwa sukeyi ba yanzu…ranar da safe ya danna mata kira abunda shi kanshi ya manta yaushe rabon daya kirata…tana dagawa ko sallamarta bai amsa ba yace”ki shirya zanzo daukanki by 1..ur dad wants to see u”…yana gama fadin haka ya kashe wayarshi ko tsayawa jin amsarta baiyi ba…yana yi mishi ciwo idan ya tuna yanda take treating dinshi kmr wani stranger…kilan dan taga ya fara damuwa da ita take mishi haka so Its better ya koma old self dinshi yanda zasufi daidaitawa da kyau.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba…masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank…sai a tura evidence of payment via 07063800556.
38
Karfe dayan nayi kuwa ya kama hanyan FCNM…tareda da driver dinshi suke amma haka nan ya sallameshi sbd baison ya tukashi if suna tareda ita…yana isa makarantan ko ciki bai shiga ba yayi parking daga nan waje snn ya kira yace ta fito ta sameshi bakin gate…duk yanayin haka ne sbd jin ciwon shariyar data tsiri yi mash…da tasan yanda ya damu da ita da batayi mishi haka ba wlh…ita kuwa shiryawa tayi cikin long doguwar rigarta na wani cotton material orange da qananun flowers lemon green a jiki…bata sa dankwali ba as usual tayi rolling dan karamin veil dinta daga kai zuwa shoulders dinta…bata dauki bag ba sai phone dinta a hannu snn ta saka flat shoe dinta ta fita tanata mitan ya sata tafiyan kafa..da bestie na nan ne tasan batada matsala duk inda tace ya kaita zai kaita amma now that he is not around dole ta zage ta koyi tafiya da kafafunta tunda dai tasan baby bazai yiwu ya dinga kaste aikinshi yana zuwa kaita ko ina da ina ba…kafin ta bar first gate dinsu taga wani mota yazo ya wuceta da gudu sai kuma taga yayi slowing down tareda yin reverse ya dawo inda take…dauke kanta tayi kmr bata gani ba sai taji wanda ke cikin motan yace”Hajia Lamido”..dan juyawa tayi tana kallonshi sai kuma ta saki murmushi ganin shine tace”Tajuddeen ashe kaine”..yace”yeah nine..ina zakije haka a kafa?..”tace”cikin college zan shiga wlh”..yace”amma why bazaki kira bus ya kaiki ba?.tafiyan akwai nisa fa”..dan murmushi kawai tayi batace komai ba…hannu yakai ya bude mata kofan kafin yace”to bari nayi dropping dinki”..girgiza kai tayi da sauri tana cewa”no nagode”..kallonta yake sosai yace”i insist..if kina tunanin wani abu ne ki dena don na dade da hakura ni kam..nasan ba sona kike ba amma for this once ki bari na taimaka maki”..bata sake mashi musu ba ta karasa ta shiga motar shi kuma yaja suka wuce…ganin bata ga motarshi a premises ba tace ya fita da ita waje kilan ta sameshi a can…suna fitowa kuwa ta hango motar nashi a tsallaken titi dan haka yayi dropping nata ta tsallako titin…tunda ta fito daga motar yake kallonta bacin ranshi na sake karuwa fiyeda wanda yake ciki already…wato da yace ta fito shine ta kira one of samarinta ya fito da ita sbd batada hankali…ta zauna gaban motarshi tanata washe mashi baki sbd batasan ciwon kanta ba ga wani shegen riga da tasa da bai gamsheshi ba sam..gaba daya rigan ya bayyana surar jikinta instead of tasa hijab shine ta dakko wnn dan veil din tayi rolling sbd rashin nustuwa…ranshi yaji yayi wani irin 6aci baisan lokacinda ya hada kan nashi da starring motar ba…yana rantsuwa da Allah idan har yarinyar nan zata cigaba da abubuwa haka mutuwa zaiyi…yasan for sure ko wulakancin da take mashi bai kasheshi ba to duk ranar da aka daura mata aure da wani nashi ya kare…a yanda yakejin zuciyarshi tamkar tana dab da fashewa ne sbd ciwon da yakeji cikinta ya fara mishi yawa…kiri kiri wai kana son mutum shi kuma baya sonka wani yakeso…duk ya tunada wnn abu sai yaji kmr yayi commiting suicide ya huta…har ta karaso inda yake bai iya dago kanshi ba..ganin tanata knocking ko dagowa baiyi ba kawai ta bude motar ta shiga fuska daure kmr wanda tayi ido hudu da makiyinta…duk abunda take yana jinta amma ko dagowa baiyi dan shi kadai yasan what is taking place in his heart…addu’o’i yayita karantawa iri iri har yaji ya dan samu relieve snn ya dago kan nashi ba tareda ya kalleta ba ya tada motar suka tafi…a hankali ta dan saci kallonshi taga fuskan nan a dinke kaman na saniya dan haka ta shafawa kanta salama tayi kasa da kanta tareda cewa”ina yini”..ko kallon inda take baiyi ba balle tayi tunanin samun amsa daga wurinshi…ta tabe baki tana gyara zamanta dama ba gaisheshi tayi dan ya amsa ba dan rainin hankali kawai…haka suka cigaba da tafiya in silence har suka isa Malam Aminu Kano International Airport…mamaki ya cikata ganin airport ya kawota ko me zasuyi a nan kuma oho?..bata dai tambayeshi ba tanaji bayan ya gama parking ya dauki wayanshi yayi dialing number daddy…bayan ya dauka Bobby yace”mun iso airport din sir”..daga daya bangaren daddy yace”muma gamu nan shigowa ciki yanxun nan”..daga haka ya kashe wayarshi snn ya bude motar ya fita…itama ta bude daya side din ta fita…suna fita kuma motan daddy yazo yayi parking a kusada nasu…ta wani zare ido tana kallon motar kmr bata taba ganinta sbd mamaki…kenan daddy ne yace ya kawota airport zasuyi tafiya ne ko kuma yaya abun yake?..daddy ne ya fara fitowa daga motar sai Ammi sai Husna da Yusra suma suka fito a tare…da sauri ya karasa inda suke yana kokarin durkusawa daddy yayi saurin kama hannunshi ya hada da nashi sukayi musabiha yana fadin”bana hanaka durkuson nan bane Attahir”..murmushi kawai Bobby ya saki kanshi kasa yace”barka da isowa”..daddy yace”barka dai..ya aiyuka?..”kai a kasa yace”Alhamdulillah sir”..sake kama hannunshi daddy yayi yana nunawa Ammi yace”to Maimunatu yau dai gaki ga Attahir”..ya juya yana duban Bobbyn shima yace mishi”itace Maman Aysha”..kokarin durkusawa ya sakeyi still daddy ya hanashi…ba yanda ya iya haka nan ya mike saidai ko kusa ya kasa dago kanshi ya kalleta a hankali yace”Ina yini”..Ammi dake kallonshi tana murmushi tace”lafia lau Attahir..ya aiki ya kuma akaji da fama da Aysha?..”murmushi kawai ya saki kanshi a kasa…daddy ya sake nuna mashi su Husna kafin yace”ga sisters dinta nan..wnn sunanta Asma’u karamar kuma Yusra”..kallonsu Bobby ya shiga yi yana murmushi..Husna ta fara gaisheshi snn Yusra duk ya amsa musu smilingly…yaji gaba daya ahalinta sun shiga ranshi don sunada karamci sosai…ita kuwa Aysha da tayi mutuwar tsaye tun daxun tana kallonsu sai yanxu ta samu sararin karasawa inda suke hankalinta duk ya tashi kar ace tafiya zasuyi ba tareda ita ba tac”daddy sannunku da zuwa”..daddy yace”yauwa..ya karatun?..”tace”fine daddy gobe zamu fara exams”..yace”Allah ya bada sa’a”..ta amsa da Ameen snn ta juya tana kallon Ammi jiki a sanyaye tace”Ammi ina yini”..itama ta amsa mata da”lafia lau..ya mkarantan?..”tace”fine..Ammi tafiya zamuyi?..”murmushi Ammi ta saki gamida girgiza kai tace”tafiya zamuyi dai..keda zaki fara exams waye zaiyi tafiya dake?..”nan ta marairaice tace”Ammi dan girman Allah zanje kinga ko last year ma da banje umrah ba..kuma ai Friday zamu gama exams din”..kafin Ammi tayi mgn daddy yace”yanxun ma ba cewa akayi bazaki jeba ai..zakije amma sai kin gama exams dinki zaku taho tareda Najeeb”..shiru tayi batace komai ba itadai Allah ya sani tafi son ta tafi tare dasu…Yusra ce ta matsa kusada ita kmr zatasa kuka tace”daddy nima zan zauna da Adda”..daddy yace”no itada take makaranta a ina zata ajiyeki”..da sauri ta sake cewa”daddy nidai zan…”bai bari ta karasa ba yace”stop it Yusra bazaki zauna nan ba”..ba musu tayi shiru tana turo baki Ammi dai kallonsu kawai take tana murmushi…hannun Bobby daddy ya kama yace”zo muyi mgn son”..ba musu ya bishi a baya…Aysha kmr jira takeyi su bar wurin ta matsa kusada Ammi kmr zatasa kuka tace”Ammi dan Allah ki cema daddy ku jira in gama exams plss”..harara mai kyau Ammi ta watsa mata kafin tace”sbd ke kika haifemu sai mu zauna zaman jiranki ki gama exams koh?..idan kika cigaba da damuna wlh gaba daya zan soke tafiyan naki saiki koma gida ki jiramu kafin mu dawo”..ta wani tale baki kmr zata sa kuka tace”kai Ammi dan Allah”..harara ta kuma watsa maka before tace”just dare me and see what will happen..keda har yanxu bazakiyi hankali kisan kin girma ba”…shiru tayi bata sake mgn ba sai turo baki da take…juyawa tayi taga yanda suke mgn cikin kwanciyar hankali har wani smiling taga sunayi duk su biyun cikin ranta tace”ai dole kayi daria tunda kana neman shiga tsakanin da mahaifina..mugu dakai kawai”…bayan kmr 5 mins suka dawo wurin…Bobby yayi sallama da Ammi dasu Husna snn ya bar wurin…itama Aysha sallamar tayi dasu idonta har ya ciko da hawaye ta juya zuwa inda yayi parking…tana bude motar ta shiga saita hada kai da guiwa ta shiga sauke numfashi…Bobby yayi shiru yana kallonta baidai ce komai ba…lumshe ido yayi ya jingina da kujera yana jin wani irin zafi na neman rufeshi…wai after duk wulaknci da ignoring dinshi da take still bayason ya ganta cikin damuwa…ya rasa wani irin al’amari ne wnn ace wai duk bata maka rai da mutun zaiyi even for once bazaka iya fita sabgarshi ba…ko kuka yaga tanayi sai yaji kaman da idanunshi takeyi…baya son jinshi ko kadan kuma yasan ko yayi mata mgn ma zaiyi wahala ta dena..baisan meyasa ta tsaneshi to this extent ba…bude idonshi yayi a hankali tareda tada motar suka bar cikin airport din…driving yakeyi a hankali yanajin yanda har yanxun kukanta bai bar taba zuciyarshi ba…ganin abun nata bana kare bane sai ya gangara gefen titi yayi parking shima ya hada kanshi da starring motar yana sauke numfashi…duk duniyar sai yaji tayi mashi wani irin kunchi da zafi da baisan daga ina hakan ke fitowa ba…saida ya dauki lokaci mai tsayi a haka kafin ya dago kan nashi da kyar yana kallonta…cikin muryanshi da yaji ya disashe all of a sudden ya kira sunanta”Aysher”…banza tayi dashi bata amsa ba kuma bata dago kanta ba..ya sake kiran sunan nata still bata amsa ba baisan lokacinda cikin karaji yace”idan baki denamin kuka a mota ba saukeki zanyi wlh..are u small kid da zakisa mutum a gaba da kuka sbd an tafi an barki..”..shiru tayi still bata dago kan nata ba..da karfi yakai hannunshi ya dago fuskan nata sai yaga ko digon hawaye babu..iskanci ne kawai yasa tayi hakan ashe ba kuka take ba..kallon cute face din nata ya tsaya yi without blinking…rabonshi daya kalli face dinta haka har ya manta..a hankali yaji wani irin nutsuwa na sauko mishi sbd ganin fuskan nata…ya lumshe ido yana sake budeshi kan face din nata da har dunia ta nade yasan bazai taba gajiya da kallonta ba…sai ya nemi duk wani haushinta da yakeji ya rasa..baisan ko magic take using a kanshi da baya taba iya dogon fushi da ita ba..duk yanda zata kai da bata mashi rai yana kallon face dinta sai yaji ya yafe mata komai sbd tsabar farin cikin da kallon fuskan nata ke sanyashi musamman idan tana cikin farin ciki…lokaci daya kuma ya dauke idonshi daga kanta ya wani sake dinke fuska snn ta tada motar suka cigaba da tafia…wani babban super market taga yayi parking yace ta jirashi nan ciki snn ya fita daga motar…bayan few minutes ya dawo da babban leda a hannunshi yasa back seat snn ya shiga ya tada mota suka cigaba da tafia….ko a hanya bai iya cikakken minti uku ba tareda ya juyo ya kalleta ba…haka nan sai yakejin ganin nata na tafiya da duk wani kunchi da damuwarshi…babu wanda yayi mgn har suka isa FCNM Hostel…daidai gate dinsu yayi parking kafin ta bude motar ta fita yayi saurin dauko ledan daya ajiye a baya ya mika mata cikin wani irin kaushin murya yace”ina iya neman wani alfarma wurinki?..”juyawa tana kallonshi wai alfarma zai nema shine fuskanshi cunkus haka..kai kawai ta daga mashi alamar eh…ledan ya sake mika mata kafin yace”hijabai ne nan ciki..inaso ko dan darajar amanarki da mahaifinki ya bani ki dinga sawa idan zaki fita..ko cikin college zaki shiga ki dora akan uniform dinki idan kinje class sai ki cire tunda na fuskanci ke har yanxu bakisan ciwon kani ba”…kallonshi kawai takeyi kmr mai tunanin wani abu sai kuma can ta numfasa tareda karban ledan da yake miko mata tace”nagode”..da sauri yace”banji kince zaki na sawa ba”..a takaice tace”zan sa”..ya saki wani murmushi yana binta da ido yace”nagode”..komai bata sake cewa ba ta bude motar ta fita shi kuma yayi relaxing nan ciki yana kallonta har saida ta shiga ciki snn yaja motar yayi reverse ya wuce.