ABADAN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

ABADAN COMPLETE HAUSA NOVEL

sai kuwa inna hadiza ta hauro itama huwailan dake kusa ta bi mata,sai fada ua zama hudu,binta nayi da lubabatu,huwaila nayi da hadiza ,mama ta yunqura zata fita bada haquri hindatu ta tareta tace wallahi mama babu inda zaki,lokacin da suke ‘yar dadin babu wanda auka dauka abanza ieinki saboda haka yanzun ma ba ruwanki,su kashe kansu”a haka malam mamuda ua sjigo ya tadda gidan nasa

zancan ya bibiya amma daga qarshe sai ya goyawa inna hadiza baya,ko dama can itace mowar,balle yanzu da jamila ke satowa tana kawowa uwarta ita kuma take yagar masa,bayan sun shige daki ba qaramin ciwo abun ya yiwa huwaila ba,ta cizi yatsa yafi sau ashirin,lubabatu dake tsaye tana taya uwar tata takaici tace
”wallahi huwaila duk ke kika ja mana tun asali,da tuni nice kan matsayin jamila kika tsaya gina wasu kika qi gina kanki,ai da arziqi,a garin wasu gwara a garinku a garinku ma aunguwarku a unguwarma agidanku a gidanku ma adakinku”
”duk banga haka na lubabatu sai yanzu,nayi dana sani wallahi yafk a qirga,tsinanniyar mata ta kuma samun power a gida?”
”ato,shawara dai ta rage ga mai shiga rijiya,saiki zauna ki tuna bunyi”

kamar tayi mata allura ta figo mayafinta dake ajjiye saman qofar falon ta tace
”kinga zauna ki jiremin daki na,ba’a bori da sanyin jiki,bari naje gidan talatuwa”
saman tabarmar dakin ta zube tana fadin
”sai kin dawo”cikin zuciyarta tana addu’ar Allah yasa adace,tuni ta fara hango kanta a irin daular da jamila ke ciki,tana yin son ranta wanda tuni an maida jabir wani sususu,aure dai an yishi amma amma fa na cin abinci da cin kayan dadi da dibar kudi

mrs muhammad ce????

????????????✍????✍????✍????
[9/17, 12:51 PM] 80k: ????????????????????????????
????????????????????????????
???? ABADAN????????
????????????????????????????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
????????????????????????????
????????????????????????????
WRITTEN BY
SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA
????????????????????????????
????????????????????????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????

    ▶1⃣7⃣

sama sama hadarin ke hadowa yana bajewa tun daren jiya,hakan ne ya sanya har safiyar yau garin yake da lullumi,lullube sama take da hadari mai duhu saidai sanyi sanyi yake bayarwa har yau ruwan bai kai ga sauka ba,qarfe goma ta kammala komai,wankanta tayi ta shirya cikin pskistan riga da wando daya daya daga cikin tsarabar da raliya tayi mata ta south africa,orange ne wanda aka yiwa adon dutsina dark blue daga gaban rigar da qafar wandon

mayafinshi shara shara ne amma yana da dan girma shi ta saka ta yane kanta da shi,tun baiwai yau mami ta fita saboda ta cinye hutunta na kwanaki ukun saboda haka bangaren babu kowa sai ita daya,kusan tunda tazo gidan bata fita ko ina ba saboda hala tayo sha’awar dan zagaya wa,wayarta na hannunta ta saka flat shoes ta fito

iya girma gidan yana da shi,ba ma wannan ba yanayin ginin ya burge maryam,bugu da qari yanayin da gafin yake ya qarawa maryam nishadi,lokaci gida hadarin ya yaso garin yayi duhu sosai,cikin qanqanin lokaci iska ta taso ruwa ya kece

da sauri sauri take nufar hanyar sashen nasu don bata son ruwan ya tabata,su uku me ysaye a waiting parlour din,nene zahariyya sai wani matashi da ya bawa qofa baya yana fuskantar nene,shigowar tata taji sunyi dif a maimakon sauti sautin maganar da take iya ji duk da cewa baka iya tantance abunda suke fadin,binta sukayi duka su biyun da kallo wanda hakan ya ja hankalin saurayin ya juya shima don ganin abunda suke kallon

har cikin jikinta take jin kallon nasu hade da faduwar gaba,hakanan take jin wani tsarguwa duk lokacin da suka bita da irin wannan kallon,saida ta shige sannan suka dauke idonsu
”nene,wace wannan?”ya tambayeta idonsa cikin nata cikin son jin amsa
sai da ta kuma tsuke fuskarta kafin ta amsa masa
”yar aikin da bintu ta sakewa abdullahi ce,bana buqatar kuma kace komai,idan ma wani abu kake shirin sawa zuciyarka kayi gaggawar cireshi,don wannan karon babu gudu babu ja da baya sai mun cika burin mu,a shirye nake da kawar da duk wani abu da zai kawo wa plan din mu cikas,kuma ina fatan haka ne cikin zuciyarku”

zahariyya ta tauna chewing gum dinta ya bada sautin qas qaqass
”nifa nene na fiki son cikar burin nan,sabodda haka har abunda ma ke ba zaki iya ba ni tsaf zan aikata shi”
”to balle kuma ni da nake namiji,ina da burika da dama…saidai fa…gaskiya naji yarinyar cikin jini na,tana da fitinannen kyau,any way zan ajiiyeta a side har sai bayan kammaluwar plan din mu”
”ato ya dai fi maka alkhairi”cewar nene tana buda hanci

garam taji taci karo da wani abu wanda tsabar sauri da rudewa yasa bata gane ko meye ba,ga duhu da ya mamaye falon kasan cewar duk wani qwan lantarki ta kasheshi lokacin da zata fita din
tsoro yaso kamata da tabi inuwar abun da kallo dogo ne wanda duk tsawonta ya kereta,yana kuma tsaye qiqam bai ko motsa ba
gabanta yayi mummunar faduwa,bata sake rudewa ba sai da taji muryarsa na fadin
”wannan wanne irin shshanci ne haka da hauka,kina tafiya kamar mai tabin qwaqwalwa,yanzun kuma da kinji min ciwo fa”

haushi maganar ta bata,wato ita ce ma mahaukaciyar?,shi da yake namiji baiji mata ciwo ba sai ita ce,zata ji masa?ita fa bata son rainin hankali shi ya sanya har yau bata bari su hada gu da shi,don ta fuskanci ya raina ajawalin mata saboda yaga yadda suke masa rushing

cikin dan daga murya yace
”kin wani tsaya kamar wata doluwa,ina breakfast din mu yake?”
”tun dazu na dora saman dining ai”
”ok it means ni zan sarving da kaina kenan,haka kika ga mami na na yimin”
kamar tace mishi to ai ni ba mamin ka bace,sai kuma taga bai dace ba,don tana kallonta ne tamkar mamanta
”comone dallah…dole ki dinga showing caring like my mami,babu buqatar nana ta miki aikinki,duk da cewa u can’t replace my mami ko da digo daya cikin kaso dari ne,idan kuma ba zaki iya ba the door is opened”

bata ce masa komai ba ta zagayeshi ta wuce bayan ta kunna qwayayen lantarkin din dake falon,ta riga shi isa dining din don haka ta soma hada mishi tea don kafin ta kammala zuba mishi komai zafin ya dan sarara
kujera ya ja ya zauna daidai lokacin da wayarshi ta soma ringing
tamkar wani mace haka yake amsa waya,ba hayaniya ba daga murya

”shi don ubanshi bai san kai wane ba da,zai hanaka shigowa?,to ya bari mintina biyar su cika ya gani,idan ka ahigo ka sameni gefan mami”abinda kawai taji yace kenan ya kife wayan saman table,fuska a murtuke ya ja kofin shayin ya kai bakinsa,tana ahirin dakatar da shi amma tuni ya kai bakinsa,ai kuwa babu shiri ya dawo dana bakinsa ya fesar

”ke wacce iriyan muguwa ce don Allah,haka ake bawa mjtum tea da azabar zafi kamar za’a dafa mishi baki?”
muryarta a narke tace
”ayyah,don Allah kayi haquri,ina shirin dakatar da kai naga har har ka sha”
”mtswee…you are verru stupid”ya fada sannan cikin hanzari ya dauki wayarshi dake bisa teburin ya fara danne danne

”hello abdallah,lokacin aiki ne fa ina tare da patients”muryar mami kenan
”mami yarinyar nan aiki aka kawota ta min ko kisa?”a razane maryam ta dago ta kalleshi,sai kuma ta maida kqnta qasa ta sadda shi,tini oily eyes dinta suka qara sheqi ssakamakon qwallar da ta soma dan taruwa mata
cikin faduwar gaba mamin tace
”me ya faru abdallah?”
”mami zata kasheni da ruwan zafi,tea mai azabar zafi mami ta bani zai qona ni”
ajiyar zuciya ta saki
”oh my god abdallah,kasan yadda ka bani tsoro kuwa?,just ruwan zafi kawai ahine kake wa haka,sau nawa kana shan tea ba tare da ka fifita shi ba,sannan nasan maryam bazata taba baka tea da zafi tana sane ba”
”gaskiya mami bata san aikinta sam”
”enought abdallah….bani maryam din”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button