ABADAN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

ABADAN COMPLETE HAUSA NOVEL

      ▶6⃣3⃣

Daga jabir dan Abdullahi R A yace:naji Manzan Allah S A W yana cewa ”((idan mutum zai shiga gidansa sai ya ambaci sunan Allah yayin shigar tasa da yayin ci abincinsa,sai shaidan yace:baku da abinci baku da gurin kwana(a cikin gidan),idan kuma ya shiga ba tare da ya ambaci sunan Allah ba yayin shigar tasa sai shaidan yace:kun samu gurin kwana,idan bai ambaci sunan Allah ba yayi da zaici abinci sai yace(shi shaidan din):kun samu gurin kwana da abinci))

Tana dakin suna ta hirarsu da inna wuro mami ya shigo dauke,da kwando wanda ta zuba kayan breakfast a ciki na inna wuron,da sauri maryam ta tashi ta amsheta kamta aduqe tana gaidata,ta amsa mata asakekamar kuma ba aurukarta ba yadda dai sjka saba,zama tayi itama aka soma hirar da ita duk da maryam taja bakinta ta tsuke,saboda kunyar mamin,sai ta tsugunna tana hadawa inna wuro tea.

”ni inna wuro dama zamanki kikahi wlh damu,da kiwa,naji dadi sosai”inji mami,kama bakinta inna wuron tayi
”rufani ki saya ni bintu,ina ni ina zaman maraya,wannan ao saiku,dubi fa don Allah wai wannan ruwan ahine karin safenku,ina kuwa zakuyi qwari”ta fada tana nuna tea din dake hannun maryam tana figita mata,dariya ta basu,baki daya,kai imna wuro nanu dama,duk yadda mami taso ta yadda tayi zamanta aje a taho mata da tsoho alhajinta sam ta qiya.

”amma dai inna ai kya zauna har a raka mairamun taki nata gidan anjima ko,ku gano nata dakin”maryam dake gefe gabanta ya fadi,sai walwalarta ta ragu,tsoro ne fal ranta
”nan fa daya,nifa yau sai qauyen ni’ima bintu”da qyar tasha kanta amma fa saidai a rakata taje ta gano don babu faahi yau zata koma,ta bar tsohonta shi kadai a gida(hmm,mata irin na da kenan masu iya tattala miji da bin umarni)
”kema sai ki zauna ki karya don hajja laila ta iso yau takeso itama ta koma audan din,tana can gun takwararki ana mata gyaran jiki da qunshi,sai kije can ki samesu don nan ba zaku sake na saboda mutane”kamar an dira mata dutse haka taji ta amsa da ”to”
”sannunki bintu,ke dai kin zama uwar kowa kenan,kin kama kowa kin riqe kamar yadda hausawa suke cewa da na kowa ne,arziqinki na kowa ne,Allah ya albarkaci rayuwarki data yaranki,da za’a samu ire irenki cikin al’umma su wadata da an bar kukan yunwa qunci da talauci,Allah ya jiqan mai gidanki”inji inna wuro
”ameen ameen inna,ai shi arziqi da Allah ya baiwa dan adam tamkar ka dauki wani abu ne mallakinka ka baiwa,wani kace ya amfana ya kuma amfanar da wasu,muma aro Allah ya bamu da rabon mu aciki da rabon wasu,ma’ana ka ci ka ciyar da wasu,ruwanka ka ci kai kadai ka tashi ran qiyama cikin wahala,don Allah na narka dukiyar ne ya dinga maka azaba da ita,abinda ka bayar shine rabonka don shi zaka taras a cikin littafinka ranar gobe qiyama,wanda kaci kuma banza ne don na wani ka yiwa ba bare a rubuta maka ladar ka ciyar da dukiyarka ga wani,kai kanka baka da tanbas din dawwama cikin dukiuar,wataran Allah na iya karbe kayansa ya baiwa wanda yaa dama,ko ka muti kabar zuriya to baka aikata alkhairi na wa kake zaton zai kula maka da su?”
”wannan haka yake binta,Allah kasa mu dace”inji inna wuro,maryam na gefe tana jinsu ita kanta addu’a takewa mamin cikin zuciyarta,ko bata taba mata komai ba ta haifa mata GWARZON MIJI DAYA TAMKAR DA DUBU ABDULLAHI BAWAN ALLAH,bare babu irin halaccin da bata mata ba,mami mutum ce wadda samun kamarta zaiyi wuya

ruwan shayin kawai ta sha taji cikinta gaba daya ya cushe don haka ta fice tabarsu adakin,dakinta ta koma tayi wanka ta saka baqar doguwar riga don kada kayan ta su baci garin lalle,can ta tars da haj laila tana hada lallen qunshi,tuni mero an shige cikin dilka da kurkum ga bayaga halawa da aka sha.

Ita kanta kasa gajiya tayi da sabawa fatarta sabulu saboda wani irin santsi da taji tana yi na ban mamaki,itakam dama ko ba’a gama gyaran jkkin nan ba a yau zata cewa haj laila abarta haka,tana kallon yadda mero keta fama ina ga ita,fitowarta kenan haj lailan ta miqa mata wani anu cikin cup sai qamshin citta da kanunfari yake tace
”shanye diyata”haushi ma kamata yayi bata ce komai ba tayi kurba uku ta faki idonta ta fita da shi da niyyar zubarwa
cikin garden na gidan ta shiga ta daga zqta fara zubarwa taji an riqe hannunta,a hankali ta dago kanta sai suka hada ido,sanye yake cikin suit baqi da ja saidai yar saman ya cireta tana singalalin hannunshi,da alamu har ya dawo daga fitar da yace mata zaiyi
sai da ya mashe mata ido daya sannan yace
”shigowata kenan naga wani haske ya cika gidan nan,ina waiwayawa naga ashe kece,shine na biyoki ina fata banyi laifi ba”ya fadi maganar yana qoqarin amshe cup din daga hannunta,tana qoqarin boyewa ta bashi amsa
”um um,ko daya bakayi laifi ba”
ganin yana qoqarin maida abin babba yana son ya rungumeta yasa ta sakar masa cup din a sauqaqe,sai ya leqa ciki yana fadin
”hala wanann abun dadi ne mami ta baki ko,Allah yayi da rabo na kenan nasha?”ya tambayeta yana kallonta,wani irin kyau yaga tana fitarwa,tambayar kawai yayi amma bai gane me yake fada
da sauri ta girgiza masa kai
”a’ah,kada kasha”
”why?,muba muta ne bane”yayi tambayar yana dan zaro ido gami da dage gira.

Sai kawai taga ya dangwalo ya tsotsa
”hmmmm,gaskiya da dadi”ya fada yana kaiwa bakinsa,kafin ta qwace har ya kurba,ta karbe kana ta zubar
”na gaya maka mazq baku sha,idan poising ne kuma fa?”
sai taga ya saki murmushi mai fidda sauti kana ya harde hannunsa a qirji
”sai abun ya zama abun alfahari a gareni,masoyiya ta bawa masoyinta guba sabida tsabar qauna,kuma zaqinta zanji dear na,ballantana ma na sani ke din ba zaki iya ba,saboda wasu ma da suka yi yunqurin bani naci kin kawar da hakan,ko kin manta har asibiti kika je aka tabbatar miki da irin nau’inta da kuma qarfinta?”
ido ta zaro,wai abdallah aljanine ko kuwa yana da su ne?
murmushi ya kuma yi,ta bude bakinta da niyyar yin magana,sai yayi azamar qarasowa gabanta,yasanya tafin hannunshi ya rufe labbanta yana kallon qwayar idonta tare da cewa
”yi shiru da bakinki,ki adana duk wasu tqmbayoyi da kike da,su,wannan hiran na daya dagq cikin hirarrakin da na tsara mana,cikin gidan mu na qauna,a kan gadon soyayya,a kuma qirjin masoyi”ya qaraahe maganar yana kashe mata ido.

kunya ta kamata sai ta zame bakinta tana murmushi ya sake matsowa kusa da ita yana yin qasa da murya saitin kunnenta
”ina fata kin tanadarmin salo salo na soyayya da,qauna wadda zaki shayar da ni,kinsan abdallah dan soyayya ne,yana son soyayya musamman ga matarsa”ya fada yana qoqarin janta jikinsa,gabanta ya shiga faduwa,ta faki idonsa ta zille tayi hanyar fita,baiyi yinqurin binta ba don ya tabbatqr da mutane a wajen amma sai ya matso uadda zata iya jinsa ya biyo bayanta
”ki gama zulle zullenki yarinya,awa,nawa,ne ya rage?”hakan da ya fada sai ua sata tsayawa ta juyo ta dubeshi idonta har ya cika da qwalla,dariya ya sa mata tayi hanzarin ficewa daga gun.

Zuwa la’asar gaba daya hajja laila ta gama da kyawunta,tamkar buga qunshin akayi aka dayeshi,banu kuskure ko daya aciki,ja ne amma har saman hannu da saman qafa,abinka da fara ya fito kuwa yayi marun,kyau kam basai an fadeshi ba ya gama yi,tuni yan kawo mero sun tafi don yaci ace ma zuwa la’asar din sun kai gida,saukowarta kenan daga saman mami dauke da wata leda wadda wani arnen codenet ne a ciki da aka fidda wa dinki na garari,kudadr mamin ta saka masu yawa ta siyawa maryam din sabida wannan rana,sallama akayi aka shigo falon qasan,raliya ce janye da hannun fadil(yaronta)sai hindatu da lubabatu da kulu,baaba huwaila da hajiya atika.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button