ABADAN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

ABADAN COMPLETE HAUSA NOVEL

mrs muhammad ce????

????????????✍????✍????✍????
[9/17, 12:49 PM] 80k: ????????????????????????????
????????????????????????????
???? ABADAN????
????????????????????

WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA
????????????????????????????
????????????????????
????????????
????????
????

       ▶3⃣

sanye take da material silk dark pink wanda aka yima ado zane na qaqen flowers manya,yayin da ta yane kanta da mayafi baqi tayi rolling dashi wanda ya maisheta tamkar jinsin larabawa,qaramar jaka ta sagale a gwiwar hannunta sai baqin toms mai kyau,sosai shigar tayi mata kyau tamkar bata da wata matsala a rayuwarta

a rumfa ta tadda mama tayi mata sallama tace mata a dawo lafiya ta gaida fadil da mamarshi,suna zaune a tsakar gidan kamar ko yaushe ko wacce ta maida hankalinta kan kayan sana’arta,wanda da zaki tambayesu suk cikinsu babu wadda zata iya gaya miki taqamaimen inda yaranta suke,sana’arsu ta fiye musu komai

da sauri ta fara qoqarin ficewa daga gidan don bata fatan daya daga cikinsu ta,ganta balle ta jefeta da kalmar da zata bata ranta,saidai duk iya saurinta bata ci nasara ba sai da huwaila ta ganota
”uhmmm,mutanen burtali,an fita kenan”
bata fasa sauri don ta fice a gidan ba kamar yadda bata ko waiwayo ta dubesu ba

cikin soron sukayi kacibus da AZARA,qanwar ta ce ta hudu wadda tayi aure da yaranta uku,ba laifi mijinta na iya bakin qoqarinsa duk da wasu abubuwan bai iya dauke nauyinsu,sai kuma Allah ya hadashi da mace mai izgili izza da rainuwa,azara akwai rainuwa da izgili saidai ba laifi rashin kunyanta da sauqi akan ta sauran yaran,tunda ko babu komai idan sun hada zata tsaya su gaisa koda zata jefeta da habaici a fakaice

yanzun ma hakance ta kasance,fuskar maryam din fadade da murmushi ”maraba da mutanen fanshekara(unguwar da take aure)”ta fadi tana miqa hannu zata amshi yaron axaran yaqi zuwa saboda dan banzar qiwar da yakeyi,azaran tace
”hmmmm,sannunku kuma”
”azara yaron nan qiwa yake haka?”
”ko ba ya qiwa aike yayi miki tunda ba ganinki yake ba,mu ko nsmu gidan ba’a zuwa saboda bamu da komai”
murmushi maryam tayi,don ta fahimci inda tasa gaba
”ko daya ba haka bane azara,kinsan bani da lokaci sai weekends,to su din ma sai wani zarafin ya shigo ya cinye wunin naka duka”ta kawar da maganar don kada tayi nisa ta hanyar cewa
”ina sauran yaran?”
”kunun aya ne bai qare ba na,barsu su qarasa saidawa don kada ya lalace shi yasa ma ban taho da su ba”

wani abu ya tokare maryam,wato irin rainon da aka mata shi zata yiwa nata ‘ya’yan,a maimakon ta bata amsa da sun tafi islamiyya don a yanzu lokacinta ne sai tage gaya mata ta barsu gun talla?,du du du yaran nawa suke?,kamar tayi mata magana kuma sai taja bakinta ta tsuke don kada cibi ya zama qari
”sai ina kuma?”azaran ta tambayeta bayan ta gama qare mata kallo
”wallahi zani gidan raliya ne”
”hmmm,babban goro sai magogin qarfe,su ai sun isa ayi da su din,bari na qarasa ciki ko,sai kin dawo”
danne zuciuarta tayi ta murmusa
”to shikenan,idan na dawo na tadda ke to”
”o’o,anya zaki tadda ni kuwa,wannan fitar taku ta manya wa yasan ranan dawowarku”
”to ki gaida gida”
”gida zaiji”

tana tafe a layin zuciyarta cunkushe da tunane tunane,hasbunallahu wa ni’imal wakeel ta dinga karantawa har ta iso titi,akwai qarqncin motocin haya kan titin nasu ko kuma ace kusan duk wadda tazo cike take da ‘yan makarantar boko da suke dawowa gida,kusan motoci uku ne suka tsaya don bata lift saidai ko kallo basu isheta ba,hakan,na yawan faruwa da ita kasancewar unguwar nasu na maqotaka da unguwar nasarawa G R A,duk sanda hakan ta faru takan yawaita neman tsarin Allah,sannan takaici mamaki gami da tsoron maza kan sake yawaita cikin zuciyarta,basu da burin da ya wuce suga sun samu damar da zasu shiga rigar mutuncinki su wuce su barki babu batun aure

da qyar ta samu wata da yara yan makaranta biyu a ciki,ta masa kwatance inda zai ajjiyeta

cikin murna raliya ta tarbeta,cikin falonta suka zube bayan ta cikata da kayan ciye ciye suka hau hirarsu da bata qarewa fadil na bisa cinyarta,
”kinga kawo fadil din na riqe miki shi tunda yayi bacci ki samu kici wani abun,idan ba haka ba bazai barki kici komai ba”
”a’ah qyalemin shi”
cikin haka wayar raliyan ta soma tsuwwa,ta cirota ta duba screen din tana fadin ”abban fadil ne”
magan sukayi ta tsawon minti biyar sannan ta kashe tana duban maryam bayan ta miqe
”yace yana miki sannu da zuwa,bari,na saka miki wani film ya dan debe miki kewa ni shiga kitchen ya kamani,abban fadil ne zaiyi baqi”
”haba kema raliya naji zancan shiga kitchen kuma na zauna,ai kinsan sai anyi da ni”
”sannu uwar madafa”ta fada cikin zolaya
”na karba,ko kin manta kan abinda na samu degree kenan”
”wannan gaskiya ne,bani fadil din to na kwantar da shi sai mu wuce kitchen din ko?”

qarfe hudu da mintina ashirin suka kammala,lafiyayyen girki ne wanda maryam ta gwada basirarta akai,ita kanta raliya komawa tayi gefe tana kallonta don bata zaci qawar tata takai haka ba,biyar saura ta suna falo,ta soma hada kayanta don tafiya gida ”amma diyana(haka suke kiranta wani lokaci a makaranta)ki sake wanka mana wannan aiki da kika sha”
”ai dole ne,amma fa idan na isa gida”
”ai ko wlh anan zakiyi”
murmushi tayi wanda har dashashinta sai da ya bayyana
”kinsan dai bana wanka na maida kayan da na cire,ni kuma ban taho da spare ba”
”tsarabarki ta south africa tana nan,saiki zabi daya a ciki kisa”
duk wayon,maryam sai da raliya ta sata yin wankan ta kawo mata ledar tsarabar ta zabi doguwar riga guda daya da tasha adon jajayen dutsina masu yawa da sheqi

a falo ta taddata”kinga kuwa maryam yadda rigar nan ta miki,Allah ya kawo miji na gari,gaskiya ba qaramar hidima zamu sha ba”
”har yanzu babu abinda ya ragu a surutun raliya”
”haka miskilanci kyau da ajin maryam diyana har yau yana nan”duka sai suka sa dariya,yana daya daga abinda ya sa qawancensu ke ma maryam dadi,raliya akwai vbarkwanc,inda kuma halinsu yazo daya ta bangaren haquri da dauke kai

qarar bude get din gidan ne yasa suka ankara da isowar abban fadil
”kinga har sun iso ina nan a zaune,biyar harda kwata”maryama ta fada tana miqewa
”kinga malama koma ki zauna tunda sun riga sun iskemu tare ai bakya tafi ba,ki bari mu tari baqinmu qarasa ladarmu tare”babu yadda ta iya haka ta koma ta zauna,ta fiddo wayarta tqna yiwa hndatu texs ta sanar da mama tana nan tahowa raliya ce ta tsaidata

tana cikin sending sallamar baqin ta ratsa dodon kunnenta,a sanyaye ta dago tana amsawa,su uku ne abban fadil na hudu,duka sai taji ta a takure gashi raliya ta shiga ciki sako mayafi,sai ta miqe tana daukar jakarta tace
”sannunku da zuwa,abban fadil yanzu raliyan ta shiga ciki bari na mata magana”
dakatar da ita yayi
”a’ah yi zamanki,nasan a gajiye kike kunsha aiki bari na fito da ita,jabir bari na fito da madam”

falon yayi shiru su duka harda baqin,wayarta na hannunta tana danne danne amma sai take jinta a takure,gashi daga raliyan har nasir din shiru kamar an shuka dusa
”madam haka ake kula da baqi?”
tajiyo maganar lokaci guda,ta daga kanta don ganin me maganar,shije zaune opposite dinta,sanye yake da shadda hartin da hula,murmushi ta danyi a taqaice
”ai bani bace matar gidan,ku jirayi fitowarta”
”ke da ita din ai daya ne,don na tabbata yarda ce tasa suka barki da baqinsu”
sai ta maida idonta kan wayarta don bata da abun ce masa,Allah ya taimaketa masu gidan suka qaraso

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button