ABADAN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

ABADAN COMPLETE HAUSA NOVEL

Maryam tasa abdallah ya dauka shi da security dinsa taje su tafi gida itakam qnan zata kwana kafin gobe ta sanar da dangin zahariyya din a samu wanda zai dinga kwana da ita,ba maryam ba har abdallah da yasan mamin farin sani mamaki take bashi,wata iriyar kubutacciyar zuciya Allah ya hadata da iya,basu ce komai ba suka juya suka tafi


kiran sallar asuba ya sa mami miqewa ta ajjiye wayarta dake hannunta wadda ta bude application na qur’ani tana karantawa cikin zuciyarta,kwana batayi bacci ba kusan sabonta ne saboda kowa yasan ma’aikatan lafiya da iya kwanan zaune
fara daura alwalarta kenan ta fara jiyo salatin zahariyya tana yi tana shaquwa,jade da ambaton sunan Allah,da sauri ta saki alwalar ta koma cikin dakin da gudu,shaquwa take sosai idanunta a qaqqafe suna kallon sama,da sauri,mamin ta fara bata duk wani taimako da ya kamata a matsayinta na likita,saidai duk yadda takai ga son ceton rayuwar zahariyyan wanda ya halicceta ya riga da ya wanzar mata da qaddararta,ta amsa kiran ubangijinta ta riga mu gidan gaskiya,duk dauriya irin ta mamin saida ta saki kuka,babi shakka mutuwa ishara ce izina ce hakanan abar tsori da fargaba ce ga duk wani abu ma rai,ba bil’adama kadai na hatta da sauran halittu dake numfashi a doron qasa


Gidan kawunta qanin mahaifinta can suka sada gawar din su suka fi haqqi da ita,cikin qanqanin lokaci aka mata sutura aka kaita gidanta na gaskiya,shikenan duniyar,zancan banza ce,idan kayi damara don ita ka kwance,don katsaham zata zo maka tace sai ka bar cikinta bata da buqatarka don wa’adinka ya cika na zama acikinta,kusan azahar mamin taga giftawar wata mace goye da yaro,tayi tsammanin daya dagq cikin dangin mahaifinau zahariyyan ne mutanen qauyensu yan gaisuwa,sai data sake ganin wulgawar matar ta saka ido sosai sai taga kamar zubaida,matar dake gefanta ta taba tana tambayarta
”waccan kamar zubaida ko?”da sauri matar ta amsa mata din cike da murna take,yau gata tana zaune daura da haj bintu
”eh,zubaidan hajiya nene ba, ita ce mana kema kin kasa shaidata ko ke da kuka zauna tare ma tun tana qaramarta,hmmm duniya ce ai budurwar wawa,wadda ta ishi kowa riga da wando,uwarsu ta gama bata su ta lalata su yanzu yau gashi yadda suka koma,dan ahege ne fa goye a bayanta,yanzu haka aikatau take wani guri tana ciyar da kanta,don babu wanda zai dauki jigilarta bayan lokacin da suke da ahi bani wanda suka morawa komai”ko kadan bayanan matar bai burge mami ba,jasalima haushi ta bata,cikin takaici tace da ita
”harshe yana iya kai mutum wuta nan da nan cikin qanqanin lokaci,anna bi yace idan kaga dan uwanka cikin wata musiba ka shiga aibata shi da yadashi,Allah yana iya yaye masa kai kuma ya jarrabceka da abinda ka aibata shi akai din,abinda aka umarcemu da cewa duk lokacin da muka ga wani da,Allah ya jarabta da wani abu ko cuta ce ko makamancinta shibe ALHAMDULILLAHIL LAZI AAFAANI MIMMAB TALAKA BIHI,WAFADDALANI ALA KASIRIN MIMMAN KHALAQA TAFDILA,daga haka mamin ta miqe ta bata guri

Bayan zubaidan tabi wadda ta gani riqe da robar abinci ta zagaya can baya ta kunce qarmashshan danta daga goyo ta zaunar da shi kan cinyarta ya soma bashi abincin cikin robar,don tausayi sai da qwalla ta zubo mata,ta qarasa kusa da ita tana kiran sunanta,sai kuwa tq zabura ta miqe zata gudu
”kada kije ko,ina zubaida”sai ta kira sunan mamin hawaye,na bin kuncinta,inda take ta qarasa tasa hannu ta amshi dan ta jata gefe guda

Tiryan tiryan ta debe abinda ya faru da ita bayan barinta gida,ashe gun mugu ta gudu wanda shine uban danta,ba dadeea ta ganshi ya sato,nene yazo ya hadasu,ashe abinda yasa ya nuna yana sonta,cikin jikinta yakeso ta haife ya dauke yaron ya saidawa qungiyar asiri,tun daga rqnar data fuskanci haka suka shiga tashin hankali ita da nene wadda ta dawo tamkar tababbiya,duk da haka wani lokacin idan abun ya lafa mata sai ka gantq ras kamar mai hankali,ruqon Allah suka dinga yi cikin ikomsa Allah ya kawo abokan gabarsu suka murqushesu shine su kuma sukayi amfani da wannan damar suka tsere,yanzu haka nene na gidan mahaukata ita kuma tana aikin wanke wanke fidan wani saida abinci da shi take dan taimakon kanta da nenen

kuka sosai mamin tayi kana ta amshi adress din gidan aikin nata tace zata nemeta,itakam ko wani abu ne ai zubaida bata masu komai ba face kanta data zalunta ta biyewa son zuciyarta

????????????????????????

Zaune suke gabanta tana saman kujeravtana rubuce rubucenta,ta sake dagiwa karo na biyu ya dubesu
”uhmmm,idan kun shirya yimin bayanin ina jinku”abdallah ne da maryam kusan awa guda an rasa mai bayani tsakaninsu,sai kallon kallon,gaba daya ta fahimci sun maidata kakarsu,akwai surukuta tsakaninta da maryam don haka ta dubi abdallah
”gayamin meke faruwa?”mutsu mutsu ua shiga yi kana cikin inda inda yace
”mami,kince ne dama idan mukaji da matsala mu miki magana wata uku da ya wuce,to maryam ce tace tana jin abu kamar dutse a mararta”sguru mamin tayi tana nazari,babu shakka zatonta ya fara zama gaskiya,ta dade tana yiwa maryam din kallon mai cikin,jin shiru babu wanda yayi maganar daga ita har shi ua sanya itama ta tsuke bakinta ta bisu da addu’a

kai tsaye dakin data ware cikin gidan ta sata ta shiga,ba tare da bata lokaci ba ta fara taba cikinta,kasa gasgata kanta tayi sai data saka na’urar scanning,hoton dan tayin jariri radam ya bayyana kan fuskar na’ura,tsura ido sukayi shida maryam din suna kallon talabijin din,tsantsar farinciki da murnar mami kasa boyuwa tayi har sai da murmushi ya qwace mata
”tabbas,gabunta da wautar dan fari bata barinsa,hakanan tabarar auta ma bata taba barinsa,Allah ya ahiryeku maryam da abdallah,ciki wata hudu amma daga ke harshi babu wanda ya fahimci hakan,wadan nan kam da aqauye kuke cewa zanyi ba mamaki,yarinya ta kusan cinye buhun kwaki amma bai isheku ku gane komai ba?”wani uban tsalle abdallah ya daka sai gashi gaban mamin saura kadan ya kada ita qarfin ba daya ba,ta dafe gadon da maryam ke kai tana fadin
”abdallah yi a hankaki mana”
”mami zan zama daddy fa kika ce,wayyo Allah na kana sina Allah”ya fada yana daga hannayenshi sama
”janye mijinki maryam kada ya targada min kafada tun kafin jikan yazo na rasa hannun daukarsa”mamin ta fada cikin tsokana,kunya ta kama maryam don ta sadda kanta qasa,tabbas cikin abinda yasa ta kasa gane cikin ko mutanen da take tare da su baya ga na fari ne tsahonta ya shanye cikin sai ya qara mata qiba kadan ta murje fatarta tayi kyau,har wani lokacin abdallah idan yana son tsokanarta zakaji yana ce mata
”diyana ‘yar lukuta ta bawan Allah”sosai mamin ta zauna tana musu bayanin yadda zasu kula da cikin don ta fuskanci daga abdallan har maryam din jirgi daya ne ya kwasosu

kuyi maneji da wannan

mrs muhammad ce????

????????????✍????✍????✍????
????????????????????????
????????????????????????
???? ABADAN????
????????????????????????
????????????????????????
????????????????
????????????
????????
????

WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA
????????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
© HASKE WRITERS ASSOCIATION????
home of expert and perfect writers

????????????????????????????

    ▶6⃣9⃣

Daga mu’az dan anas R.A yace:Manzan Allah S A W yace:((duk wanda yaci abinci sannan yace:ALHAMDU LILLAHIL LAZI AD’AMANI HAAZA WARAZAQA NIHI MIN GAIRI HAULIN MINNI WALA QUWWAH,an gafarta masa abinda ya gabata na daga zunubinsa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button